x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 8 - RAWANIN ZALINCI STEP 1

  • 21001 words
  • 24000 words
  • Out of 297772 words

Category: Love Stories

Views 435

10 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
abubuwan ciki.

Tsabta akwai daɗi, kai da kanka idan ka tsabtace waje sai kaga ya yi wani irin masifar kyan gani, komai talaucin mutun idan yana da tsabta yana da sha'awar kallo a ido wlh.

Bakinsu ɗauke da cikakkiyar sallama irin ta addinin Musulunci waɗan nan yara suka shigo cikin gidan nasu.

Dayawan mutane ba kowa ne yake yin cikakkiyar sallama ko ya amsa sallamar a cikenta ba, dayawa mutane suna yanketa wanda hakan kuma ba dai'dai bane, domin kamar yadda kuka yanketa haka ma'anarta ta yanke.

Dayawan mutane zaka ji suna cewa Salamu alaikum, masu amsata kuma suna cewa Alaikumussalam, wanda hakan sam ba dai'dai bane, nasan dayawanku baku san kuskure kuke yi ba, to tabbas kuskure ne yanke sallama da kuke yi, kuna yanke ma'anarta.

Masu shigowa zasu ce Assalamu alaikum, Mala'ikun Rahma suna amsata da Amin wa'alailumussalam, idan ku dayawa ne kuka shi go kenan, idan kai ɗaya ne, Amin wa'alaikassalam, shi ne cikakkiyar sallama ta addinin musulunci, Allah ka yafe mana kura kuranmu.

Masu cewa in rinƙa rubuta addu'a ko wata tunatarwa kamar dai sallama dana gyara maku yanzu, masu cewa na rinƙa rubutawa da hausa ba da larabci ba, dan basu iya karantawa ba, zan yi ƙoƙarin yin hakan In Sha Allah, amma wani lokaci dole ne na rubuta da larabcin kun gane ai?.

Daga cikin ɗaki aka amsa masu cikakkiyar sallamar tasu tare da cewa. "Ƴan mata na an dawo?".

Babban cikinsu ne ta amsa da. "E mama mun dawo".

Tana magana tana cire hijabin jikinta, sannan ta ajiye wannan ledar dake a hannun nata a tsakar gidan, kafin ta wuce izuwa cikin parlourn.

Ita kam karamar dama tun shigowarsu ta sanya kai izuwa cikin parlourn da sauri abinta tana faɗin. "Mama baba ya aiko mun da lemun?.......".

Turus ta ja birki a tsakiyar parlourn lokacin da idanuwanta suka sauka a kan maman nata tare da wata bakuwar mata suna zaune a saman sofa suna hira. Mama ta sha kwalliya cikin wani haɗaɗɗen lace mai tsada da ya sha ɗinkin doguwar riga, ta yi kyau sosai, launin black color ne lace ɗin da ratsin milk, hakan ya kara mata kyau sosai kasancewarta farar fata, ta sha ɗaurin ɗan'kwalinta ɗas da shi. Ita kuma wannan bakuwa tana sanye da abaya launin ash color, ta yafa mayafin abayar a kanta.

Nan take yarinyar ta ɗaure fuska sosai kamar ba ita ba, duk da cewa dama can fuskar tata ba wani murmushi ne a samansa ba, daga ita har babban yayar tata babu alamar murmushi a saman fuskarsu, da alama basu da yawan fara'a, shi ne ma yasa da suna dawowa daga islamiya sai magana yara sa'anninsu suke yi masu, amma sun ki kula kowa.

"Zinarun babanta ya kika tsaya haka? Ki ƙariso ciki mana". Cewar matar dake hira da mamar tasu.

Kara ɗaure fuska sosai Zainab ta yi, da alama bata kaunar matar ko kaɗan. Daidai lokacin ita ma babbar ta shigo cikin parlourn tana faɗin.

"Mama ga can kayan miyar nan na kawo maki, amma mama wai fa babu attarugun ɗari biyu, shi ne na saya maki ta ɗari biyar kawai, shi ma baki gansa ba ɗan kaɗan da shi........"

Bata kai karshen maganar ba ita ma idanuwanta suka sauka a kan wannan matar, ɗaure fuska sosai ita ma ta yi tare da wucewa zata nufi ɗaya daga cikin ɗakunan dake a cikin parlourn.

"Khadija baku ga Auntynku bane? Aunty Hauwa ce fa, ba zaku gaisheta bane". Cewar maman tasu.

Wucewa Zainab ma ta yi ta rufawa Khadijah ɗin baya, dan su shiga cikin ɗakinsu.

"Sannunki da zuwa Aunty Hauwa". Cewar Khadijah, ta yi maganar tana wani irin kunbura kumatu, alamar sam bata ji daɗin sakata gaisheta da aka yi ba.

Washe baki Aunty Hauwar ta yi tana faɗin. "Hadiza bage maganin maza, wai ni kam duk masu suna Khadijah haka suke ko? Haka kanwata ma take sam bata son baki".

Wata uwar harara Zainab ta wurga mata ba tare da sun lura ba, cikin ɗaki ta wuce abinta, har ga Allah ta tsani wannan Aunty Hauwa ɗin, ko me dalili?.

Turɓune fuska Khadijah ɗin ma ta yi kamar wadda aka aikowa da sakon mutuwa, yara kanana da su sun san kin abu, kome dalilinsu oho.

Uniform ɗin jikinsu suka cire, suka sanya kayan gida, wasu dogayen riguna bakake, iri ɗaya kayan, sai dai na Khadijah mai kwalliyar flowers ja ne, na Zainab kuma mai kwalliya pink color, shi ne kawai banbancin kayan nasu.

Fitowa suka yi suka sake wuce maman tasu da Aunty Hauwa, waje suka nufa, a lokacin sai kiraye kirayen sallar mangariba ake yi.

Famfo tsakar gidan suka je suka kunnna, Khadijah ce ta fara gabatar da alwala kafin ta bawa Zainab waje ita ma ta ɗauro nata alwalar, da alama mamansu ta saba masu da yin komai cikin tsari, dan daga yanayin yanda suka shigo suka je suna cire uniform suka fito suka ɗauro alwalar nan, alama ya nuna cewa tabbas an sabar masu da hakan ne.

Ciki suka koma, dai'dai lokacin aka kawo wutar nepa, sallah suka je cikin bedroom nasu da yake tsab tsab suka gabatar, ita kuma mamar tasu tana zaune ta biyewa Aunty Hauwa sai zuba hira suke yi har yaran suka idar da sallarsu.

Abin mamaki cikin nutsuwa suke gabatar da sallar nan tasu tamkar wasu manya.

Bayan sun idar ne suka fito parlourn, a yadda suka bar mamarsu haka suka fito suka sameta.

Khadijah ce ta ce. "Mama yau kin manta baki yi sallah da wuri ba".

"Ban manta ba Khadijah, ai ba'a mantuwa da ibada, yanzu nake son tashi na yi".

Da gudu Zainab ta nufi kofar fita daga parlourn jin an taɓa kofar gida, faɗi take yi oyoyo baba oyoyo Yah Haidar. Da sauri Khadijah ma ta rufa mata baya, tamkar basu ne masu ɗaure fuska yanzun nan ba, a take suka fara zuba murmushi na ganin mahaifin nasu da kuma yayansu, ashe dai suna dariya, amma da alama ƴan gidansu kawai suke yi wa dariyar.

Yah Haidar ɗin nasu yana rike da kaji na hausa guda biyu a hannunsa, zakara da kuma mace, sai kuma wani katuwar bakar leda a ɗayar hannun nasa, shi kuma baban nasu yana rike da wata leda irin mai zane a jikin tan nan, kayan fruit ne a cike a cikin ledar.

Khadijah tana zuwa ta fara kiciniyar karɓawa baban nasu ledar hannun nasa, ita kam Zainab tuni ta yi tsalle ta ɗale jikinsa tana dariya har da kyakyatawa, kamar ba ita ce yanzun nan ta gama hararar Aunty Hauwa tare da turɓune fuska ba, dama fa masu suna Zainab da Khadijah wlh sai a hakankali, kusan kaso tamanin cikin ɗarinsu haka suke, akwai shegen tsare gida, sai dai suna yi wa wanda suka ga dama fara'a, kamar dai yadda kuke ganin waɗan nan yaran baban nasu.

"Zeezeena kun yi sallah?".

Shi ne tambaya ta farko da wannan uban na garin ya fara yi masu, ya yi maganar kuma yana sakewa Khadijah ledar fruit dake a hannunsa, yaran kirki, yana da kyau duk wata uwa ta koyawa ƴarta karɓar abin da mahaifinsu ya shigo da shi, hakan shi ne tarbiya.

Khadijah ce ta bashi amsa da. "Mun yi baba, amma mama bata yi ba, tana can suna hira da wannan Aunty Hauwar ta gidansu Khadijan nan na islamiyyarmu".

Dariya kaɗan Haidar ya yi yana faɗin. "Ke yanzu Khadijah waye ya tambayeki mama ta yi sallah ko bata yi ba? Ba dai ke kin yi ba? To Allah ya karɓa, ni bana hanaku faɗi ba'a tambayekun nan bane wai?".

Ɗaure fuska Khadijah ɗin ta yi tare da wucewa ta nufi cikin parlourn tana turo baki, ita a dole Yah Haidar ya shiga maganarta ba da shi take yi ba, ranta ya ɓaci.

Wucewa wajen ɗan madaidaicin kitchen ɗin nasu Haidar ɗin ya yi, a ciki ya ajiye kajin tare da ledar cefenen da yake a hannunsa, sannan ya fito ya nufi wannan ɗakin samarin da yake a harabar gidan.

Ita kuwa Zainab baba ya ɗagata sama suka nufi cikin parlourn.

Bakinsa ɗauke da cikakkiyar sallama ya shigo cikin parlourn.

A tare Aunty Hauwa da maman nasu suka amsa mashi sallamar. Ƙarisowa ciki ya yi tare da wucewa ya nufi ɗaya daga cikin ɗakunan dake a cikin parlourn, har cikin ransa yake jin daɗin shakar wannan daddaɗar kamshin turaren wutar da yake tashi a cikin parlourn, bai ce da Aunty Hauwa ko sannu ba, da alama irin mazan nan ne da idan bakin matansu sun zo gida ba su kulasu, in dai ba su ne suka ɗaga masu gaisuwa ba, to ko sannu ba zasu ce masu ba, ko kallon in da suke ma ba zasu yi ba, dan haka shi ma dai ko kallon Aunty Hauwa ɗin bai yi ba, ya sa kai zai wuce abinsa, yana ɗauke da Zainab a saman kafaɗarsa.

Cikin sauri Aunty Hauwa ɗin ta ɗaga mashi gaisuwa tana wani kara faɗaɗa murmushin da yake a saman fuskarta.

A takaice ya amsa mata da amsa ɗaya wato lafiya, ya amsa kuma ba tare da ya kalli in da take ba, daga haka kuma yasa kai sai cikin bedroom nasa abinsa.

Ajiye ladar da ta karɓo daga hannun baban nata Khadijah ta yi a tsakiyar parlourn, sannan ta yi sauri ta bi bayansa izuwa cikin ɗakin nasa.

Miƙewa Aunty Hauwa ta yi tana faɗin. "Babansu Zainab ya dawo, bari na je gobe zan dawo mu karisa maganarmu".

Da sauri maman tasu ta ce. "A'a tsaya ki sha fruits mana".

Ba kunya ta ce to a bata, ita kuma maman cike da zumuɗi ta buɗe ledar ta fara haɗo mata komai ɗaɗɗaya kamar ita ta kawo ta ajiye.

Kuskure ne idan mijinki ya sayo abu ki ɗauka ki yi kyauta da shi ba tare da saninsa ba, ansan cewa duk abin da zai sayo ku ya sayowa, amma kuskure ne ki kyautar baki tambaye shi ba, koda ƴan uwanki zaki bawa, yin hakan wlh sam bai dace ba, kina zubar da kima da kuma darajarki ne a gabansa, kuma hakan yanasawa namiji ya ji ya daina sha'awar saya maku abu idan ya fita, dan zai ga kamar baku ɗauki abin da mutunci da daraja ba, tabbas idan kin tambaye shi zaki yi kyauta da shi zai yi wuya ya hanaki, wannan tambayarsa da zaki yi ɗin zai kara maki kima da daraja, zai kuma sa mijin naki ya ji cewa yana da kima a idanunki da har zaki tambaye shi kafin ki yi kyauta da abin da ya saya maku, koda bai nuna maki ya ji daɗin tambayarsa da kika yi ɗin ba, wlh ina mai tabbatar maki ba ƙaramin daɗi suke ji ba, dan haka koma me ya kawo koda kannenki zaki bawa, ki tambaye shi cewa zaki bawa su wane kaza abu kaza, musamman ma idan a lokacin ya kawo abin, yasan adadin yawansa da in kin kyautar zai gane, wasu mazan in kin tambayesu zasu ce maki to ki bayar mana ba ke suka kawowa ba? Kada ki damu wlh suna jin daɗin tambayar, kuma kada amsarsu yasa gobe ki fasa tambayarsu, ki tambaya ɗin zai fi.

Ai kuwa ita dai maman su Zainab duk ta haɗawa Aunty Hauwa fruits ɗin nan komai ɗaɗɗaya, ta ɗauko wani leda daga cikin kitchen ta sanya mata a ciki, sannan ta rakota har kofar gida, sai zuba godiya Aunty Hauwa ake yi kamar me.

Naira dubu ɗaya mamansu Zainab ɗin ta bata a kan ta hau abin hawa zuwa gida. Sai murmushi take yi tasa hannu ta karɓa, tana ta zuba godiya ta tafi.

Ita kuma Maman Zainab ta juya ta dawo cikin gida.

A parlourn ta isko su Zainab suna zaune, bata ce da su ko sannu ba ta yi saurin wucewa cikin ɗakin baban nasu, dan ko ba'a gaya mata ba tasan ya fito daga wanka ne ya ce su Zainab su je parlourn bari ya sanya kaya, dama haka yake yi da su.

A hanzarce ta faɗa cikin ɗakin baki ɗauke da sallama, daidai lokacin yana ƙoƙarin zura jallabiya a jikinsa.

Ƙarisowa kusa da shi ta yi tana faɗin. "Ka yi hakuri baban Zainab, yau Hauwace ta tsayar da ni ban zo na fitar maka da kayan sakawa ba".

Fuskarsa a ɗauke da ƙayatattcen murmushi ya bata amsa da. "Kada ki damu, ai kullum kina fitar mun, dan yau kawai baki yi ba ai ba komai, muje bari maje masallaci lokacin sallar issha ta gabato".

Dayawan maza suna bawa mata irin wannan masa da baban Zainab ya bata a yanzu, wanda kuma magana ta gaskiya wlh ba har cikin zuciyarsu wannan amsa take ba, suna dai faɗa ne kawai, dan haka mata sai ku kiyaye, kada ki bari ya maimaita maki irin wannan amsa sau biyu zuwa uku, daga haka za'a fara samun matsala, wani ma idan ya cigaba da maimaita maki sai ki ji ya bushe idanu wata rana yana ce maki ai bama ki taɓa fitar mashi da kayan sawa ko makamancin hakan ba, duk kuma ke kika fara jawowa kanki, kada ki bari dan kin yi bakuwa tasa ki fasa yi wa mijinki abin da kika saba yi mashi, idan bakuwar ba zata jiraki ki yi attending nasa na ɗan lokaci ba, to gara maki ta tafi zai fi, dan haka sai a kula sosai.

Murmushi ta yi ita ma tana mai kara bashi hakuri, cigaba da gaya mata babu komai ya yi kafin ya ɗauko perfume nasa mai daɗin kamshi da nufin ya feshe jikinsa da shi.

Hannu ta kai ta karɓi perfume ɗin ta fara fesa mashi tana mai yabawa kyan da ya yi. Ba karya fa babansu Zainab kyakkyawa ne sosai, sai dai chocolate color ne, ya fi mamar tasu kyau sosai, ita kuma ta fishi hasken fata, farace sosai, su Zainab duk shi suka ɗauko a kyau, sai dai ita Zainab ta ɗauko hasken mamanta, kyan babanta, ita kuma Khadija komai na baban ne harta launin fata.

Bayan ta gama fesa mashi perfume ɗin ne ta ɗauko mashi wayarsa babba da karamar da suke a saman shinfiɗaɗiyar bed nasu 6/7, gadon ya sha gyara kam, ba karya maman Zainab akwai ƙoƙari wajen sake jiki ta yi aikin gidanta da kyau da kyau, yanzu haka wannan jallabiya na jikin baban Zainab ita ce nan ta wanke ta zuba mata guga, sai kyalli take yi, ta sha iron, ita fa maman Zainab da alama gugan kaya baya yi mata wahala, dan harta bedsheet dake a shunfuɗe a saman bed ɗin nan ya sha guga sosai, da yake ma sun saba shan guga sai ka gansu da karin gugan ya fito ɓaro ɓaro, ya riga ya kama kayan, to abu ne da ake yi ba jiya ba ba shekaran jiya ba, an jima, dole kunga su kama karin guga.

Parlourn suka fito, a nan ya isko sanyin idaniyarsa wato ƴaƴan nasa, Zainab tana kallon Tv, ita kuma Khadija tana rike da wayar mamanta tana buga game.

"Zeezeena zan je masallaci amin addu'a".

Ya faɗa yana nufar kofar fita daga cikin parlourn. Har suna rige rige ita da Khadijah wajen zuba mashi addu'ar adawo lafiya Allah ya tsare ya kiyaye hanya.

Da amin ya amsa masu kafin ya fice. Har harabar gidan maman nasu ta rako shi kafin ta dawo wajen famfo dake harabar gidan ta ɗauro alwala, a lokacin aka fara kiraye kirayen sallar issha.

Fitowa daga nasa ɗakin Haidar ya yi, cikin sauri ya kariso wajen famfon dan shi ma ya ɗauro alwala. Sannu ya yi wa maman Zainab ɗin tare da tsayawa a gefe guda yana jiranta ta gama.

Amsa mashi sannun nasa ta yi tare da tambayarsa ya kasuwa.

Alhdulillah ya amsa mata da shi, sannan ya ɗaura mata da cewa. "Sadiq dai yaki dawowa yau ɗin ko?".

Ɗagowa ta yi daga wajen fanfom tare da kasheta tana faɗin. "Ba yadda ban yi da shi ba a kan ya dawo, ya ce mun sam shi bai kalli mama sosai ba, wai sai jibi zai dawo".

Ta kai karshen maganar tare da wucewa ta nufi hanyar komawa cikin parlourn.

"Gaskiya Sadiq bai kyauta mun ba, sam goben nan ban so fita kasuwa ba, dan ina da wanki da ɗan aikace aikace da zan yi a ɗakinmu, amma shi ne yaki dawowa, next time ba zan barshi ya yi tafiyar nan ba".

Murmushi kaɗan ta yi tana faɗin. "Ai kun fi kusa". Daga haka ta wuce ciki abinta.

A parlourn ta isko su Zainab ɗin a saman dadduma, sallah suke yi, wucewa nata bedroom ɗin ta yi, dan ta biya sallar mangariba kafin ta ɗaura da issha.

Bayan sun idar da sallar, zama suka yi a saman dadduma Khadija tana karawa Zainab karatun malumat da Nahhu, a haka babansu ya dawo daga masallaci ya samesu, a lokacin kuma mamansu ta idar da nata sallar har ta zo ta ɗauki fruit ɗin da ya kawo ta wankesu tsab, ta zuba masu su a cikin plate tare da sanya masu wuƙa a saman plate ɗin wanda zasu yanka fruit ɗin, ta ajiye a tsakiyar parlourn haɗe da abincin darensu, akwaita da ƙoƙarin aiki kam, bata da son jiki, bayan ta yi dukka wannan ma kitchen ta wuce ta hau shirya kayan cefanen da Haidar ya shigar dasu ciki, su curry ne dasu maggi, kayan kamshi da dai sauran kayan girki, su tattasai da attarugu ne kawai babu a ciki, baban Zainab akwai shi da iya sayan kayan kamshin girki, ya iya cefene sosai kamar wata mace, idan ya yi cefenensa ma yafi wata macen.

Bayan ta shiryasu cikin robobin kayan miyarta ne ta dawo ta ɗauki kayan miyar da Khadijah ta ajiye mata a tsakar harabar gidan, tomatoes ne da su attarugu, dama su babansu bai cika sayo irinsu a cikin cefenensa ba, da yake cefenen sati sati yake yi, su kuɗi yake bawa maman nasu ta saya.

Kitchen ta kai kayan miyar ta shiryasu yadda ya dace, dan na miyar gobe da safe ne, dama haka suke yi kullum, tun da yamma a hanyar islamiya Khadijah take yo masu cefanen su tomatoes na miyan washegari, dan su ajiye komai ready, saboda kada su Khadijah su yi lattin zuwa makarantar boko a dalilin jiran girki ya nuna.

A parlourn ta isko baban nasu tare da Haidar sun dawo daga masallaci, a kusa da baban ta zauna tare da fara ƙoƙarin zuba masu abinci, dan duk zaman cin abinci suka yi, da alama da yunwa suka dawo daga kasuwar nan.

Jawo plate na kayan fruits ɗin nan baban nasu ya yi, fuskarsa ɗauke da
End Ads