x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 42 - RAWANIN ZALINCI STEP 1

  • 123001 words
  • 126000 words
  • Out of 297772 words

Category: Love Stories

Views 397

10 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
bata cewa komai saboda zalinci, sai dai ta kawar da kai, dama na gaya maku uwar bata da hali mai kyau. Sai dai ko da ta ce ba zata sake zuwa gidan ba tana hakura ta sake zuwa, saboda abincin da take samo masu su ci da iyayenta, mahaifinsu ya manyanta sosai, baya iya yin aikin karfi, amma yana iyaka bakin ƙoƙarinsa!.

Wata rana mamarsa tana ƙasa ita kuma Jasrah tana sama tana goge goge, sai ya ce ta je ɗakinsa ta gyara mashi, kamar zata ce ba zata je ba, amma saboda tsoron mamar tasa yasa ta je ta fara gyara masa. A nan ya iskota tana faman gyara mashi bed ɗinsa, ai kuwa yana zuwa ya turata saman bed ɗin tare da ƙoƙarin yi mata fyaɗe ta karfin tsiya, tana ƙoƙarin yin ihu ne ya yi saurin toshe mata baki da hannunsa. Hakan yasa ta fara ƙoƙarin kwatar kanta ta karfin tsiya a in da suka fara kokawa, ya sanya karfi zai yi mata fyaɗe ita kuma ta sanya karfi zata kwaci kanta.

Da yake mummunar kaddara ta gifta a tsakani sai ta sanya hannu tana laluɓar abin da zata buga mashi, cikin ikon Allah ta ɗauko kwalbar mardbe da ya yi amfani da shi ya barshi a saman bedside drawer ba'a fitar ba, ai kuwa yana danne da ita yana ƙoƙarin cire mata riga, bata yi wata wata ba ta buga mashi kwalbar a kansa, hakan yasa ya tashi daga kanta a haukace, saboda azaban zafi da ta ziyarce shi.

Abinku da yarinta, zuciyar kuruciya tana ɗebansa, cikin fusata ya kwace kwalbar daga hannunta tare da fasata a ƙasa, tana ƙoƙarin guduwa ta fita daga cikin ɗakin ya rikota da nufin ya kasheta da kwalbar, dan yana ɗaukarta a ƙasƙantacciyar ƴar aiki mara galihu, koma me ai baiwarsu ce ita ɗin, ko ya kwasheta ya kashe banza a banza.

Wage baki ta yi a in da ta zunduma ihu da karfi, a zuciye ya kai mata duka a bakin nata da ta yi ihun, ba shi ta haɗiye ihun da take ƙoƙarin kurmawa a karo na biyu, gadan gadan ya yi niyar kasheta, sai dai cikin ikon Allah ta samu ta ɗauko ɗaya daga cikin kwalaben da suka yi saura a kasan wanda ya fasa, a ƙoƙarin ta yi mashi barazanar kada ya kara matsowa kusa da ita, sai kuma mummunar kaddara ta gifta ta caka mashi wannan kwalbar a cikinsa, wannan ita ce sanadiyyar mutuwarsa kenan.

Wannan ihu da ta yi na farko yayansa ya ji ihun nata, hakan yasa ya nufo ɗakin, ya shigo kuma dai'dai lokacin da ta caki Ameer ɗin da kwalbar har ya faɗi a saman bed ɗinsa da yake yana a kusa da bed ɗin dama, hakan yasa yayan ma ya kurma ihu mai sauti wanda ya ja hankali kowa da yake gidan. A guje suka nufo ɗakin, kafin ma ayi wani yunƙuri Ameer dai ya ce ga garinku, rai ta yi halinta, wannan shi ne abin da ya faru, ko da aka kira jami'ai sai cewa mamansa ta yi ai daba Jasrah bata kaunar Ameer, kuma ta taɓa cewa sai ta kasheshi a baya lokacin da ya mareta, to shi ne yanzu ta bishi har cikin ɗakinsa yana kwance ta kashe shi.

Da jami'an suka tambayi cewa ina shaidar maman na cewa Jasrah ta taɓa yin ikirarin zata kashe Ameer, sai ta gabatar da shaida na farko yayan Ameer ɗin, da kuma sauran ƴan aikinta wanda dan dole suka amsa da anyi hakan, dan kawai basu da zaɓi da ya wuce hakan in dai suna son cigaba da rayuwa su kuma cigaba da yin aiki, haka suka bi bayan karya suka rufawa Ameer asiri na cewa shi yake neman lalata Jasrah, suka ɓoye wannan magana, kuma kowa na gidan yasan da cewa tabbas Ameer shi yake neman Jasrah da faɗa, saboda wani lokaci idan tana tsaka da yin aiki tare da sauran ma'aikatan gidan ya zo wucewa zai kai mata mari a mazaunanta a gaban kowa, kuma ya wuce ya mari banza, so sun san komai, amma basu da zaɓin da ya wuce su amsa maganar maman Ameer ɗin a matsayin gaskiya.

Wasu matan wlh munafukai ne na karshe, Maman Ameer dai da kanta ta goge ɗaukar CCTV camerar da yake parlourn wanda ya ɗauki video Ameer ɗin lokacin da yake cewa Jasrah ta je ta gyara mashi ɗaki, sai ta goge wannan ɗauka dan ta kara tabbatar wa da jami'ai cewa tabbas haka kawai Jasrah ta shiga ɗakin Ameer ta kashe shi saboda ƴar tsama da ta taɓa shiga tsakaninsu har ya mareta, ko da aka tambayeta wace tsama ce, sai ta ce ai Jasrah ɗin ce ta zubawa Ameer ɗin tea mai zafi a jiki bisa rashin sani, shi ne shi kuma ya fusata ya mareta, shikenan ta ce ba zata barshi ba. Haka dai suka shirya karya da gaskiya tare da shirya hujjojin da dole sai ka yarda da maganar tasu, wannan dalilin yasa aka kai Jasrah kotu ba tare da ɓata lokaci ba aka yanke mata hukunci kisa daga nan sai gidan AAJ za'a tsareta zuwa lokacin da zata kai munzalin karɓar hukunci kisa kamar yadda ta kashe Ameer ɗin.

Iyayenta sun yi kuka ne har mahaifinta ya kwanta jinya na tsawon lokaci, haka kanwarta Alveena, mahaifiyarsu har yau bata dai'na kuka ba, suna zuwa AAJ ɗin ziyartar Jasrah ɗin, amma ba koda yaushe ba, saboda basu son zuwa su ganta a cikin wani hali, idan suka koma gida a ranar da suka ziyarceta kwana suke yi basu yi barci ba bayin Allah. WANNAN SHI NE LABARIN SUHANA DA KUMA DALILIN ZUWANTA AAJ, BA SAI NA TSAYA YIN DOGON BAYANI BA NASAN KUN FAHIMCI IN DA AKA DOSA!.

Mu koma kan labarinmu.❤️‍🔥

"Shikenan Leesharh, bari na je lokacin cin abincin yana kurewa, kuma kin san komai yana da lokacinsa a cikin gidan nan, dan haka bari na je na ci nawa kada time ya kure banci ba a hanani". Cewar Jasrah. Ta kai karshen maganar tana miƙewa tsaye.

Da idanu kawai Leesharh ta bita har ta fice daga cikin ɗakin, nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tare da sanya hannayenta dukka biyu ta dafe ƙuncinta, duniyar tunani ta afka, yau gabaɗaya tana cikin damuwa sosai da sosai.

🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️

IDAN MUKA WAIWAYA WAJEN SU KAMRAN KUWA WATO FOREST.🔥🤍

Zaune suke a ƙasar wata ƙatuwar dutse mai girma dake kusa da wannan ƙoramar na kusa da wajen su Pretty, da alama an fasa yin harbi da kifiyar kenan, akwai itatuwan mangori sosai a ta kusa da wajen, hakan yasa suka samu ishasshen ƴalwar inuwa sosai a wajen.

Yana zaune ya jingina da jikin dutsen ya kuma lumshe idanunsa tare da ɗan ɗaga kansa sama kamar mai yin tunanin wani abin, Sweetie na zaune a gefensa na hagu saman farin yashin da yake a wajen. Hannunta na rike da lemun zaki tana ɓarewa duk da bata gani, Kamran ɗin ne ya ciro masu lemun a wata bishiya dake ɗan nesa da ƙoramar. Ita kuwa Pretty sarkin kauɗi tana zaune kusa da shi sosai, ta ɗaura ƴan kyawawan kafafun nan nata a saman nasa ƙafafun tana ɓare nata lemun, idan baku manta ba Kamran ɗin bai fito da wukarsa bane yasa suke ɓare remun da hannu, ba halin yankawa.

Shi dai Kamran ya afka duniyar tunanin abin da yake damunsa tun daga haɗuwarsa da su Pretty, kullum yana yawan mafarkinsu sosai, ga shi a duk lokacin da ya haɗa idanu da waɗan nan sexy eyes ɗin nata sai ya ji gabansa ya faɗi, tana rikita shi, ya rasa me dalili. Haƙiƙa idanunta suna da rikita mai kallonsu, wasu irin shegun sexy eyes ke gareta, amma shi nasa rikitarwar na daban ne, har tsoron kallon cikin idanun nata yake yi, gata da shegen daddaɗar zazzakar murya wanda idan ta yi magana sai ya ratsa jikin duk wani mai sauraro, ko baka son haɗa idanu da ita idan ta yi magana sai ka ji duniya baka da burin da ya wuce ka ɗaga idanu ka kalli face nata, saboda muryar nan tata akwai ratsa zuciya, sannan ga ɗan banzan shiga rai garesu daga ita har Sweetie, bugu da ƙari ga ɗan banzan wayo kamar wasu renon tsofaffi.

"Kamran ga lemun nagama ɓarewa".
Cewar Pretty, ta yi maganar tana kai hannu zata taɓa lallausan kumatunsa.

Ajiyar zuciya ya sauke tare da waro idanunsa a hankali, dai'dai lokacin ta kai ɗan kyakkyawan lallausan hannunta saman kumatunsa, a tunaninta barci ya ɗan yi shi ne zata tashe shi.

Karaf idanunsa ya sauka cikin nata. Ɗauke hannunta daga saman kumatun nasa ta yi tare da miƙo mashi lemun da yake a ɗayan hannun nata tana mai do da kallonta izuwa saman gashin kansa, duk da yana sanye da hula baka iya ganin gashin kan nasa sosai, amma ya ɗan fito ta gaban goshinsa.

"Kamran kana da gashi sosai kamar mu".
Ta faɗa tana mai cigaba da kallon kan nasa.

Nisawa ya yi tare da karɓar lemun. "Waye ya gaya maki gashina kamar naku ne?".

Gyara zamanta ta yi tare da ɗauka kafafunta daga saman nasa, ta yi zama irin na masu cin abinci ta lankwashe kafafunta dukka biyu suna fuskantar juna.
"Babu wanda ya gaya mun, kawai na gano yawan gashin naka ne duba da yadda ya cika hular kanka, hakan yana nufin gashin na dayawa sosai".

"Pretty ke dai kin cika sa ido".
Ya bata amsa yana mai raba lamun da ya karɓa daga hannun nata gida biyu. Bayan ya raba biyu sai ya miƙo mata rabi.

Maƙe mashi ɗan kafadarta ta yi alamar bata so tana faɗin.
"Ni bana saka ido, daga magana kawai sai ka ce na iya saka ido? Kuma ni ba zan sha lemun ba".
Ta kai karshen maganar tare da yunƙurawa zata miƙe, ita a dole ta yi fushi tun da ya ce mata mai sa ido.

Cikin hanzari ya kai hannunsa ya riƙo nata hannun yana faɗin.
"To sarkin fushi yi hakuri, am so sorry baki da sa ido shikenan?".

Tana ƙoƙarin sake yin magana Sweetie ta katsesu da cewa.
"Hmmmm ita kam ma ai ta ji daɗi tun da tana da idon da zata yi kallo har ace mata tana sa ido, ni kam sai dai na kalli abu da zuciyata".

Wani irin yanayi mara daɗi dukkansu suka ji da jin maganar Sweetien, haƙiƙa maganar ta taɓa zuciyar Kamran sosai, wani irin tausayinta ne ya kamashi, ya sani rashin ido babu daɗi sam, ga shi a yadda ta yi maganar kamar zata yi kuka sai ka ji kalaman nata sun ratsa maka zuciya sosai, sai ka tausaya mata duk taurin zuciyarka, ita ma Pretty da take sarkin kauɗi ta ji kalaman har cikin ranta bare shi Kamran da dama already yake sarkin tausayi mai zuciyar musulman farko, ai dole ya tausaya mata.

"Our Sweetie idanunki zasu buɗe nan bada jimawa ba kin ji ko? Kada ki damu kanki, zan nemo maki magani".
Cewar Kamran, ya yi Magana da wata iriyar murya wadda da ka ji ta zaka san lallai maganar tata ta taɓa mashi zuciya.

"Allah yasa ka samu maganin Kamran, ina son idanuna su buɗe, ina son na ga ya fuskarka take? Ina son sanin kamanninka, saboda kai kawai nake burin idanuna su buɗe".

Har lokacin yana rike da hannun Pretty bai saki ba ya bata amsa da. "Nan ba da jimawa ba our Sweetie, zaki samu lafiya sosai kamar baki taɓa yin ciwo ba".

"In Sha Allah, zan tayata da addu'a sosai nima". Cewar Pretty.

Maido da kallonsa a kanta ya yi yana kallon ɗan bakin nata da ta furta In Sha Allah ɗin.
"Take your orange".
Ya faɗa yana mai miƙo mata rabin lemun.

Sarkin rigima kara maƙe mashi ɗan kafaɗar tata ta yi tare da girgiza mashi kai. "I don't want, ba ka ce mun sarkin fushi ba? So don't talk to me again".
Tana magana tana turo baki.

"Oh sorry ba zan sake ba ai".
Ya faɗa tare da miƙo mata lemun.

"To sake mun hannu na sai na karɓa".

A hanzarce ya saketa, shi kwata kwata ma ya mance da cewa ya rike mata hannu, ya ji hannu mai laushi luwai luwai.

Karɓar lemun ta yi tare da komawa ta gyara zamanta da kyau, sarkin rigima ce sosai Pretty.

Ta ƙasan idanunsa yake satar kallonta yadda take tsala lemun nata tsala sala, a hankali take kai sala ɗaya ɗan bakinta, idan ta kai ɗin ma ba dukka take turawa a cikin bakin nata ba, sai ta gutsira ta raba biyu, ta rike rabi a hannu ta bar rabi a cikin ɗan bakin nata tana tauna a hankali hankali kamar bata son motsa ɗan bakin, da alama akwai yauki a tattare da ita, tana kara girma kuma hakan yana kara bayyana.

Sosai yake jin daɗin kallon yadda take shan lemun, hakan yasa ya mance da nasa baya sha, saukar zazzaƙar voice ɗinta a dodon kunnuwansa ne yasa ya ɗan firgita tare da dai'dai nutsuwarsa cikin hanzari kamar wani mara gaskiya.

"Kamran muje ka cigaba da koya mun harbin kwari da bakar ko?".
Shi ne abin da ta faɗa wanda ya fargar da shi daga satar kallonta da ya lula. Ta yi maganar ita kuma ba tare da ta kalli in da yake ba.

Ƙasa da idanunsa ya yi tare da sanya hannu ya fara sala lemunsa kamar yadda ya ga ta yi, bai taɓa shan lemu irin haka ba, bai ma taɓa ganin an raba lemu a haka ba sai yau da ya gani a wajenta, shi kullum Mammarsa ce take yanka masu da wuƙa sai su ɓare su sha, yau ya ga sabon salo na tsala ta tsala sala.

"Pretty koya maki harbi da kifiya sai na shirya, gara mun na fara koya maki busa tukun nan".
Ya kai karshen maganar tare da kai lemu sala ɗaya ɗan bakinsa ya tura ciki, a hankali ya fara sha.

"Amma kuma ɗazun kai ne fa ka ce harbi da kifiya zaka fara koya mun?".
Ta yi maganar a ɗan shagwaɓe kamar yadda take zubawa Sweetie shagwaɓa, sannan ta yi maganar tana kallon kyakkyawar fuskarsa tana aikin turo ɗan baki.

A hankali ya ɗago idanunsa ya saukesu a saman kyakkyawar fuskarta. "Zan koya maki, amma ba yanzu ba gaskiya, sai na yi magana da mamana na tambayeta wani abin tukun nan, yanzun na ji na kasa ne, ba zan iya ba".
Ya faɗa muryarsa a ɗan kasale, alamar kwata kwata dai baya son ya tuna da zancen koya mata ɗin, dan shi kaɗai yasan me yake ji a duk lokacin da suka haɗa jiki, komai ƙanƙantar haɗuwar fata da tsokan jikin nasu sai ya ji jikinsa ta amsa.

Matsowa kusa da Sweetie ta yi tare da kwantawa a kasa a wajen ta tada kai da laps na Sweetie, dama kun santa sarkin son jiki ce kamar mage.

"Ki tashi a jikin Sweetie kada ki ji mata ciwo sarkin rigima kawai". Cewar Kamran, yana magana yana cigaba da shan lemunsa.

"Sweetie in yi kwanciyata ko?". Ta tambaya tana mai da kallonta izuwa samar fuskar Sweetien.

"Kullum da kike kwanciya a jikin nawa izinina kike nema ne?". Sweetie ta bata amsa tana mai kai hannunta a saman fuskar Prettyn, dogon hancinta ta laluɓa ta ɗan ja.

"Wash Allah na, Sweetie kin fara ko?". Ta faɗa tana rike hancin nata da hannu ɗaya, tana kuma turo baki.

Shiru Kamran ya yi yana kallonsu gwanin birgewa, suna son junansu sosai, akwai fahimta sosai kuma a tsakaninsu, dan Sweetie tana da hakuri ga hangen nesa sosai yarinyar duk da bata gani, Pretty kuma shagwaɓa, kauɗi, saurin kuka, son jiki, rashin iya juriyar yunwa, da dai sauransu duk ta haɗa, hakan kuma baya sa su yi faɗa a tsakaninsu, duk kuma hakurin Sweetie yasa basu yin faɗar, da ace kamar Prettyn take ba hakuri ai da tuni kullum sai sun yi ta faɗa, ita fa Pretty ko yunwa ta fara ji sai ta yi kuka saboda rashin hakuri.

"Daga yanzu ki dai'na kwanciya a jikin Sweetie tun da kin ga bata da lafiya, idan kina jin kwaɗayin kwanciya ki zo ki kwanta a jikina, kada ki kara mata nauyi kan nauyi". Cewar Kamran, yana magana idanunsa yana a kansu sosai, saboda sun burgesa sun kara burgesa sun kara burgesa over to over.

"Yauwa Kamran gaya mata dai, ni yanzu ma ka duba mun ita ta yi ƙiba ne ko? Dan naji ta kara mun nauyi, da idan ta kwanta a kafata bana jin nauyi sosai, amma yanzu sosai take yi mun nauyi in ta kwanta". Cewar Sweetie.

Lumshe idanunta kamar mai jin barci ma ta yi abinta ta kyalesu, kamar bata jin me suke faɗa, tana jin Kamran yana gayawa Sweetien ai ta girma ne yanzu shi yasa take kara nauyi, amma sam taki kulasu, dan barci barci ma take ji, yanayin weather wajen ya yi mata daɗi sosai.

Sweetie da Kamran kuwa cigaba da hira a tsakaninsu suka yi cikin mutunta juna tare da nuna kula ga juna.

Kamar daga sama gurnanin Rocky ya doki doduwan kunnuwansu. Ai a dubu ɗari Pretty ta waro idanunta. Cikin sanɗo ta miƙe daga kwanciyar da ta yi, abin gwanin ban dariya ta fara rarrafawa a kasa kamar wata mage ta nufi Kamran, tana rarrafawa tana zaro idanu nan nata kamar ka ruga a kuje idan ka gansu, tana kuma rarrafawa tana ƴan waige waige tana neman ta ina zata gano ɓullowar Rockyn?.

Abin ya so ya bawa Kamran dariya, sarkin tsoro kenan, ji yadda take sanɗo tana rarrafawa kamar wadda ta je ta yi sata, kai wannan yarinya sai shirin Allah.

Yana tsoron ya yi mata dariya abin ya zamar masu rigima, dan haka sai ya yi kamar bai ganta ba, ya kawar da kansa. Kusa da shi sosai ta zo ta zauna, har da sanya hannu ta riƙo nasa hannun a cikin nata, cikin dabara tana yi tana zaro idanu ta kwantar da kanta a saman shoulder ɗinsa, sai muzurai take yi tana jiran taga ta ina wannan damusa mai gurnanin zai bayyana? Cikinta har ya ɗuri ruwa.

Ita ma Sweetie tsoro ne ya kamata, barema da ta ji Pretty ta tashi daga kafarta, sai ta ruɗe, a ruɗe ta fara ambatar sunan Prettyn da kuma tana tambayar Kamran Damusa ce ta sake dawowa zata cinyesu ko?.

Ɗan satar kallon sarkin tsoro Pretty ya yi, ta
End Ads