ta tashi, bayan ta koma gida tana ta neman layukansa, amma shiru ba ta samunsa a wayar.
Sai washegari ya kirata da wata lambar daban, ya ce mata yana bauchi cikin ƙoshin lafiya, da wannan lambar za ta din ga kiransa.
Jin muryarsa wasai ya sanya ta cewa "To amma yanzu zaka dawo ko?"
"Ko zan dawo ba yanzu ba, kewarki ce kawai take damuna"
"Dan Allah ka dawo ka ji babban mutum, manya ba sa haka, idan laifi muka yi mutanen kano, tuba muke yi kar a hora mu da yi mana yaji, ka san menene zan dafa maka abinci mai daɗin gaske, na san abun da ya saka bar garin zuwa yanzu ka huce ai ko? Zan yi maka girki"
Raihan yayi dariya ya ce "Matar raihan, kirarin nan kawai ya ƙara sanyaya mini zuciya, kar ki saka na ɗaukko mota na taho mana. Ke dai ki yi ta addu'a kamar yadda na ce miki kin ji ko?"
"To shikenan, amma dai ka yi tunani a kan lamarin nan".
Can gida kuwa Alhaji Tahir ya saka mami a gaba da masifa, tare da cewa duk in da ɗan sa yake sai ta fita ta nemo shi, dan ba a samun sa a waya, baya gida kuma baya office.
Abu kamar wasa, hankalin mami ma ya tashi, ba ta yi zaton raihan zai yi haka ba.
kwana kusan biyar, babu raihan babu dalilinsa.
Dr. Ya samu ummi ya ce mata ta shirya kayanta, washegari za su yi tafiya ta kwanaki uku, ta sanar a wurin aikinta.
Ummi tayi ta mamakin, ina za su je haka afujajan babu cikekken shiri babu komai.
Ba ta matsa masa da tambaya ba, ta shirya kayan kamar yadda ya umarce ta.
Mami kuwa, Anty rakiya ta bata shawarar ta je har gida ta ci mutuncin ummi, kuma ta tursasata ta gaya mata in da raihan yake, dan ba zata kasa sani ba.
Alhaji Tahir ya shigo a fusace ya ce "Kin yi naki role ɗin, barkana tun da na san in da ɗa na yake, amma bari na gaya miki wani abu, idan har kin cigaba da dagewa ba za ayi auren nan ba, to ki tabattar da zan kawo yarinyar nan matsayin matata ta uku, dan ba zaki zubar mini da mutunci a idon duniya ba"
Gabanta ne yayi wata irin mummunar faɗuwa, wayarta ta fara ringing, cikin rawar jiki ta ɗaga. Saboda kura ta san gidan mai babban sanda bijirewa ɗaga wayar ka iya jefata cikin matsala.
"Bilki, ashe baki da mutunci baki da hankali? Ashe wayewar ta ki ta ƙarya ce, saboda wulaƙanci da rashin mutunci ke da ba a aure, da zamu bari Tahir ya aureki ne? Ke kin san auren zumunta muke yi, da matarsa ƴar uwassa tana son shi yana son ta, ya auro ki, mu a cikinmu waye ya hanakk zaman lafiya? Saboda rashin kunya yaro ya kawo mace yana so ki ce a'a, saboda wulaƙanci idan shima ya faɗa shaye-shayen ki ce me? Bar ganin ke ki ka haifi raihan, wallahi ba zamu lamunci son zuciya ba, ko tsohuwa ya ce yana so, zamu bashi goyon baya, ba dan Allah ya sa ya taho nan bauchin wurin mu ba, wani wurin yayi ba, to ahir ɗinki wallahi idan ba haka ba da ni ki ke zancen, kuma bauchi ya zo kenan, ku nemi wanda zai riƙe muku kasuwancin naku, tun da kin hana shi auren".
Cikin tsuma Mami ta ce "Dan Allah Hajiya Aisha ki yi haƙuri, in sha Allah hakan ba zata sake faruwa ba"
"Oho miki ta cigaba da faruwar ma, kin ce ya fasa aure, ai ke uwa ce yayi biyayya ya janye, amma ya ce a gaya miki, shi da aure har abada, sai kuma ki shirya idan ya kawo miki ɗan gaba da fatiha ki karɓa ki riƙe tun da ba ki da hankali" ta kaste wayar.
What's app only please, masu so daga farko su yi joining channel ɗin nan.
08081012143
Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya
Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.
And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ayshercool.
PAID ADVERT!.
Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku
Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi
Man garan gashi
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921
*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*
BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.
*CUTARWA*
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
Wani irin gumi ne ya dinga gangaro wa mami, duk da yadda sanyin AC ke ratsa ko ina a falon.
Raihan ƙararta ya je ya kai wa wannan masifaffiyar yar uban nasa kenan? tuno maganar Alhaji Tahir, da tuni ya bar falon da yayi ya sanya ta jin wata muguwar gudawa, saboda yadda cikinta ya murɗa mata.
Afujajan ta fita ta nufi sashinsa, har da tuntuɓe.
"Wallahi Baka isa ka gaya mini maganar da zata hana ni sukuni ka fice ka bar ni ba, kai yanzu saboda abun kunya goɗai-goɗai da kai sai ka auri yarinyar da ɗan ka ya ce yana so?"
Alhaji Tahir ya ce "In dai haka shi ne mafita a gareni me zai hana? Ku mata ku kuka san wani abun kunya, mu maza abu in dai mu yayi mana ba ruwanmu da abun kunya, kuma ina sake tunatar da ke, bana magana biyu, wallahi da gaske nake, sai dai idan na aureta wanda ba zai iya zama da ni ba ya ƙara gaba, shawara ta rage ga mai shiga shiga rijiya" ya ƙarasa maganar tare da ɗaukar wayarsa ya fita.
Kamar wadda ta zare, haka ta sake kwasa har da gudu, ta tafi ta kira Anty rakiya a waya.
Rakiya na ɗagawa mami ta fashe da kuka, "Anty rakiya na shiga uku na lalace"
"Wane irin kin shiga uku, meyafaru ba yanzu muka gama waya lafiya ba?"
"Ashe raihan bauchi ya tafi, ya je ya haɗo ni da wannan masifaffiyar matar yayar babansa, kin ga yadda ta ci mini mutunci kuwa? shi kuma Alhaji wai idan ban bari an yi auren ba, wai shi zai aureta ya kawota gidan nan a matsayin matarsa"
Anty Rakiya ta ce "Kai haba, dalla rabu da shi, barazana ce kar ki fasa wallahi, kar ki yadda a kawo miki bazawara a matsayin sirika"
"Anty Rakiya waye ya gaya miki Alhaji Tahir yana barazana ne? Magana ɗaya yake yi ko ta yi maka daɗi, ko kuma akasin haka, har rantsuwa yayi mini, na shiga uku, kuma wai raihan ya ajiye aikin nan ina na kama?"
Anty Rakiya ta ce "Taɓ, lallai raihan ba shi da hankali, to wallahi idan ki ka zuba masa ido, haka zai aurota ya fi ƙarfinki, tun da har ya san yayi miki yaji, ki kira shi ki ce lallai ya dawo dan ubansa"
Mami cikin takaici ta ce "Lamarin fa ya wuce yadda ki ke tunani, kin san taurin kan raihan kuwa? To cewa tayi wai ba zai dawo ba, ya bar aikin kenan, ya kuma ce idan aka karɓo kuɗin auren nan, shi da aure har abada, ga babansa ya ce idan aka fasa zai aureta, na shiga uku ina na kama? Kin ga suna nema su haukata ni, raihan kafiya da taurin kai kamar ubansa, idan ya ƙi aure ya lalace yaya zan yi?"
Anty Rakiya ta ce "Ai kawai ki dage ki samu ya dawo tukuna, ki kira shi a waya"
"Wayoyin da duk ya kashe su, ina zan yi?"
"To ki koma ki samu babansa ki lallaɓa shi, ya dawo da shi kar a rasa wannan damar kuma ta kasuwancin nan "
Mami tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, zan kira ki mayi magana anjima" ta katse wayar ta ajiye tana wani irin haki, ita ba mai asma ba.
***
Dr. suna tafe a mota da shi da ummi, ya ce "Mamana zaki ga zamu yi doguwar tafiya, ba sayar da ke zan yi ba abun alkhairi ne"
Ummi ta yi murmushi ta ce "Idan sayar da ni ɗin ma ka yi ai na saidu kawu"
Yayi murmushi ya ce "Idan na sayar da uwata ina na kama? Yakamata ace kin yi azumin farinciki kan mu yi tafiyar nan"
"To Ubangiji ya tabattar mana da dukkanin alkhairin da yake cikinta"
Ya amsa mata da "amin"
Ummi ta gaji da zaman motar nan sosai da sosai, sai dai tun da taga symbols da sunan borno, jikinta ya fara sanyi, har ta rasa tunanin me ma za ta yi ne?.
Kawu kuma ya mayar da kai sosai a kan tuƙinsa, sai lokacin salla ya tsaya suka yi salla, ya saya mata abinci.
Ta tuno lokacin da ya ɗaukkota daga gagarwa a wahale, ba sutura ga ciwo, ko ba komai ta samu alkhairi a dalilin riƙonta da yayi
A ranta ta ce "Allah sarki kawuna, baba ya tafi amma ya bar mini Allah, Allah kuma ya bani kai, Allah ya kula da kai da zuriyarka".
Duk da ba ga saba baccin mota ba, gajiya ta sanya wani irin nannauyan bacci yin awon gaba da ita.
"Mamana tashi mun zo" a hankali ummi ta motsa tare da buɗe idonta, har suka fito daga cikin motar, ba ta iya cewa komai ba, sai bin wurin da kallo.
Ƙofar wani gida suka tsaya, dr. Ya ciro wayarsa ya ɗan daddana ya kara a kunnensa ya ce "Gamu mun zo"
Wani matashin saurayi ya leƙo ya durƙusa ya gaida dr. Sannan ya ce su shiga.
Suka shiga cikin gidan, ummi ta zubawa dattijon da suka tarar a tsakar ido, yana zaune a kan buzu, da Alƙur'ani bugun warshi a gabansa.
Dattijon ya miƙe tsaye yana yi musu maraba, tare da bin ummi da kallo, ba ta ɗaga niƙabin fuskarta ba, sai dai ta shagala da kallon sa ta san shi, amma a ina? Ta kasa tunawa.
Yayi musu jagora har wani matsakaicin falo, yana ta yi musu sannu da zuwa.
Suka gaisa da dr. Ummi ta gaishe shi, ya amsa mata cikin kulawa, sai dai bai tambayi wacece ba, kuma ya kasa daina kallonta.
Dr. Ya ce "Ina mutuniyar kuwa?"
"Wai sun fita barka a nan bayan layi, jikin ne ma ya ɗan motsa, amma Alhamdilillah mun gode Allah, bari azo a ɗora muku girki, ai bamu san zaku zo ba"
Dr. Ya ce "Ai alƙawarin da na ɗauka na zo cikawa, zuwan babu cikekken shiri, bari mu yi salla kafin su dawo".
Ya ja dr. Suka fita, bayan nuna wa ummi banɗaki, tayi alwala ta yi salla, ta nemi wuri ta kashingiɗa tana hutawa, saboda gajiyar da tayi.
Ummi ta ɗan jima a zaune, sannan dr. Ya shigo, shigowar ta sa yayi daidai da shigowar matashin da ya yi musu iso, ya kawo musu nono mai sanyin gaske, da nama fal malam ya ce a kawo musu da ruwa, dan azo a ɗora sanwa.
Ummi dai ta kasa sakewa ta ci, dr. Kuma sai hira suke yi da malam.
Dr. Ya ce "Malam ba ka ganni da baƙuwa ba ne? Baka tambayeni wacece ba"
Malam yayi murmushi ya ce "Tun da baka gaya mini ba, bai kamata na yi shishshigi ba ai, na ma zata ko mai ɗakinka ce, shiyasa ban yi magana ba, kuma na ganta sanye da niƙabi"
Dr. Yayi murmushi ya ce "Aishikenan, mama malam ne fa, baki gane shi ba?"
Ummi ta ce "Na sanshi amma na manta a ina?"
"To ki cire niƙabin ko zai gane ki"
Ummi ta jinjina kai tana ƙoƙarin cirewa, aka yi sallama.
Bayan matar farko ta biyun ma tayi, a nan take ummi ta daskare, ƙirjinta ya buga da ƙarfin gaske, ta ji tamkar numfashin ta zai bar ƙirjinta, wata irin tsuma ta ji ta fara yi, amma ta gaza motsawa.
Malam ya ce "Daga zuwa barka kun yi zamanku, gashi kun yi baƙi tafiyayyu daga kano"
Ta ce "Baban ummi ne?"
Malam ya ce "Eh shi ne, tun da shikaɗai ki ka sani a kanon ba"
Shigowa suka yi tare, tana riƙe da mayafinta a hannu, hannunta kamar amarya an yi mata lalle yayi jawur.
Ba ta kalli baban ummi ba, kai tsaye ummi ta zubawa ido, yayin da ummin ma ta zuba mata ido, tana jin yadda ƙirjinta ke lugude. Gaba ɗaya suka zuba musu ido, kai tsaye ta nufi ummi ta zauna a gabanta, tana cigaba da kallon ummi ta niƙabinta.
Ta miƙa hannu a hankali ta ɗaga niƙabin ummin, tayi tozali da fuskar ummin da a duniya bata ganin kyan komai, kamar yadda take ganin kyawun wannan fuskar.
A gigice ummi ta yi mata wata irin runguma ta fashe da matsanancin kuka, saroro mariya tayi, ta kasa taɓa ummi sai hawaye da ya fara zuba daga idonta.
Mama ta miƙa hannu tana faɗin "Ki yi mata a hankali ba ta da cikakkiyar lafiya"
Mariya ta buge hannun maman da ƙarfi, ta ruƙunƙume ummi, tana wata irin ajiyar zuciya kamar za ta fita daga hayyacinta.
Ta miƙa hannu ta warware mayafinta, ta lulluɓe da ummi da shi, ta ɗaukko mafici kuma tana yi mata fifita tana kuka.
Sai a yanzu suka gane wacece, malam ya sunkuyar da kai yana hawayen tausayin ƴar sa.
Ya zura hannu a aljihunsa ya ɗaukko wayarsa, ya kira Maryam a waya da kuma yaya ɗan lami.
"Ummina, kina cin abinci kuwa? Naga duk kin rame, iya tana yi miki wanka? Ko dai zazzaɓi ne a jikinki?" Tayi maganar tana ɗora hannu a goshin ummi.
Wasu irin jijiyoyi suka ɗaɗɗaga a goshin ummi, wani irin riƙo take yi wa mariya, tana jin kamar an sanyata a wata ni'ima.
Sun fi mintuna talatin a haka, sun ƙi sakin juna, mariya sai kakkare ummi take yi, kar wani ya taɓa mata ita.
Dr. Yayi gyaran murya ya ce "Yau na cika alƙawari ko?"
Ta jinjina masa kai, tana kuka ta ce "Wallahi ba zan taɓa yafe wa iya ba, Allah ya saka mini zaluncin da ta yi mini, ta ƙwace mini ummi bayan ba son ta take yi ba, ta ce ni na kashe mata ɗa, kalli yadda duk ummi ta rame, haka zan kwanta in yi ta mafarkin ummi tana kuka, tana cewa na zo na tafi da ita"
Ta ɗago ummi tana goge mata hawaye ta ce "Ki daina kuka kin ji ummana, ba zan sake bari a mayar da ke wurin iya ba, na san ba ta sonki ba ta ƙaunarki, ban san me ki ka yi mata ba, wallahi ba zan yafe mata ba, yaya ɗan lami yaƙi dagewa ya karɓo mini ƴa ta, kullum sai na yi kuka saboda ummi, yaya maryam ma ta hantare rannan wai kamar nikaɗai ce me ƴa, ki daina kuka kin ji ummina, da kaina zan din ga yi miki wanka, ina baki abinci, katifata zata ishemu mu din ga kwana tare, ba zan sake bari a kai ki wurin iya ba kin ji mamana"
Ummi ta ƙura mata ido, yadda mama ke wannan surutan daga wannan zuwa wancan tare da kasa gane ummi ta girma yanzu, ya tabbatar wa da ummi cewar mariya bata da lafiyr ƙwaƙwalwa.
Ta miƙa hannu ta ɗaukko ledar pure water, ta buɗeta ta saka wa ummi a baki tana faɗin "Na san ƙishirwa ki ke ji ummi, sha ruwa kin ji"
Babu wanda tausayin ummi da mariya bai kama a wurin ba, uwa kenan duk da ciwon ya motsa ba ta hayyacinta, amma hakan bai hanata gane ƴar ta ba, duk da shekarun da suka shafe basu haɗu ba.
Dr. Yayi gyaran murya ya ce "Alhamdilillah ala kulli halin, na gode Allah da ya sanya ummi da mahaifiyar ta suka haɗu, ba tare da ta Allah ta kasance ba. Ummi na yi miki laifi, kuma na yi muku duk da ina godiya da fahimta ta da ku ka yi.
Ummi ban ƙi sada ki da mahaifiyarki dan baƙanta miki ba, a lokacin da na ganota, tana cikin halin larura sosai, ba komai take ganewa ba, na yi fargabar haɗuwarku ba za ta yi daɗi ba, idan ku ka haɗu ta kasa gane ki, abu na gaba kuma ina tsoron halin da ki ke ciki, ya sanya ki ƙi zama ki dawo wurinta, alhalin kina tsaka da karatu, dan duk wanda yake ruwa, ko takobi aka miƙa masa zai kama, dan haka a matsin nan da ki ke, duk da kasancewar ki mai biyayya, zaki iya bujirewa ki zaɓi dawo wa gaban mahaifiyarki, ba tare da kin yi acheiving wani abu ba.
Wanda a lokacin babban burina da fatana, ki samu nagartaccen ilimi, da zaki iya tsayawa da ƙafafuwanki, ina fatan zaki yafe mini daga ke har mahaifiyar ki" yayi maganar a sanyaye.
"Ai dama kai na yafe maka, baka cuceni ba, amma iya iya iya, ban san me na yi mata ba,