x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 25 - CUTARWA

  • 72001 words
  • 75000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 496

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
kun fi kusa, ka kira su ka gaya musu mana"

Yayi murmushi ya ce "Shima zan gamu da shi ne, ko a waya baya nema na"

Ta ɗan yi murmushi ta ce "Wai ɗazu da ina bacci, da wa ka ke magana ne, ka ke ta faɗa?"

Ya ɗan ja guntun tsaki ya ce "Salim mana, wai zuwa yayi na bashi kuɗi zai yi gyaran mota".

"To meyasa ba ka bashi ba?"

"A kan me zan bashi? Duk iya ƙoƙarin da zan yi na yi wa yaran nan, dan su zama na gari, amma abu ya gagara. Yanzu daga shi har ɗan uwansa da a nutse suke, da yanzu yaushe zan din ga wannan zirga-zirgar?"

Bilki ta ɗan yi ajiyar zuciya ta taɓe baki ta ce "Laifin babarsu ne, da ta bari suka lalace".

Yayi saurin girgiza kai ya ce "No, Hajiya na iya ƙoƙarin ta a kan tarbiyyar yara, dan har ta fiki tsanantawa ma wasu lokutan"

Ta tsuke fuska ta ce "Eh, nice mai sake da tarbiyya kenan?"

"A'a mai gado ba haka nake nufi ba, ai kin ga matan duk lafiya ƙalau, gashi duk sun yi aurensu suna zaune lafiya, su ɗin ne dai, kuma shima na san jarrabawa ce, ba a barin ɗan Adam haka".

"Allah ya kyauta, amma nikam ba zan bari auta ya riƙa ba yazo na kasa contrilling ɗin sa ba, aure zan yi masa yana dawowa"

"To hakan ma yana da kyau, Allah ya zaɓa abun da ya fi alkhairi mai gadon zinari" yayi maganar yana jan hancinta.

"Ba wata mai gadon zinari, ka koma wurin dattijuwar matarka"

Kwashewa yayi da dariya, ya ce "Bilkisu, hajiyan ce dattijuwa Allah ya sa ta ji ki, ai shekarunta ba sa nunawa, saboda gayunta, kuma ni bana ganin girmanta, ba ta fi fifty fihe ba, amma idan ta ɗaura ɗankwali kamar ƴar 30yrs. Ai da yake ni na mayar da ita tsohuwar, ganinta nake kamar ƴar 16 lokacin da na aurota, hajiya ba ta tsufa"

Wani irin haushi ya kama bilkisu, ta yinƙura za ta tashi ta bar masa wurin, ya riƙeta yana dariya ya ce "Danne kishin nan kar ki bari ya fito".

Alhaji Tahir kenan, tsohon ɗan boko, kuma babban ɗan kasuwa, da yake juya naira yadda yake so.
Mutum ne mai sauƙin kai da matuƙar son iyalinsa, mussaman ƴaƴansa, dan mutum ne mai biyewa ra'ayin yaransa, duk abun da suke so muddin bai saɓawa addini ba, zai yi musu shi, yana bawa iyalansa ƴancin yin abun da suke so, ba tare da ya takaura musu ba.

***
Rashin wayar hannu, yana daga manyan abubuwan da suka zama barazana ga ummi, a harkar karatunta, gashi ita ba kowa take raɓs ba, balle idan an bayar da assignment ko class work tayi, idan assignment ne ta gwammace ta kai yamma a makaranta, ta je Library ta yi.

Gashi farida ta tsiro da sababbun hanyoyin muzguna mata, ta hanyar ƙirƙirar mata abun da za ta sanya ta makara, wataran har ma ta rasa lectures baki ɗaya.

Daga baya ne take iya roƙon Abdul aron wayarsa, tayi assignment da ita.

Abdul ne ya gaya wa dr. Yakamata a saya wa ummi waya, saboda makaranta.

Da ya tashi dawowa ya taho mata da sabuwar waya, mai kyau da tsada, amma farida ta ƙwace ta bawa kausar, kuma ya kasa magana a kai.

Ba waya kawai ba, hatta undeas ummi na fuskantar matsala a kan su, sai dai idan ta tara ƴan kuɗi da ƙyar, idan farida ta aiketa kasuwa ta sai na gwanjo.

Daga baya Abdul ya saya mata wata ƴar ƙaramar waya, gionee take amfani da ita.

Makaranta ma da nata irin ƙalubalen, domin kuwa ƴan ajinsu, akwai yaran masu kuɗi, akwai ƴan ƙarya da yaran talakawa masu jin cewa su wasu ne.

Gani suke ummi ba tsararsu ba ce da za su yi mu'amala da ita, mussaman ganinta babu suturar kirki, kullum cikin hijjabi, hijjaban nata da guda biyu ne take zuwa da su, sai takalminta ɗaya ɗan wambai.

Banda masu zunɗen halittar ta, ko tambaya za ayi a aji, idan za a tanbayeta, sai malami ya  ce dark skin girl.

Ummi ta sanya a ranta babu wani ƙalubale, da zai sanya ta kasa haƙuri ta cimma burinta.

Yunwa da tafiyar ƙafa a kan karatun nan suka zamewa ummi jiki, ko lissafasu ba ta yi a cikin wahalar rayuwa, handout kuwa ba kowanne take iya saya ba, wataran idan har zata sayi handout, sai ta yi trecking, domin samun kuɗin sayen handout.

Ta wuni a makaranta ba cin abinci, ta koma gida ta ci uban aiki, a ƙarshe ba godiya sai zagi da muzantawa.

HOD kuwa ba ƙaramin mutunta ummi yake yi ba, saboda idan ta ganshi sai ta kai ƙasa take gaishe shi, idan ta ganshi da jaka, sai ta bishi ta karɓa.

Yana jinjinawa tarbiyyar ta, da bayar da misali da ita, dan shi rabon da yaga ɗalibi mai biyayyarta tun a zamaninsu, shima zamanin na su ba kowa ba.

Ummi ta dawo daga masallacin makaranta, tana ta sauri ta ƙarasa aji, saboda malamin da zai shiga, ko da minti ɗaya ya rigaka shiga aji, ba zaka shiga ba.

Abun da kunnuwanta suka jiyo mata wani ɗan ajinsu ya faɗa ne ya tayar mata da hankali matuƙa.

"Kai ishaƙ, ka yi sauri mu tafi kar malamin nan ya rigamu shiga, ga gorillar ajinmu can na ta sauri".

Kalmar gorilla! Ta daki ƙirjin ummi, hakan ya haifar mata da wata irin mutuwar jiki, munin nata har ya kai a kira ta da gorilla?

Zuciyarta ta din ga bugawa da sauri-sauri, tamkar zata kifa ƙasa ta shiga ajinsu tana wani irin kuka, wane irin abu ne wannan?.

Ishaq ya kalli abokinsa ya ce "Kai Nura kamar fa ta ji ka"

"Ahha haba dai?"

"Tana kusa fa ka faɗa"

Nura yayi tsaki ya ce "To sai me?".

Ishaq ya ce "A'a nura, zuciya ba ta da ƙashi, cin fuska ba shi da daɗi, tuntuni na gaya maka ka daina kamanta ta da dabba, yarinyar so silent ba ruwanta da kowa bai kamata ba wallahi"

"Ka ga kar ka isheni, jokes ne"

"Ai gaskiya ce, ba wani jokes wallahi, ko kusa yarinyar nan ba ta yi kama da abun da ka ke misalta ta ba, hidden beauty ne da ita, baƙinta da rashin gayu ke hana kyanta fitowa, amma ba ta yi kama da abun da ka ke faɗa ba".

Suka tafi aji, yana ta yi masa faɗa, suna shiga aji kuwa, kan ummi a ƙasa da alama kuka take yi.

Gaba ɗaya jikin Ishaq yayi sanyi ya ce "Ka gani ko? Kuka take wallahi".

Shigowar malamin ya sa kowa ya nemi wuri ya zauna, ya fara gabatar da abun da ya kawo shi.

Sai dai yana lectures yana ganin yadda ummi ke sharɓar hawaye.

"Ke are you ok? Meyake damunki ne?"

Ta kasa magana ta tashi tsaye tsam, ta ɗauki jakarta cikin kuka ta ce "Sir dan Allah ka bani iznin tafiya gida"

Duk da zafin malamin da rashin son wargi, amma kukan da ummi take yi, yana nuna akwai tsantsar damuwa a zuciyarta.

Kamar yadda ake son malami ya kasance cikin kulawa ya ce "Babu damuwa, amma zaki iya tafiya? Ko ki na da ƙawa ta raka ki gidan?" Ta girgiza masa kai ta ce "Zan iya tafiya"

"Kin tabbata?" Ta jinjina masa kai alamar eh.

Ya ce "To shikenan, ki tafi a hankali ki yi ta Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ta jinjina masa kai ta risuna masa ta yi masa godiya sannan ta fice ta tafi gida.

Ta daɗe ba ta yi kuka mai yawan na yau ba, tun noor tana rarrashinta, har ita ma ta fara kukan.

Ta rarrashi noor, ta aiketa kitchen, ta mayar da ƙofar ɗakin ta rufe, ranar ba irin bugun da farida ba ta yi ba, a kan ummi ta buɗe ta zo ta yi mata aiki, amma mursisi taƙi buɗewa abun za ba ta taɓa yi ba kenan. Ta san ƙarshen abun dai, zagi ne za ta sha shi da cin mutunci a wurin farida.

Tayi shiru tana tunani kala-kala a zuciyarta "Ko zan ji daɗi a rayuwata? Ko zan huta, ko kuma a haka zan cigaba da rayuwa, sanin gaibu sai Allah.
Idan ina da rabon hutawa da jin daɗi, Allah ka kawo mini su da wuri, ba dan na gajiya da karɓar jarrabawar ka ba, ni'imominka gareni sun ninka jarrabawar, Allah ka shiga lamarina" tayi maganar a bayyane cikin kuka

Sai da ta jera kwana biyu ba ta je makarantar nan ba, ranar da ta je, malamin da a period ɗin sa ta tafi gida, ya kirata ofishin HOD, suka din ga tambayar ta meyake damunta, dan malamai da yawa sun fuskanci kamar tana da social fear.

Kukan da ta kasa riƙewa a gaban su, ya tabbattar musu da tana da damuwa sosai da sosai.

Duk yadda suka matsa ta, ba ta gaya musu abubuwan da suke damunta ba, duk da tana da abubuwa da dama a ranta, da take son tattauna shi da wani, amma ta kasa samun wanda zuciyarta za ta nutsu da shi, su tattauna sosai, ko ba ayi mata maganin damuwar ba, atleast ta furta abun da yake damunta.

Suka nemi zasu zauna da mahaifinta, amma ta din ga yi musu magiya, a kan kar su yi hakan, dan a ganinta idan aka yi hakan tamkar ƙure babanta kawu yahaya ne, domin kuwa yana iya ƙoƙarin sa a kanta.

Nasiha suka din ga yi wa ummi, tare da bata ƙwarin gwiwa, a kan muhimmancin mayar da hankali a kan karatunta, da shanye ƙalubale, wanda ba ƙaramin jin daɗin nasihar ta su yi ba.

A ƙarshe HOD ya cigaba da tsokanar ta, da cewar ba ta da visa baƙar balarabiya ce ta shigo musu ƙasa.

Ɗaya malamin yake ce mata, tun da ƴar jarida ce ita, kuma an san su da neman suna, idan ta mutu yana son idonta zai saya da tsada, ta shiga kundin tarihi.

HOD ya ce "Allah ya kiyaye, wannan idon na larabawa ne a Nigeria Masha Allah, in dai wannan tarihin ne mun yafe, ko Salma"
Ummi ta sunkuyar da kai tana murmushi.

Ummi ta ji daɗin mutuntawar da malaman da take wa kallon iyaye suka yi mata, da nuna damuwarta kamar ta su, nasihohin su, sun shige ta sosai da sosai.

HOD yaje ajin su ummi, ya yi musu jirwaye mai kamar wanka, ta hanyar gugar zana a kan wulaƙanta ɗan Adam, da muhimmancin girmama ɗan Adam.

Ta samu sassauci daga jin wani abu mai nauyi da yake damun zuciyar ta.

Sai dai ta kasa manta kalmar gorilla, noor da Abdul suna falo suna kallon film ɗin king Kong, ummi har ta wuce ta dawo, ta ce "Yaya Abdul"

Ya ɗaga kai ya ce "Na'am yaya ummi"

"Dan Allah wai ina kama da gorilla?"

Wani irin banzan kallo yayi mata ya ce "Wace irin magana ce wannan?"

Cikin son ɓoye abun da ya faru ta ce "Amm, dama kawai na tambaya ne, dan na ji ana cewa ni mummuna ce"

"Kuma sai ki haɗa kanki da biri, haba ummi, ke tsakani da Allah idan aka ce ke mummuna ce sai ki yarda? Ki ƙarewa kanki kallo, a kan me zaki yadda ke mummuna ce? A halittar Allah babu mummuna, duk wanda ya ce miki mummuna ki ce ubansa ya sassaƙo kamar ki"

Noor ta ce "Maama kenan za a gayawa, itama tana cewa yaya ummi mummuna, kuma fa yaya ummi gashinta har nan, tafi fa maama gashi"

"Tashi ki bar nan wurin kan na tatsileki, baba suda" yayi maganar yana kallon noor.

Ummi kuma ta ce "To shikenan yaya Abdul, na gode sosai "

"Dan Allah kar ki kuma faɗar haka "

"Ba zan sake ba in sha Allah" sai dai a ranta tana jin har ta mutu ba zata manta da Nura ba, ya shiga cikin jerin mutanen da take yi wa wani irin kallo a zuciyarta.

Ƴan ajinsu ummi ba su tashi mamaki ba, sai da result ya fito na first semester, ummi ta ja magana, GPA ɗin ta 4, wanda kaf ajin babu mai wannan grade ɗin.

Kasancewar ɗabi'a ce ta ɗan adam, mu'amala domin cikar muradi, ya sanya suka fara lallaɓowa, domin shiga jikin ummi, amma fafur taƙi ta cigaba da rayuwar kaɗaici.

***

Gidan Idris kuwa, kamar masu zaman bariki, saboda faɗa zagi yana zagin hindu tana ramawa, tana kiran sunan uwarsa da ubansa tana zagi, idan yayi gangancin dukanta kuwa, ta dinga wawurar abubuwa tana kwaɗa masa kenan, dambe da zage-zage har ƙofar gida kamar dabbobi, maƙwabta suna raba su.
Sulhu kuwa an yi musu shi babu adadi, amma abu ya ci tura.
Sam ba ta ganinsa da mutunci, shi ma kuma haka, taje gidansu ta gaida Iyayensa kuwa ba ta wannan, saboda ta ce ba zata je gaida tsohuwar banza ba, ta ji labarin zaman da yayi da matarsa ƴar uwassa, ita ba zata lamunci cin zarafi ba.

Ya gaji da iskancinta, ya kamata yayi mata tulus da duka, ashe tana da juna biyu, ta yanke jiki ta faɗi, ƙarshe dai sai da iyayenta suka rufe Idris a police station, aka wulaƙanta shi aka kai ruwa rana kafin a sake shi, banda kuɗin magani da aka saka ya biya.

Kwana biyu da dawowar sa daga hannun ƴan sanda, ya je ya samu hashim a kan ya bashi shawara, so yake a lallaɓa kawu yahaya da ummi, a dawo da auren su.

Hashim ya ce "Haba Idris, lokacin da na din ga ankarar da kai ai kasa ganewa kayi, ummi tafi ƙarfin ka yanzu, wace irin azaba ce ba ka yi mata ba, tun tana ƙaramar yarinya. Yanzu ta sauke Alqur'ani har sau biyu, ta shiga jami'a tana karatu, ka ce ta dawo, to tayi maka me? Kai da ko kwalin sakandare baka da shi".

Idris ya waro ido ya ce "Ummin ce a jami'a, kai waye ya gaya maka?".

Hashim ya ce "Muna waya da ita, bautar ƙasa nake son na gama, idan Allah ya sa na samu aiki, zan nemi auren ummi".

Idiris yayi masa wani mugun kallo ya ce "Amma dai ka ci kai, matar da na saki zaka aura? Bazawara ce fa kai kuma baka taɓa aure ba. Haryanzu bana son ummi, ban taɓa jin ƙaunarta a raina ba, amma ina da muradi a kanta, idan har ba ta dawo mini ba, idan ina raye baka isa ka aureta ba".

Hashim ya yi murmushi ya ce "Zamu gani ai" Idris ya tashi fuuuu ya tafi.

Idris yayi shiru yana tunani, tun da mahaifinsu ya takura masa da maganar aure, ya gaya masa ga ƙudurinsa, Iya ta ce bai isa ba, ba zai auri bazawar da ƙaninsa ya saki ba, kuma ta riga ta cire ummi daga jikokinta tun da ta ƙi yarda a rufawa Idiris asiri!.

Babansa kuma ya ce Idan ya sake ɗaga maganar nan, zai yi masa abun da bai taɓa tsammani ba.

Duk son ummi da islamiyya, haka ta haƙura, saboda yanayin makaranta, ta samu wata makarantar, a nan unguwarsu, take zuwa asabar da lahadi ɗaukar karatu.

Sai dai ganin ummi tana da ilimin addini dai-dai gwargwado, idan aka yi mata ƙarin nata karatun, sai a haɗata da aji tayi musu ƙarin Alqur'ani da wasu litatafan.

Duk da ayyuka sun ƙara yi mata yawa, hakan yayi mata, saboda tana zama busy sosai, tana hana zuciyarta tunane-tunane da sukan jefata cikin damuwa.

Ga bikin Intee ya matso kusa, sai gori take sha a gidan nan, wai ta zama guzuma, babu mashinshini a haka za ta dauwwama wanke-wanke da shara.

Kawu yahaya yayi rawar gani, ya yi wa inteesar kaya na kece raini, ya so ace ta fara makaranta kan yayi mata aure, amma ta dage soyayya ta rufe mata ido, ta ce ita fa aure take so, dan haka ba yadda ya iya ya ƙyale ta.

Sagir ya danƙaro mata uban kayan lefe, kaya ba na wasa ba, ya ciko akwatuna da kaya, sai iyayi take tana rawar kai.

Albarkacin auren inteesar, a wannan karon da kawu yahaya ya yi mata ɗinki, farida ba ta ƙwace ba, har da sabon takalmi, farida kuma ta bata tsohon mayafi, kalar kayan.

Ranar party, farida ta ce ta zauna a gida, ta kula da baƙi masu shige da fice, kuma ta tsaya a kan girke-girken da za ayi.

Ummi ta zage ana can ana party, tana gida suna aikin girki, dan ita ta jagoranci aikin abincin bikin.

Ranar wuni ya kama ranar da za'ayi ɗaurin aure, dan haka da wuri motoci suka kawo ƴan gagarawa.
Su Idris da babarsa, su magaji kafatanin ahalin Iya.

Lokacin ummi ba ta gidan, suna can tana ta hidima da ƙawayen inteesar, ana yi wa inteesar kwalliya.

Ummi ta yi wanka, ta yi wa noor, ta saka kayan ankonta da ita da noor.

Sai da inteesar ta kalli ummi ganinta babu mayafi, dan zata iya ƙirga rabonta da ta ga ummi babu hijjabi.

Tayi ture ka ga tsiya, ta kanannaɗe gashinta a ƙeyarta, ɗaurin ya zauna cas a kanta, ga ɗinkin ma dai-dai jikinta.

Ta shafa man leɓe, ta yafa mayafinta a kanta, ta rufe jikinta sosai, ta kama hannun noor, suka fice.

Wani irin farinciki ya kama ummi, ganin ƴan gida gaba ɗaya sun zo, dan rabonta da su tun da ta baro gagarawa.

Duk bin ummi suka yi da kallo, yadda ta girma ta zama budurwa.

Cikin su ummi ta shiga tana gaishe su, Iya sai wani hura hanci take yi.

Ta ce "Ina yaya magaji?"

Sa'adatu ta ce "Sun tafi wurin ɗaurin aure".

Ummi ta karrama su da abinci, dan matar gidan ba ta ta su take yi ba, ta kai su ɗakinta, ta yi ta ɗawainiya da su.
Bayan azahar su Hashim suka dawo daga wurin ɗaurin aure, ummi baki yaƙi rufuwa saboda duk ƴan uwan mahaifinta sun zo.
Ɗaya bayan ɗaya ta din ga gaishe su, suna mamakin yadda ta girma, ta zama cikakkiyar mace, sai dai ko kusa bata kalli in da Idris yake ba.

Farida sai bin ummi take yi da kallo, dan ba ta taɓa tsayawa ta kalli ummi sosai cikakken kallo ba sai yau, rashin gyara ne ke ƙara munanta ummi, idan ka kalleta sau ɗaya sai ka sake kallonta, mussaman yadda take kokowa da mayafin, kasancewar ita ba ma'abociyar ta'amalli da shi ba ne ba.

kasancewar hashim shi ne mutumin ummi, can harabar gidan suka koma, suna ta hira.

Ya dubeta ya ce "Ummi, kawu yayi miki magana kuwa a kan batun nemo mamanki?"

Cikin sauri ta ce "A'a, ya ake ciki?"

"Subhanallah, ya ce dai kar na kuskura na gaya miki saboda wani dalilinsa, amma dai idan bai ganta ba yana daf".

"Ya salam, bai gaya mini ba, ko maganar zan yi masa?"

"A'a, dan ya yi mini kashedin kar na gaya miki, ki kwantar da hankalinki duk
End Ads