x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 29 - CUTARWA

  • 84001 words
  • 87000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 522

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
ciki, dan taga kamar ya ɗau maganar noor serious.
Gaba ɗaya ma dariya ta bashi, dan haka ya shareta ta cigaba da banbaminta

***
Haka nan ummi ta ɗan damu, kwana biyu shiru ba Raihan babu labarin sa, ya daina nemanta a wayar ma, kamar za ta damu, kuma ta basar ta manta, ta cigaba da sabgoginta.

"Hi dear" taga message ta what's app ɗin ta, what's app ɗin da ta fi ƙarfin sati uku ba ta buɗe shi ba saboda rashin data, sai yau da ta samu ta saka ɗari biyu.

Baƙuwar lamba ce, ba ta san waye ba, dan haka tayi replying da Assalamu alaikum.

Ta tsaya ta ƙurawa message ɗin ido, hi dear, dear kalma ce da ake iya gaya wa kowa, amma mussman wanda yake da muhimmanci.
To ita akwai wani wanda take da muhimmanci a gare shi, da har zai ce dear.

Tayi guntun tsaki da ta tuna, akwai mutanen banza a what's app, wanda ba su sanka ba, amma su yi maka maganar banza.

Ta cigaba da shirinta na tafiya wurin aiki, ba ta taso ba sai ƙarfe huɗu da rabi, a hankali take tafiya, sai dai wata mota ta cika mata kunne da horn. Ta matsa gefe amma ya cigaba da yi mata horn.
Gefe ta koma ta bar wa motar hanyar, ta cigaba da tafiyarta.

"A wannan yangar da iyayin naki, sai kin fusata mutum ya ture ki" cak ta tsaya, ta waiwayo da mamaki ta ce "Laa raihan, yi haƙuri ban san kai ne ba".

"Eh shi ne ki ka bar mini hanyar, wato na ci kaina, ban isheki kallo ba"

Ummi ta ce "Eyya ba haka bane ba, ban san kai bane" tayi maganar tana kallon sa, idonsa yayi ja, kamar daga wani wurin yake.

"Wucewa na zo yi, na san sai yamma ki ke tashi, na tsaya ki fito mu tafi".

Ɗan shiru ta yi tana kallon sa, ba ta son shiga motar nan tasa, kar a fara zargin wani abu.

Ya ɗan marairaice ya ce "Nayi awa a wurin nan ina jiranki, dan Allah kar ki ce a'a".

Ta ce "To" tabi bayansa, suka nufi motarsa.

Suna tafe a hanya, har lumshe ido take yi, saboda gajiya.

"Yaya ummi kwana biyu ko ki neme ni, anya za ayi zumuncin nan da ni kuwa? Na yi busy sosai kwana biyun nan, ko waya bamu yi ba, kuma baki nemi in da ƙanin naki yake ba".

"Yi haƙuri ba haka bane ba, zan din ga kiranka in sha Allah".

"Allah ya sa, ya karatu ya ɗalibai?"

Ta amsa da"lafiya ƙalau Alhamdilillah"

"Masha Allah, nima kwana biyu Alhaji ne ya sakani aiki, ya ga ina sararawa bana aikin komai, ina ga gani yayi sharholiya ta yi mini yawa, ya sani aiki ko cikakken lokaci bani da shi, duk na rame na zama baƙi"

Ummi ta ɗan yi murmushin yaƙe, cikin fargabar abun da ka iya biyo bayan maganar sa, wataƙila cin zarafin kalar fatarta.

Bai damu ba ya cigaba da maganar sa, "Ni fa yunwa ma nake ji, ko mu tsaya mu ci abinci?"

Tayi farat ta ce "A'a, na ƙoshi ma ai, a ƙoshe nake ai"

"Yaya ummi kenan, da abinci ki ke zuwa kenan? Tun safe fa kina wurin nan, to idan kin zo da abincin ki din ga ci kina rage mini, dan ni yau tun da aka kirsheni a wuri ɗaya tun ina ganewa har na daina, bari na yo takeaway a wannan wurin abincin". Ta ce "To".

Ta kai mintuna sha biyar a motar, sannan ya dawo da manyan ledoji, ya tarar ta sauke facemask ɗin ta.

"Sannu na bar ki kina jira ko? Tuwo na so in samu, babu sai shinkafa ni kuma damuna take yi"

Tayi murmushi ta ce "Kana cin tuwo kenan? Abdul ɗin gidanmu baya son tuwo"

"Haba dai, ai yaya tuwo abun so ne, ni a bauchi na saba, Alhajin Bauchi da shi yake karyawa, ga kwanonsa ga nawa, amma shima fa tuwon bana jera kwanaki ina ci yake isata"

Tayi dariya ta ce "Ka fi son dai a din ga ccacanzawa"

"Yauwwa, ba kullum abu ɗaya ba"

Yau dai yayi sa'a, ta ɗan saki jiki kaɗan, dan yau har da dariya.

Ya ƙarewa hijjabinta kallo, duk yayi fari takalmin ƙafarta ma ya tsufa.

"Ummi"

Ta ce "Na'am"

"Me ya fi burgeki a rayuwa? Wanda yin sa yake yi miki daɗi, ko samunsa, abun da dai yake saka ki farinciki?"

Tayi shiru tana tunani, oho, ita akwai wani abu da take jiran samuwar sa ya sanyata farinciki ne? Duk abun da ya zo mata a rayuwa kawai, karɓa take yi.

"Babu"

"Ban gane babu ba? Kawai haka ki ke rayuwa ba farinciki?"

Ta sunkuyar da kai ta yi shiru.

"No dole akwai, ki tuna sai ki gaya mini"

"Babu" ta sake bashi amsa.

Bai sake ce mata komai ba suka cigaba da tafiya, in da ya ajiyeta wancan karon, ta sake cewa ya ajiyeta.

Ya yi parking sannan ya kalleta ya ce "A nan zaki sauke, ba zaki bari na ga gidan ba?" Ta hau wasa da yatsun hannunta bata ta kula shi ba.

"Bayan ƴan uwa let's be true friends ummi, ki tuna abun da yake saki farinciki ki gaya mini, mu zama ƴan uwa kuma abokai saboda Allah"

"To in sha Allah"

Yayi murmushi ya ɗauki leda ɗaya, ya ce "Ungo naki" ta kalleshi zata yi magana, ya ɗora yatsansa a kan laɓɓansa ya ce "Shhh".

"Idan zan wuce gobe in Allah ya kaimu zan jira ki mu tafi tare" ta jinjina kai, ta fice daga motar.

Addu'a take yi, tana fatan Allah ya sa kar wani ya ganta, cikin ikon Allah babu wanda ya ganta, har security gidan yana banɗaki, ta wuce ta shiga har ɗakinta ba ta haɗu da kowa ba.

Ta sauya kaya ta fito, ta dudduba gidan babu kowa, ta koma ɗakin ta duba ledar da Raihan ya bata.

Rabin kaza ce guda a cikin ƙatuwar roba, sai shinkafa da salad.

Jikin ummi har rawa yake, duk wannan kazar ita kaɗai?.

Sai kuma ta yi shiru tana tunani, anya ba ta zura jiki ba? Kasa ci tayi ta tashi ta shiga aikin gida.

Abdul ne ya shigo yana waya, ya kammala ya tsaya yana mita.

Ummi ta ce "Yaya Abdul kana nan dama?"

"A'a yanzu na shigo, wani ɗan rainin hankali ne ya kirani, wai babansu ne ya buɗe shago a tal'udu, suna neman casheir, wanda zai din ga zauna musu da safe zuwa azahar, ko azahar zuwa magariba".

Ummi ta ce "Dan Allah yaya Abdul zan yi, ina so"

Ya kalleta ya ce "Zaman jiran shagon, shagon furnitures ne fa da kayan kitchen"

"Eh yaya Abdul dan Allah, dama na gama SIWES, kawai dai sun buƙaci na cigaba da zuwa ne, dan Allah zan yi"

Abdul ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Zan yi magana da Abba, idan ya yarda shikenan".

"Yauwwa zai yadda ma in sha Allah" tayi maganar tana addu'ar Allah ya sa Abba ya amince, ita ko kuɗin babu yawa tana so, atleast ta din ga samun na sayen wasu abubuwan da take buƙata.

Ta kasa zaune ta kasa tsaye da kazar nan a ɗaki, dr. Gidansa ba ya rabo da nama da kaji, amma tsaf ummi za ta yi aikinsu, farida ta karɓe idan ta ga dama ta sanmata idan ba ta ga dama ba, sai ummi ta zo wanke-wanke ta ɗan tsinci sauran hanta, da diddiga ta lasa abun ka da zuciya.

Hankalinta bai kwanta ba, sai da ta saka noor a gaba, ta gaya mata yadda aka yi, kamar sa'arta.

Noor ta din ga murna ta ce "Yaya ummi kar ki gaya wa kowa mu cinye abunmu".

Ummi da noor suka cinye takeaway tare, suna ta murna, dan kuwa ummi ba ta taɓa cin kaza mai yawan haka ba.

Masu nema daga farko dan Allah ku duba a watpad
Ayshercool
08081012143

    *CUTARWA!*

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

P23

FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya

Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.

And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ayshercool.

PAID ADVERT!.

Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku

Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi 
Man garan gashi 
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702   08025453921

*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*

BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.

23


Murmushi ummi ta yi ta sauke wayar, tana sake gazgata maryam da take yawan faɗar Raihan rigiamamme ne.

A ɓangaren sa shima ajiye wayar yayi yana murmushi. 

Ya sauka daga kan gadon sa, ya shiga banɗaki ya yi wanka yayi brush, ya sanya kayansa ya fita.

Sashin mami ya nufa, duk ba su tashi ba, ya duba kan dining an ajiye masa kayan breakfast da masu aiki suka girka.

Ya buɗe foodflask, ya tarar da doya ce da ƙwai, sai kayan tea, doyar ta ja mai sosai da sosai.
Yayi guntun tsaki, ya fice ya nufi sashin Hajiya, sai dai kai tsaye ɓangaren mahaifinsu ya wuce.

Yana zaune yana shan tea, gefen sa ƙaton tray ne, ɗauke da kayan marmari yana kallon labarai.

Ya ɗaga kai ya kalli raihan ya ce "Dama kana gidan nan?"

Raihan ya ƙarasa kusa da shi ya risuna ya ce "Barka da safiya"

"Yauuwa barka babban mutum, ka tashi lafiya?"

Alhamdilillah, ya amsa yana zama a kusa da Alhajin.

Ya ce "Alhajin Allah kana sararawa, ka bar mu a nan ka je ka huta ka dawo, ka ƙara fresh sosai"

Sanin halin raihan, na zolaya ya sanya shi yin murmushi ya ce "Ina wani hutu Raihan? Ina can ma aiki nake yi, haryanzu ban huta ba, zuwa yanzu yakamata ace ku kuke kula da komai, amma sai dai nayi da kaina, yayyenka sun fi mayar da hankali a kan shashashanci".

Cikin kulawa raihan ya ce "Ka yi haƙuri, ka daina damun kanka, kai ka ce ƙuruciya ce take damunsu, za su daina".

"Zuwa yaushe kenan? Idan ƙuruciya ce kai meyasa ba ka yi?"

Raihan ya ce "Haka ne, amma dai kayi haƙuri ka kwantar da hankalinka, abun da su Yaya Salim suke yi, ka ɗauka jarabta ce daga Allah.
Kalli shekarunka sun ja, ba hawan jini, ba ciwon suga, ga mu Allah ya baka, ga tarin dukiya da al'umma suke amfana ga Hajiya ga mami dukkan mu naka ne, idan ka duba wannan ni'imomin sai ka ga abun da suke yi bakomai bane ba, dan Allah kar ka saka damuwa a ranka wani ciwon ya kama mana kai".

Kallon Raihan yake yi, cikin tsananin soyayya da kulawa, ya tsiyayo tea cup, ya bawa raihan sannan ya ce "Madalla da yaron kirki, nasiharka na ratsa mini zuciya, in sha Allah zan cigaba da yi musu Addu'a"

Raihan ya ce "Yauwwa father like no other, we are proud of you, ka cigaba da yi musu addu'a in sha Allah zai zama labari"

Alhaji Tahir ya ce "Mahaifiyarka na ganin kamar laifin Hajiya ne ya sanya su lalacewa, amma kamar hajiya na iya ƙoƙarin ta a kan tarbiyya".

"Haba Alhaji, kar ka ɗorawa kowa laifi, Hajiya ba ta da sakaci ko kaɗan".

"Haka ne, ina son na roƙeka wata alfarma ne".

Raihan ya gyara zamansa ya ce "To Alhaji, Allah ya bani ikon yi".

Ya ce "Yauwwa, lissafin da muke yi na shekara shekara da manager, da kai nake so ku yi, a fitar da zakka, a fitar da wanda za a biyawa umara, harajinmu na nan gida da sauran ƙasashe, da duk wasu gyare-gyare da zamu yi, idan ku ka gama sai ka kawo mini na duba"

Raihan ya ɗan yi shiru yana nazari, "Ya dai na ji ka yi shiru?"

Raihan ya ɗago ya ce "Babu damuwa in sha Allah za ayi, zan je na same shi".

Alhaji Tahir yayi murmushi ya ce Yauwwa "Babban mutum, ka ga atleast na sake na huta sosai da sosai"

Raihan yayi murmushi yana cigaba da zuƙar shayi, nauyi ne mai girman gaske Alhajin ya haɗa shi da shi, dan aiki ne ba ƙarami ba.

Ya shanye shayin, ya miƙe tsaye ya ce "Bari na ƙarasa wurin Hajiya mu gaisa"

"To shikenan babu laifi"

A sanyaye Raihan ya tashi ya nufi sashin hajiya, ba zai iya cewa mahaifinsu a'a ba ne ba, amma wannan aikin kamar yayi masa yawa, ba zai iya jajircewa ya yi shi, kamar yadda shi Alhajin zai yi ba.

"Babban mutum ya dai, na ga kana tafiya a hankali, ko yunwa ka ke ji ne?"

Ya zauna yana faɗin "Eh, ina ɗan jin yunwa ma, me ku ka yi?".

"Ka san halinsu, kowa dafe-dafensa yayi, ni kuma tuwo na saka a ɗumama mini na sha da tea"

"To ni ma zan ci tuwon"

Ta ce "To bari a kawo, har da man shanu kuwa da yajin daddawa, mai ɗan karen daɗi"

Yayi murmushi ya ce "Hajiya kenan, ina su Yaya Sagir?"

Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Ba su tashi ba".

Ya jinjina kai sannan ya ce "Yauwwa Hajiya, kin tuna yarinyar nan ummi? Ƙawar maryam?"

Ta ce "Eh, ya aka yi?".

"Yauwwa Alhamdilillah, dan Allah me ki ka sani a kanta?"

Hajiya ta ɗan yi shiru tana nazarin sa, sannan ta ce "Meyafaru da ita? Me ka ke son sani a kanta?".

"Ba wani abu bane ba, mami ta fara faɗa mini abubuwa a kan ta, so ina son sanin if their is way, we can help her, like she's not socially ok"

"To ai kaga ƙawar maryam ce, ni kuma ba wani son shiga harkata suke yi ba, amma dai ina ganinsu tare da maryam, yarinya ce mai matuƙar haƙuri da biyayya, kamar babanta ne ko babarta ce ɗaya daga ciki ya rasu, yayan babanta yake riƙonta, matarsa take maltreating ɗin ta, gaskiya i don't know much about her. Na so ace a cikin yaran nan akwai nutsatstse, ai da na haɗa su aure, tarbiyyar ta na burge ni sosai da sosai"

"Kin san meya ja hankalina, har na tambayeki?"

"A'a sai ka faɗa".

"Yadda maryam take yawan bani labarinta, da irin abubuwan da suka din ga yi mata na wulaƙanci suna makaranta, gidansu an yi maltreating ɗin ta, makaranta yara sun yi maltreating ɗin ta, wai wasu lokutan har da malamai, abun bai yi mini daɗi ba wallahi Hajiya"

Hajiya ta ce "Shiyasa nake yinka babban mutum, akwai hangen nesa da zurfafa tunani".

Cikin damuwa ya ce "Hajiya, kowace halitta da Allah yayi, tana da muhimmanci da kuma amfani, sosai nake jin zafi idan na tuna abun da maryam ke faɗa a kan ta, gaba ɗaya yanayin ta kamar a tsorace take da mutane ma, kuma ni banga muninta ba, baƙa ce kawai, meye abun aibata mutum a kan abun da baka da ikon yin sa?"

"Babu kam"

"Amma Hajiya kina ganin zan iya taimaka mata?"

"Me zai hana? Idan har da ɓangaren da zaka iya supporting ɗin ta, go ahead nima zan yi farinciki da hakan"

Raihan ya sake gyara zaman sa ya ce "Wallahi na so maganarki ta farko ta tabbata, ina ma akwai nutsatstse a cikin su yaya salim, da ɗaya daga cikin su, ko shi ko yaya sagir da wani ya aureta"

Cikin damuwa ta ce "To ya zan yi, sun ƙi karatu, sun ƙi kasuwa sai shirme, sai addu'a kawai"

"Kar ki damu Hajiyarmu, lokaci ne, zasu daina ne in sha Allah, ayi tayi mana Addu'a"

Hajiya ta ɗora hannunta kan na Raihan ta ce "Addu'a kullum cikin yi muku ita ake ai, ubangiji Allah ya tsare mana ku"

Ya amsa da Amin.

Sai da ya ci ya cika cikinsa, sannan ya tashi ya fita.

Har ummi ta koma gida, Raihan bai sake nemanta ba, tayi ta duba wayar amma bai kira ba.

Dr. Yan gari, yana ta ƙoƙari a kan kausar ta samu admission ita ma, domin kuwa a wannan karon, Farida ta ce ba zata sake aurar da ƴa ba, sai ta fara makaranta, saboda kar a sake kwata irin yadda aka yi a kan inteesar.

Suna falo suna kallo, dr. Ya ce lallai ummi ta fito falon ita ma, dan baya son duk suna tare a falo, amma ta din ga ware kanta ita kaɗai a ɗaki.

Ummi dai ta zo gefen kujeru ta zauna a ƙasa, tana kallon, wanda a son ranta tafi son zaman kaɗaicin a ɗakinta.

Noor ta hana su yin kallon, sai tsalle take a tsakar falon, tana karanta ayar Allahu nooro samawati wal ardi.

Abdul ya ce "Noor, dan girman Allah ki zauna wuri ɗaya ki yi karatun nan a nutse".

Sai ta koma hawa kan kujera tana dirowa.

"Ke dan ubanki ki nutsu" Kausar tayi mata tsawa.

Noor ta ce "Babanmu ɗaya"

Dr. Ya ce "Lafiya ce wannan tsalle-tsallen da take yi.

Farida ta ce "Duk ta bi ta ishi mutane da karaɗin tsiya".

Noor ta koma kusa da dr. Ta zauna ta ce "Dr."

Ya ce "Na'am shalelena, yau kuma a dr. Na nake"

"Ka san me? Wata a ajinmu, babansu ya auro kishiya, yanzu mamanta biyu kenan".

Yayi dariya ya ce "Masha Allah, to Allah ya sanya alkhairi ya basu zaman lafiya".

Ta gyara zama ta ce "To Abba ni bani da wata maman sai maama, ita kuma ba ta so na"

"Tana sonki mana".

"Abba dan Allah muma ka auro mana kishiya, nima mamana ta zama guda biyu"

Ashar ɗin da farida ta yi mata sai da duk suka razana, ta zaburo zata make noor, amma noor ta tashi da gudu, tana murguɗa kwankwasonta tana dariya, ta tsaya daga can ƙarshen falon ta ce "Wallahi Maama idan ki ka kuma dukana, sai na ce Allah ya sa Abba ya auro kishiya"

Farida ta dafe kai ta ce "Na shiga uku da wannan yarinyar, anya
End Ads