x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 23 - CUTARWA

  • 66001 words
  • 69000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 501

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
zunduma over size hijjab fisabilillahi. Ranar da babu school, ki zo gidanmu akwai wata mai mayukan gyaran jiki, muje ta haɗa miki mai sai na biya"

Ummi shiru tayi tana ƙoƙarin haɗiye wani abu mai ɗacin gaske, da yake yi mata kai komo tsakanin maƙogwaronta da ƙirjinta, wannan shawara maryam take bata ko ci mata fuska.

"Ina magana kin yi mini shiru" Maryam ta yi maganar a ɗan hasale, dan daga abun da maryam ta tsana a halin ummi bai wuce miskilanci da shariya ba.
Wanda ba wai miskilancin bane kawai, tana gudun shiga harkar mutane, kar tayi wani abun da za aci mata mutunci.

Ummi ta ɗago ta kalli maryam, hawaye har ya zagaye cikin fararen idanuwanta, ta ɗan juya brown ɗin ƙwayar idonta ta ce "Maryam, I won't bleach my skin, ko a so ni a haka, ko a ƙyale ni, banbancin fari da baƙi a wurin Allah, wanda yafi tsoronsa mu ƴan adam mune muke ɗorawa kanmu".

Cikin ƙuluwa maryam ta ce "Au dan na baki shawara ina nema miki mafita, shine ki ke kuka, har ki ke nema ki kafirta ni? To ki ƙarata ummi, amma zaki ce na gaya miki, wallahi babu wanda zai aureki da wannan baƙin da gidadancin"

Ummi tayi murmushi mai ciwo hawayen na zubowa ta ce "Ba ke ki ka fara faɗar haka ba maryam, an daɗe da gaya mini ba zan auru ba ni mummuna ce, dan haka ban sa aure a ka ba dama, nima na san maza farare suke so masu kyau, in dai ubangijina yana sona shikenan maryam" tayi maganar cikin sanyin halinta.

Sai kuma jikin maryam yayi sanyi, ta ce "Am sorry please, ba ina nufin na ɓata miki rai ba ummi, mafita nake nema miki"

Kawai ummi ta tashi ta bar ajin, domin kuwa an kaɗa ƙararrawar tashi.

Kai tsaye gida ta nufa, tana tafe tana hawaye ta cikin niƙabinta.

***
Babban mutum ne zaune mai cike da nutsuwa da kamala,kallo ɗaya zaka yi masa ka san a cikin hutu yake, falon da yake zaune kawai ya ƙawatu dai-dai gwargwado.
A hankali yake zuƙar tea ɗin da yake hannunsa, yana kallon ƙatuwar plasma tv da ke manne a jikin bango, sai dai kana gani ka san ba kallon yake yi ba, zancen zuci yake yi.

"Alhaji ya dai?"

Wata mata tayi maganar tana ƙoƙarin zama a kusa da shi.

"Bakomai" yayi maganar yana murmushi.

"A'a da komai mana, zancen zuci ka ke yi, shekaru sun ja, yakamata a din ga rangwatawa kai, kar wani ciwon ya kama ka"

Ya ajiye cup ɗin hannunsa ya ce "Da ciwo zai shigeni saboda tunani, da tuni ya shige ni hajiya. Lokaci yayi da yakamata na huta, huta nake buƙata amma ki duba ki ga haryanzu ban huta ba, ni nake fama da harkar kasuwancina, gaba ɗaya yaran nan basu saka komai a gaba sai shashasha. Na tara dukiya, suna ta bushashasha, gaba ɗaya babu hankali ko nutsuwa a cikinsu da zai tallafe ni yanzu, su karɓi ragamar kasuwancin ni na huta.

Ko kartun kirki babu wanda ya tsaya ya kammala a cikinsu, duk da tarin kuɗin da na kashe musu da sun yi karatu, amma kalli duk shashanci suke yi, suna manya amma duk babu mai saiti a cikin su.

Matan ne kawai nutsatsu a cikin su, su kuma duk matan wasu ne, ragamar babban kasuwanci irin wannan ma ai ba na mace bane ba.

Jiki a sanyaye ta ce "Na sani Alhaji, ka yi haƙuri, ka ɗan ƙara musu lokaci, mu cigaba da addu'a, kuma a cigaba da jan su cikin harkar kasuwancin"

"Eh su ƙarasa ni ba. Wane lokaci zan ƙara musu? Salim na da shekara talatin da ku san biyar, dukkansu babu yaro a cikinsu, wane lokaci zan basu banda wanda na basu a baya. Zan yanke hukuncin da nake ganin ya dace kawai".

Ta ɗan gyara zamanta ta dube shi ta ce "Wane hukuncin kenan?"

"Zaki gani idan na yanke" yayi maganar yana sauya channel da remote.

***
Ummi kuwa tsaye take a gaban mudubin ɗakinta, tana ɗaure da zani kasancewar daga wanka ta fito, ta shiga ƙare wa kanta kallo a jikin madubin.
Ta saki gashin nan a bayanta, ta din ga kallon ƙwayar idonta, da take brown sosai, cikin idon kuma fari ƙal, ta gangaro kan fatarta da take jiƙe da ruwa, baƙa mai ɗaukar ido.
Ta kalli gashin ta, ta ɗan shafa shi a hankali, tana tambayar kanta wace irin halitta ce ita haka. Ita kanta ta san ba ta taɓa ganin mai irin halittarta ba, a ƙasar hausa duk wanda take haɗuwa da su, ba ta taɓa ganin mai irin gashin kanta da kuma ƙwayar idonta ba.

A hankali ta murza fatar jikinta, tana tuna maganganun su kausar masu sosa rai, wai wankan baƙi asarar ruwa. Baƙar mace bolar maza, irinta kuma bolar da ko recycling ba za a iya yi ba.

"Da gaske ba zan yi aure ba, saboda maza ba sa son baƙar mace mai duhu kamar ni? To haka zan cigaba da zama a gidan kamar baiwa? Ko kuma zasu mayar da ni ƙauye daga baya, saboda ban samu miji ba? Dama Iya ta ce babu wanda zai aureni, saboda munina. Idan ma na yi aure zai iya ƙara aure ya daina kula ni, saboda ni bani da kyau, to wa ma zai ce yana so na?.

Ko dai maryam da gaske take hijjabin da nake sakawa, da kuma munina ba zai bari a aureni ba?"

Ta dubi ƙirjinta, da tudunsu ya ɗaga sosai.

Ta girgiza kai ta ce "Ni ba zan iya bari a ga jikina ba, kuma ba zan saɓawa Allah ba, idan na yi bleaching na raina halittar da yayi mini kenan. Ya bani lafiya bani da wani mummunan ciwo da yake hanani sukuni, sai jarrabawar rayuwa da tsananinta bai sanya na rabu da rai na ba"

Istigfari ta hau yi, duk hawayen idonta ya kasa daina zuba.

"Yaya ummi" ta jiyo muryar noor.

Tayi saurin share hawayenta ta ce "Na'am ƴar gidan anty ummi"

"Ki ɗora ni a kan mudubin na taɓa gashinki"

Ummi ta yi murmushi, ta ɗora noor a kan mudubinta, noor ta saka hannu biyu ta kama gashin tana dariya.

Can sai ta ƙurawa ummi ido, ta ce "Kuka ki ke yi?"

Ummi ta girgiza kai ta ce "A'a mama".

Noor ta kai hannunta ta shafo sauran hawayen ta ce "Kuka ki ke yi, maama ce ta dake ki? Ko su anty intee ne?"

Ummi ta ce "A'a mura nake yi ne, zauna a kan katifata na saka kaya" tayi maganar tana ajiye noor a kan katifar.

Noor ta din ga tsalle a kan katifar tana waƙe-waƙenta na yarinta.

***
Iya da idris fa sun haɗu da wanda suka fi su tashanci, dan mussaman uwar hindu ta din ga tatsarsu kuɗi, wai hindu ba ta da lafiya, za a saya mata magani, yadda ake kula da kowacce mace mai ciki, dole a kula da Hindu, tun da da bai yi abun da yayi ba, da hindu ba ta samu ciki ba.
Dama akuyancin sa ne ya hana su bashi hindu, dan haka tun da ya hilaceta ya ɓata ta dole ya kula da ita, saboda sun san ƴar su ba lalatacciya ba ce ba a baya.
Yadda baban hindu yayi alƙawari, sai da ta haihu, ta haifi santaleleliyar jaririya, cibiya kawai aka yanke, aka naɗo jaririyar a zani, har da mahaifarta suka kai suka direwa Iya a tsakar ɗakinta, sai tsala ihu take yarinyar.

Mutane kuma suka taru a gidan, ƙarshen tonon asirin dai da asiri ya tonu, domin kuwa rana tsaka ƙanwar babar hindu suka zo suka kawo jaririyar, sannan suka sanar da iya cewa, sun saka yara sun kama wani ƙaton rago da iya ke kiwo a waje, an kai shi can gidan za a yankawa mai jego bayan kwana bakwai na ƙauri an sakawa jaririya sunan Iya wato Hajara.


Ayshercool
08081012143.
    *CUTARWA!*

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

P19

FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya

Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.

And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ayshercool.

PAID ADVERT!.

Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku

Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi 
Man garan gashi 
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702   08025453921

*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*

BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.

P19

Tun da Iya take, ba ta taɓa cin karo da tashin hankali irin na yau ba, gida ya cika da mutane, ana ta salallami, yayin da Idris ya kulle kansa a ɗaki ya kasa fitowa saboda kunya.

Tabbas da yana da kuɗi babu abun da zai hana shi guduwa, kodayake yayan Hindu yayi masa kashedin muddin ya gudu sai ya ɗaure babansa.

Yarinya ta din ga tsanyara ihu, a tsakiyar ɗakin Iya.

Su kuma suka wanda suka kawota suka gama tijararsu da rashin mutunci, suka fice suka bar gidan.

Iya ta ce a ɗauki ƴar a kai wa babar Idris, dan ita ba ta san ya za ta yi da jaririya ɗanyen goyo haka ba, ita ko nonon ma yanzu babu sun suɗe sai fata, dan haka sai dai uwarsa.

Babar Idiris kuwa ta ce "Iya ke yakamata ki riƙe wannan ƴa ba ni ba, tun da dama sunanki suka sawa yarinyar, ba yadda ban yi ba na bawa yarona tarbiyar da ta dace, amma ki ka ƙi saboda yana da sunan mahaifinki, kin ɗau son duniya kin ɗora masa. Ko laifi yayi na yi masa faɗa, sai ki ci mini mutunci.
Dan haka Iya ke zaki kashe wannan wutar, wallahi ki ka bani jaririya ban san yadda zan yi da ita ba".

Cikin fusata Iya ta ce "Ni ki ke gayasa haka lami?"

"Iya ba rashin kunya ba ce gaskiya ce, da kin bari na bawa ɗa na tarbiyya da haka ba ta faru ba".

"Rufe mini baki, har wata tarbiyya ce da ke da zaki bawa wani? Ke ɗin a yaya ki ke? Ki zo ki ɗauke yarinyar nan ki san yadda zaki yi da ita"

Lami ta ce "Ban gane ba iya, ni na yi mata cikin, wallahi ba zan ɗauka ba"

"Lami uwata ce take faɗa kina faɗa?"

Lami ta ce "Maganar gaskiya ce fa, in ɗauki ƴa in yi yaya da ita? Ta in da aka hau ta nan za a sauka ai"

Iya ta ce "Rabu da ita, na san maganinta, yanzu abun da ya fi dacewa shi ne ka je, ka ce musu mun amince a ɗaura auren nan su karɓi ƴar nan. Amma wallahi Idiris ya cuce mu, ya janyo mana masifa da abun kunya, ga ragona da nake son sayarwa lokacin sallar layya, sun tafi da shi, ku san yadda zaku yi ku karɓo mini ragona".

Ilyasu ya ce "Iya yanzu waye yake ta rago, muntuncinmu ya gama zubewa"

Baban su Idris ya ce "Ina ga kawai mu je mu samu iyayen nata, ina sa'adatu ta zo ta yi wa yarinyar wanka, a saka mata sutura, mu je gidan su Hindun"

Sa'adatu ta ce "Taɓ ƴar gaba da fatihar? Wallahi ba zan taɓa ƙazanta ba, sai dai uwarsa ta wanketa, haka kurum in taɓa masifa"

Sakin baki Iya tayi tana cewa "Wai me yake damun matan nan ne? Ƙaddara ce fa, kowa zata iya faɗa a ka"

Sa'adatu ta ce "A'a irin wannan ƙaddarar Allah ya tsayar da ita a kan wanda ta sama"

Haka dai gida ya yamutse, kamar ayi yaƙi.

Da ƙyar babar Idris ta yi wa yarinyar wanka.

***
Yau lahadi, ummi sun yi hutun makarantar islamiyya, sai dai ta kasa zama wuri ɗaya ta hutawa ranta, dan kuwa ta san babu wanda ya bata wannan damar.
Dan haka wuni tayi tana kaiwa tare da komowa, wurin yin kwalema da tsabtace ko ina na gidan.

Tana sanye da dogon hijjabinta, da ya zame mata tamkar uniform, duk zafi ko sanyi, ko a cikin gida, da hijjbi take yawo, dan ko da ta fara ƙirgar dangi, tsananta rufe jikinta tayi, balle yanzu da take aji biyar na sakandare ta ƙara cika sosai.

Dan idan tana girki, wuta ta sha kamo mata hijjabin, ko ta yi ɓarna a kitchen, farida ta ci mata mutunci, amma hakan bai sanya ta daina sawa ba.

Hijjabin jikin nata ya sha jiki ya koɗe, sai dai kasancewar a goge yake, muninsa ya ragu.

Tana mopping noor na biye da ita suna hira, ta saki jiki tana biyewa noor, suna shiririta.

Ƙamshin turaren da ya cika falon ne, ya sanya ummi ɗaga kai, aikuwa tayi tozali da intee ta fito, sai taku take ɗaya-ɗaya.

Ta sha doguwar rigar abaya, ƙamshin kansa ummi ta kasa tantance wane iri inteesar take yi.

Tayi light make up, sai wani yatsuna fuska take yi.

Ummi a ranta ta ce "Tubarkallah masha Allah, kyau yana in da yake" ba iya kyan da inteesar tayi ne ya burge ummi ba, doguwar rigar jikinta ma ta tafi da ita, ta ji ina ma ita ma tana da ita ta saka, taga ya zata yi a ciki, dogayen riguna irin haka suna burgeta".

"Ke! Kalli gabanta kar ki kama mini kurwar ƴa" farida tayi maganar cikin tsawa.

Ɗan zabura ummi tayi, ta cigaba da aikin gabanta.

Kausar kuwa ta kwashe da dariya, yadda ummin ta ɗan shagala da kallon yayarta kamar shashasha.

Farida ta yi murmushi ta ce "Farar mace....

Caraf kausar ta ce "Alkyabbar mata"

"Farar mace kalar kyau, kalar babban gida da manyan motoci, kalar hutu da jin daɗi farar mace mowar mata"

Inteesar kamar kanta ya fashe, saboda kirarin da mamanta ke yi mata.

Ta dubi ummi ta ce "Baƙar mace borar gida".

Farida ta amsa da "Idan ta samu mijin ba"

"Idan ba ta samu ba kuma ta dauwwama ƴar wanke-wanke"

Ummi tayi burus, ta cigaba da hirarta da noor, tana jin zuciyarta na wani irin zafi.

Intee ta yamutsa fuska ta ce "Maama bari na je, ya kirani a waya, ya zo".

"To shikenan, a kula sosai, a iya karairaya da jan hankali"

"Kar ki damu maama, ammm ummi kin kammala girkin da na saki?"

"Na gama"

"Ok, ki shirya mini komai a tray, in the next few minutes ki kawo mana"

Kallon ƙasan ido ummi tayi mata, ta yi mata girkin tarar saurayi, kuma ita za ta kai musu.

Tayi ajiyar zuciya, tare da ɗan girgiza kanta.

Farida ta ce "Ke ummi in tambayeki mana"

Ummi ta ɗago tana kallonta.

"Wai dan Allah ina babarki ne?"

Ummi ta ɗan yi jimm, dan ba ta zaci wannan tambayar ba.

"Ban san in da take ba"

"Kamar yaya baki san in da take ba?"

Ummi ta ce "Ai tun ranar da ta tafi, Iya ta hana a tafi da ni, ban sake ganinta ba, sau kusan uku ƴan uwanta na zuwa su tafi da ni, amma ta ƙi bayar da ni".

"Kuma saboda rashin lissafi, ba ta sake neman in da ki ke ba, daga ita har ƴan uwanta, yau shekarar ki nawa a gidan nan, ko kare daga dangin majaifiyarki ba wanda ya nemi in da ki ke, wace irin uwa ce wannan? Ko suma ba sa buƙatar ki ne, an rasa mai riƙe ki, aka liƙa mana, anya babu lauje cikin naɗi a game da ke, ta hanyar aure aka same ki kowa yake gudunki?"

Tuni idon ummi ya fara tara hawaye, cikin ƙoƙarin kare mahaifiyarta ta ce "Ai an ce ba ta da lafiya, tun da aka ƙwace ni, ta haihu ɗan babu rai, ta samu matsalar ƙwaƙwalwa"

"Mahaukaciya ce kenan?" Kausar ta faɗa kai tsaye.

Farida ta ce "To ai mahaukaci ya san ɗan sa, jahilci kawai da rashin sanin ciwon kai, idan ita ba ta da hankali, ƴan uwanta fa?"

Ummi ta yi shiru, ta kasa magana.

Farida ta shigo falon a fusace ta ce "Wai ke ummi me ki ke taƙama da shi ne? Cewa fa na yi ki kawo mana abinci, amma dan wulaƙanci kin shanya ni, bana son rashin mutunci"

Ummi ta jingine mopper ba tare da ta ce komai ba, ta je ta ɗauki tray, ta kai wa saurayin intee.
Kallo ɗaya ummi ta yi masa ta sunkuyar da kai, gaba ɗaya bai yi kalar mutane masu ɗa'a ba.

Tunanin abun da farida ta faɗa ya ɗarsu a ran ummi, idan an ce mamanta ta samu matsalar ƙwaƙwalwa, to ƴan uwanta fa, yakamata ace sun nemeta, ta san da a hannunsu take, ba za su wahalar da ita sosai ba.

Sakawa tayi a ranta a wannan karon idan kawu ya zo gida, za ta tuna masa alƙawarin da yayi mata na binciko maata in da mamanta take, dan ita ba ta taɓa jin ko sunan garinsu wani ya faɗa ba.

***
Can gida gagarawa kuwa, an samu da ƙyar da siɗin goshi, su hindu sun karɓi jaririya, babanta ya ce idan ta yi arba'in, su zo su kawo kuɗin aure, kuma yadda ake auren budurwa komai da komai, haka za a haɗo mata, kuma shayarwa da hindu, za ta yi, sai an biyata kuɗin shayarwa ko su dawo musu da jaririyar.

Kan su dawo gida, sai da babanta ya caje su kuɗi masu yawa, sannan suka dawo, suka sanar da Iya abun da babanta ya faɗa.

Iya ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wannan wane irin matsiyatam mutane ne? Sai an yi mata komai kamar auren budurwa ba ta riga ta haihu ba, har wani kuɗin shyarwa suke nema, a gidan ubanwa aka taɓa haka, ai da an dawo da ƴar a din ga bata nonon akuya".

"A'a iya, a samu a lallaɓa mu
End Ads