x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 2 - CUTARWA

  • 3001 words
  • 6000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 547

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
na mamakin irin gashin kanta, dam idan mariya na gyara mata kai, ruf gashi yake rufe mata fuska, tamkar na larabawa.

Allah ya albarkaci gidan malam Hashimu, da yawan yara maza a jikokinsa da ƴaƴansa, mata sam ba su da yawa, kuma da sun tasa ake aurar da su.

Dan haka kusan ummi, ita kaɗai ce yarinya mace ƙarama a cikinsu, sai dai hakan ya zame mata babbar barazana ga rayuwarta!!!

08081012143
                     *CUTARWA!*

Watpad ayshercool7724
Arewabooks ayshercool7724
YouTube Cool hausa novels
What's app 08081012143

BRIGHT PENS
(FREE BATCH)

P2

Yawan kyara da hantara, haɗi da kushe halittar ummi, ya sanya ta zama yarinya mara karsashi ko a cikin sa'aninta. Dan wasu har iƙrari suke ko mayya ce, saboda launin ƙwayar idonta da ta sha banban da ta sauran mutane.

Wasu lokutan mariya duk sha'anin da za ayi na taron mutane, ta kan iya haƙura da zuwa saboda ummi, ba ta son mutane.

Abubuwan da wasu daga samarin gidan suke yi mata ne, ya sanya ta sake tsorata da lamarin mutane, ta fara ganin tamkar ita ta ta duniyar daban take, dan idris ne kawai yake amfani da ita wurin biyan buƙatar sa ba.
Mariya bata taɓa fuskanta ba, wasu lokutan har tsoron nuna wa ummi kulawa take yi, a gaban iya, saboda yanzu zata hau masifa da faɗa, wai tana nuna wa ƴar fari soyayya saboda ba ta da kunya. Ko yaya ummi ta ɗan sake a cikin yara, sai su fara cin zalinta, ko su din ga jan dogon gashin ta, ko jan kumatunta da suke tamkar doughnut ya ji yeast, ko yi mata dariya da ihun baƙar tukunya mai ƙyalli.

Takurar yara ya takureta a gida, a gidan ma iya sashinsu, shi ma fitowa tsakar gida idan ba tare da mamanta ba, ba ta fitowa saboda hantarar da kyarar da iya take yi mata.

Haka rayuwar gidansu ummi ta cigaba da garawa, iya kullum tana cikin haba-haba da ƴaƴa da jikokinta, masu kawo mata abun duniya.

Yayin da ta tattara cin kashinta, a kan balarabe da iyalin sa, tamkar ba ita ta haife shi ba.

Ummi ta ɗan ƙara tasawa, kusan kullum sai ta tambayi babanta, yaushe za a kaita makaranta.

Ganin ta ɗan tasa, kuma idan tana tare da mahaifinta, ko mahaifiyarta, ta kan yi hira da su. Sai dai da tayi yinƙurin gaya musu, abun da su Idris ke yi mata, sai ta kasa ta tsorata idan ta tuna suna cewa za su yankata.

Babanta yana bata lokacin sa, yayi wasanni da ita, har da ƴar tsere a tsakar gida. Da iya ta ganshi kuwa ranar ya shiga uku, da masifa da gori.

Kasancewar garin sun ɗan samu cigaba da wayewa, yanzu ana yin karatu sosai, akwai makarantu, ya sanya balarabe ya kai Ummi makarantar gwamnati, aka saka ta a ECC.

Ta din ga murna ganin an saka mata sabon uniform, fari da kore, ga jakarta baba na gode, an saya mata sababbin litattafai, sai washe fararen haƙoranta take yi cike da yarinta.

Tun sha ɗaya da rabi, mariya ta cewa iya zata je ɗaukar ummi a makaranta, iya ta ce "Mariya wai meyasa ba ki da ta ido ne? Ni zan ƙarasa girkin kenan, ki bari ta biyo yara, ko idan su Auwwalu sun dawo sa ɗaukkota. Ni kaita makarantar ma, Allah ya sa ba asarar kuɗi ba ne ba, kar aje yadda fuskarta take haka ƙwaƙwalwar take, ayi biyu babu".

Wani abu mai ɗaci ummi ta haɗiye, ta cigaba da kaiwa tana komowa, ta faki idon iya, ta ɗau mayafi ta fice ɗaukko ummi, duk da babu tazara sosai, amma yarinya ce ƙarama, ba ta san hanya ba.

Sai dai da ta je ɗaukar ta, ba ta ganta tana wannan murnar kamar lokacin da za a kaita makarantar ba.

Tayi zaton kawai ta gaji ne, dan da yawa yara na ɗokin makaranta, sai an kai su kuma, su ga ba abun da suke so ba, su ce ba sa so daga baya.

Mariya tana cire mata uniform ta ce "Mamana, me aka koya miki a makarantar yau?"

Cike da yarinta ta ce "Lemo aka zana mana"

Tayi murmushi ta ce "sai kuma me?".

"Bana son makaranta, ba zan sake zuwa ba?"

"Subhanallah, ummina meyasa?" Ta yi maganar cikin kulawa.

"Yala cu na ce mini baka" (Yara suna ce mini baƙa)

Mariya ta yi ajiyar zuciya ta ce "Kar ki kula su Yarinyar kirki, ki din ga mayar da hankali a kan abun da malama take koya muku"

"Ni bana son ana cewa baka"

"Za su daina Ummi, yarinta ce take damun su"

Ummi ta ce "To"

Hargowar iya ta jiyo a tsakar gida"Sai ka ce mayya, kamar a duniya babu wanda ya taɓa haihuwa sai ke, ai ba a banza ba wannan kalar idon na ƴar ki, na fara zargin akwai masu lashe-lashe a danginku, dan baƙar masifa, sai da ki ka tafi yawon ɗaukotta, shafaffiya da mai" Mariya ta yi shiru ba ta ce komai ba.

Sa'adatu matar Sagir, da tayi sallama a sashin ta tarar da iya tana ta zuba tijara, ta ce "Iya ke da wa kuma a tsakar ranar nan?"

"Wacece idan ba mariya ba? Duniya kamar babu wani mai ɗa sai ita, in dai aka wannan mummunar yarinya ce, ba ta ji ba ta gani".

"Iya kenan, mutum da ɗan sa ai sai Allah, sauran kunu na zo idan akwai in bawa yaro, ya fara yi mini kukan yunwa"

"Shiga ciki ki duba, ni fita zan yi" tayi maganar tana saɓa mayafinta a kafaɗa ta fice.

Sai da iya ta fita, sannan ta lallaɓa, ta fito yi wa ummi wanka.

"Maman ummi, ashe ummi kuma an shiga makaranta"

Mariya ta ce "Wallahi kuwa, ummi an shiga Ecc"

"Masha Allah, Ubangiji Allah ya yi jagora, ya sa an shiga a sa'a"

Mariya ta amsa da "Amin"

Ummi ta ɗan samu sassauci, daga laluben da samarin gidan suke yi mata, saboda shigarta makarantar boko, tun safe sai sha biyu na rana, daga nan kuma ta kwanta tayi ta bacci, wasu lokutan yaran gidan da ƴan sa'anninta, su zo su tafi da ita makarantar allo.
Duk da kuka wasu lokutan kuka take ba ta so, haka mariya ke tursasa mata ta tafi, saboda shi ilimi, dole a tsayawa yaro yayi shi, ko da kuwa ba ya so, mussaman ma na addini.

Duk da a hakan wasu lokutan ba ta tsira ba, ba ya hana azo har sashin su a ɗauke ta, idan mariya zata hana, iya tayi ta masifa.

***
Yau Mariya ta yi yamma wurin girki, tana ta aiki a tsakar gida, iya tana zaune a kan kujera ƴar tsuguno, ta kasa ta tsare, sai waƙe-waƙenta take yi na mutanen da, waƙoƙin daɓe wasu kamar na batsa,wasu kamar habaici.

Wata mata ce tayi sallama, suka amsa baki ɗaya, matar ta gaida iya, Iya ta amsa mata cikin sakin fuska har da yi wa ɗan matar wasa.

Mariya ta ce "Mai koko ke ce da yammacin nan? Bari na baki abun zama"

Mai koko ta ce "Wallahi kuwa, haja na kawo miki"

Mariya ta shimfiɗa mata tabarma ta ce "Haja kuma, to Allah ya sa ba ta fi ƙarfin talaka irin mu ba".

Mai koko ta kwance kaya, kayan yari da sarƙa ne da mayafai a taƙaice dai kayan koli ne.

Mariya ta yi ta ɗaɗɗagawa, kayan sun yi mata kyau sosai, ta san idan ta ɗauka baban ummi ba zai ce komai ba, amma ba ta son takura shi, dan haka ta ce "Mai koko muna da ɗan kunne, maɗaurin gashi na so saya wa ummi, sai dai wannan sun yi ƙanana ba zai riƙe gashinta ba, sai dai idan muna buƙata zan yi miki magana da yardar Allah"

Ita ta ce "Ke ma dai mai koko, ke da ki ke neman arziki, ina ke ina kawo wa wannan kaya, ba su da komai sai tsiya da babu, ki kai sashin Sagir, ko gidan iliya, wannan ai da kin taɓa su babu".

"Na ga alama kam, ban taɓa kawo kaya mariya ta saya ba, kullum sai aukin idan tana buƙata ta aiko ta saya".

"Kema tun da aka yi ɗaya biyu, ai ba kya bari ayi uku ba, da dai hidimar ƴar ta ce, nan tafi kauri, ta kanainaye mini ɗa ta hana shi arziki"

Tuni mariya ta tashi, ta koma kan aikinta.

Mai koko ta ɗaure kayanta ta ce "Aikuwa iya ki dage da nema masa magani, ƴan uwansa duk suna da rufin asiri ban da shi, sa anjima"

"Yawwa ki gaida gida"

Ba ta sake bi ta kansu ba, kamar kullum yau da wuri ummi tayi bacci, bayan mariya ta kammala girki, ta ɗebi gawayi, ta goge wa ummi uniform ɗin ta, ta gama komai, tana jiran dawowar baban ummi.

Kamar mai kiran kurma, Iya ta ƙwala mata kira, ta fito da sauri a ɗan razane ta ce "Iya gani"

"Maza yafo mayafinki, ƴaron wurin iliyasu ne, ƙaramin ya haɗiye ƙaya, ku ɗauki yaron ki raka Sa'adatu ku je gidan sarkin suu, ya bashi magani"

Ɗan jimmm mariya tayi, so take ta huta, tun safe take aiki a gidan kamar jaka, yanzu kuma iya ta tsiro da wani abun.

Ba yadda ta iya, ta ce "To, bari na goya ummi, dan tayi bacci"

"Wai ke wace irin mace ce, har yaron ya mutu baki gama goyon wannan buhun sumuntin yarinyar ba, ban da rashin kara, ai ke yakamata ki goya mata yaron, dan Allah ki hanzarta ku tafi, ina nan me zai samu ummin, hanzarta maza".

Haka nan mariya ta ji gabanta yana faɗuwa, kamar wani abu zai faru idan ta tafi, ga Iya sai ɗaga mata murya take a kan tayi sauri.

"Iya zan iya goya ummin, sai in ɗauki yaron a hannu"

"Wai mariya meyasa baki da kunya, ina faɗa kina faɗa? Salon ki je ki kayar da yaron, ga wannan uwar ƴar ta ki, kaya guda a haka zaki ɗauki, yaron ba zaki hanzar ta ba, ko dan ba ɗan ki bane ba, ko da yake ina mai ɗa ɗaya ya san ciwon ɗa ma"

Ta ce "To ko in kawo ta ɗakin ki, sai in kwantar da ita, idan na dawo na ɗauke ta?"

"A'a ba zaki kawo mini ita ta yi mini fitsari ba, wannan samgartacciyar yarinyar, ɗuwawunta ba shi da saiti. Uban meye ma zai kamata a ɗakin, ki wuce ku tafi"

Jiki a sanyaye mariya ta shiga ɗaki, ta ɗakko mayafinta, ta na ta kallon ummi, tana fatan Allah ya sa babanta ya shigo da wuri.

Ta fito tsakar gida wasu daga cikin jikokin iya suka shigo, shigowar su bai sanya iya yin shiru ba, ta cigaba da yi wa mariya masifa.

Duk mutanen da ke cikin gidan, iya ta rasa wanda zata saka yayi rakiyar kai yaron sai ita, saboda dai kar ta huta, kuma kar ta zauna lafiya.

Suna tafe a hanya tana goye da yaron, sai kakari yake yi, saboda yadda ƙayar take sukansa. Ga gidan sarkin su da nisa sosai, haka suke tafe da fitila.

Sai dai zuciyarta sai harbawa take yi da sauri, hankalinta yaƙi kwanciya, ji take tamkar ta juya da gudu, ta koma wurin ƴar ta.

Sai wajen tara da rabi suka dawo, gudu-gudu sauri-sauri ta nufi sashin su, ba ta bi ta kan iya ba, ta nufi ɗakinta.

Sai dai ta kai kai zata shiga ɗakin, shi kuma ya fito da sauri, jikinsa yana tsuma.

"Me ka ke yi mini a ɗaki yanzu? Me ka yi?" Shiru yayi yana tsuma tare da kallon ta, ta hasken farin wata.

"Me ka yi mini a ɗaki i yanzu? Me ya kai ka ɗakina?" Tayi maganar cikin ƙaraji.

Iya ta ce "Wai lafiya kuwa? Kun dawo kenan ya jikin yaron?" Hankaɗe shi ta yi daga gabanta, ta shiga ɗakin da sauri, tana kiran sunan "Ummi"

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Iya! Iya! Zo ki ga? Iya zo da sauri"

Da sauri iya ta taho da gudu tana cewa "Wai meye ne?"

Ta shiga ɗakin, ta tarar da ummi a kwance, tana ta numfarfashi, jikinta sai rawa yake yi, an tura mata hularta a bakinta, ga wandonta a yashe a gefe gabanta duk jini.

Iya ta dafe ƙirji ta ce "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'una, wace irin masifa ce wannan, me yaron nan ya zama, kar dai ki ce mini yaron nan ne?"

Cikin kuka mariya ta cirewa Ummi abun bakinta ta rungume ta, cikin ɗaga murya ta ce "Haba iya, da idonki fa kin gani, kina gani fa, waye ya fita daga ɗakin nan idan ba shi ba, na shiga uku na lalace an cuce ni, an cuci ƴa ta"

"Dalla ki rufewa mutane baki, idan kuma kururwar zaki cigaba, ki tonawa kanki asiri shikenan, idan ba wata ƙaddara ta Allah ba, waye ma zai aure ta, balle a san me ya faru da ita" sororo mariya ta bi iya da kallo, wanda hakan yayi dai-dai da sallamar baban Ummi.

Iya ce ta iya amsawa, ya shigo ya same su, mariya rungume da ummi tana kuka.

"Maman ummi, Iya meyafaru ne? Ummin ce babu lafiya?"

Mariya ta ɗaga masa ƙafar ummi, tana kuka ta sanar masa da abun da ya faru.

Salati ya saka ya durƙushe a wurin.

Iya ta ce "Da ki ke ɗorarwa ke kin tabattar shi ɗin ne? Sai ki jirani in bincika in tabbatar ai". Ta tashi ta fita daga ɗakin.

"Mariya, kina me? Garin yaya? Ya aka yi haka ta faru"

Cikin kuka mariya ta ce "Wallahi iya ce baban ummi, iya ce na shiga uku an lalata mini rayuwar ƴa ta, ina zan saka kai na"

Iya ce ta dawo riƙe da hannunsa, zuwa cikin ɗakin ta kalleshi ta ce "Uban wa ye ya yi wannan aikin? Me ka yi mata, ba sallama ka yi mini ka ce zaka tafi shagonku ba?"

Jiki a sanyaye ya ce "Wallahi iya tsautsayi ne"

A fusace balarabe ya tashi ya shaƙe shi, ya ce "Tsautsayin ka kasa sauke shi a ko ina, sai kan ƴa ta".

"Zaka cika shi ko sai na ɗauke ka da mari? Ba ɗa yake a wurin ka ba kai ma? Idan ɗan ka ne ya aikata hakan, tona masa asiri zaka yi? Ko idan ka tayar da maganar wani abun hakan zai amfanar, aikin gama ya riga gama.
Kuma bari ka ji in gaya maka, wallahi tallahi, muddin ku ka ɗaga maganar nan, wani ya ji ta, bayan mu ɗin nan, Allah ya isa ban yafe ba, kowaye sai na tsine masa. Ita dauɗar gora ai ciki ka sha ta. Idan baku rufa musu asiri ba? Waye zai rufa musu ko salon zumunci ya lalace? Ƙuruciya ce da ƙaddara da bai wuce kan kowa ba"

Da wani irin mugun sauri zuciyar mariya ke yi, ƙuruciya ga yaron da har ya san, ya toshe mata baki da tsumma, ya keta mata haddi, shi ake kira da ƙuruciya.

Jiki a sanyaye balarabe ya ce "Shikenan iya, duk ba za ayi haka ba, in sha Allah hakan ba za ta sake faruwa ba, an bar maganar da yardar Allah"

Ta kalli saurayin yaron ta ce "Kai kuma wuce ka bani wuri, wallahi ka sake aikata makamancin haka, da kaina zan ci ubanka na hukuntaka. Wuce ka bar ɗakin nan". Ya fice sumi-sumi ya ci bulus.

"Ke kuma ki daina wannan kukan, ki tashi ki dafa ruwa, ki sakata a ciki, kiyi haƙuri, ko ki cigaba da kuka baƙin ciki ya kashe ki" daga haka ta juya ta fice.

Tana fita mariya ta kuma rushewa da kuka ta ce "Yanzu shikenan baban ummi, yaron nan ya ci bulus kenan? An lalata mini rayuwar ƴa, har iya na cewa wai babu lallai wani ya aureta, wane irin abu ne wannan?"

Zuciyar sa fal takaici da ɓacin rai, saboda kar ya sake karya wa mariya gwiwa ya ce "Dan Allah kiyi haƙuri mariya, ki kwantar da hankalinki, kin ga iya uwata ce, ba yadda na iya, dan Allah ki yi haƙuri ki tayani yi mata biyayya, mu ɓoye sirrin nan, ko dan mutuncin ummi, kar abun yayi mata yawa. Dan Allah ki yi haƙuri mariya"

Tashi tayi ta kwantar da ummi, ta fita tsakar gida.

Babanta ya rungume ta, jikinta ya ɗau zafi, tana jin yadda hawayen sa ke ɗiga a hannunta.

"Ummina sannu kin ji? Meye yake miki ciwo?" Tayi shiru ba ta yi magana ba, sai sheshsheƙar kuka.

Mariya ta kawo ruwa a baho, ta fizge ummi daga hannun balarabe, ta saka ta a cikin ruwan ɗumin. Sai a lokacin ummi ta zabura ta fashe da kuka, ta ce "Mama zafi".

Tana kuka ummi na kuka, ta yi mata wanka, ta saka mata kaya, ta nemi wuri ta kwanta, ta share balarabe.

Kwana suka yi ummi na koke-koke, ko barci ya ɗan ɗauke ta, sai ta zabura tana turza ƙafarta tana ihu.

Haka mariya ta kwana kuka, da balarabe ya kai hannu zai taɓa ummin, sai ta ɗauke ƴar ta, ta juya masa baya.

Wayewar garin Allah, mariya ta saba zuwa ta gaida Iya, amma a ranar taƙi kula kowa, ta ƙi ɗora girkin gidan.

Yara masu tafiya makaranta, duk sashin ta suke zuwa karɓar kunun safe, su sha su tafi makaranta, ranar shiru ba ta ɗora ba, kowa yazo sai ya koma.

Balarabe ya din ga raragefe, ya rasa me zai cewa mariya, ya san ƙarshen cuta an yi mata, ba ma ita kaɗai ba, har da shi, sai dai ba yadda ya iya sawun giwa ya take na raƙumi, iya mahaifiyarsa ce ba yadda ya iya, dole ya bi umarnin ta.

Yayi shirin sa zai fita kasuwa, jiki a sanyaye ya ce "Mariya, ko asibiti zamu kaita, na ga kamar da zazzaɓi ta kwana".

"Dan Allah ka ƙyale ni da abun da ya dame ni, ka ƙyale ni bashir ka ƙyale mini ƴa ta, duk muninta daga jikina ta fito, ni na damu da ita, tun da a gurin kai da mahaifiyar ka, ba ƴa ba ce. Tun da baban sa yana da kuɗi dole ta ce dauɗar gora ciki ka sha ta, nayi imani da Allah da ɗan ka ne, yayi laifin nan, kowa sai ya ji" tayi maganar cikin matsanancin kuka.

Lallai mariya ta kai ƙarshe a ɗaukar zafi.

"Ki yi haƙuri mariya, ke kin san ina ƙaunar ƴa ta, ba yadda na iya ne, wallahi mariya ba ki fi ni shiga damuwa da tashin hankali ba, ki yi haƙuri dan Allah"

Ba ta kuma kula shi ba, ta cigaba da shafa kan ummi, da ta ɗan samu bacci, tana zubar da hawaye.

Da son ransa ne, ya wuni tare da su, ya cigaba da rarrashin ta, amma ya san idan ya ƙi fita, wani tashin hankalin zasu fuskanta daga Iya.

Gaba ɗaya girkin ma taƙi yi, ummi kawai ta samawa abun da
End Ads