x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 18 - CUTARWA

  • 51001 words
  • 54000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 499

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
tafarnuwa suna da tasiri a gumin mu da sauran fluids da muke fitarwa a jikinmu.

Kawu yahaya duk ya haɗowa ummi abubuwan da suka kamata, suna tafe yana sake yi mata bayanin yadda zata yi amfani da su.

Sai azahar suka koma gida, sai dai matar gidan bata nan, da kansa ya bi ummi ɗakin masu aikin, ya dudduba abun da babu ya ce zai sayo mata.

Tamkar yar da ya haifa a cikinsa haka yake jin ummi,kuma haka yake burin ta samu lafiya daga wannan ciwon, dan ya san illarsa da hatsarinsa, dan ya san halinsu maza bakomai suke iya jurewa su kawar wa da kai ba.

Ya nuna mata yadda za ta din ga amfani da heater, da sabon flask ɗin ruwan zafi.

Da kansa ya tafasa magungunan, ya zuba mata a jarka, na kama ruwan ya zuba mata a cikin flask ɗin shayi, ya ɗaukko tsintsiya ya taimaka mata wurin gyara ɗakin saboda an kwana biyu ba a gyara shi ba.

Ya je ɗakinsa ya duba bedsheet ɗin da shi ya saya da kuɗinsa, har da bargo ya kawowa ummi.

Ya bata babban gwangwanin turare a cikin nasa ya ce ta din ga fesawa.

Kallonsa kawai ummi take yi, cikin jin daɗi da annashuwa, yadda ya zage yake ta ɗawainiya da ita, daga jiya zuwa yau, idan ta ce ya bari tayi da kanta, sai ya ce mata ai bata da lafiya, kuma cikin barkwanci ya ce mata albarkar ummansa yake nema.

Haka nan ummi ta din ga murmushi tana yi masa godiya.

Ya ce "Yauwwa ummina, Allah yayi miki albarka, saura makaranta ita ma in sha Allah sati mai kamawa, zaki koma makaranta ki manta da duk abu da ya faru, iyaka dai kar ki sake ki gaya wa wani kin taɓa aure kin ji ko?"

Ta jinjina masa kai ya ce "Good, yi wanka ki yi salla, a cikin kayan nan akwai gurasa ki ci kiyi kwanciyarki ki huta"

Murmushin kawai da ya gani a fuskar ummi, ya sanya shi cikin farinciki, kullum yaje ƙauye sai dai ya tarar da ita cikin kuka, sai kuma Murmushin yaƙe.
Hatta yadda zata din ga amfani da banɗaki, sai da ya nuna mata komai.

Fitowa yayi daga ɗakinta, a zuciyarsa yana tawasalli da farincikin da ya saka marainiya yana addu'a Allah ya biya masa buƙatunsa na alkhairi.

Ba yau farida ta fara fita yawonta ba, tun yana faɗa har ya gaji ya daina yi.

Ummi kuwa tun daga kama ruwan da tayi, ta ji daɗin jikinta, ta tsiyayi maganinta ta sha bayan ta ci gurasar nan, ta ɗauki sabon phanta ta canza.

Wani irin daɗi take ji da nishaɗi, ta sake bubbuɗe kayan da ya saya mata tana jin daɗin hakan.

Ko da wasa ba ta yi gangancin fitowa daga ɗakin nan ba, dan ta fuskanci ƴan gidan ba ƙaunar ganinta suke yi ba.

Ana kiran sallar la'asar ta yi salla, ta cigaba da zamanta a ɗakin.

Kamar an watso su, taga farida da rahama a ɗakin, hakan ya sanya ta tashi a razane.

Farida ta ce "Tashi munafuka, ai ba zama ki ka zo yi ba" a zabure ummi ta tashi tana rarraba ido.

"Ba dai kawo ki aka yi leƙen asiri da saka mini ido ba, zaki ci ubanki sai kin bar mini gida da ƙafarki" idonta ya sauka a kan ƙatuwar ghana must go sabuwa fil.

Ta ce "Rahama janyo mini jakar nan ki zazzageta, wato zuwa yayi ya kashe mata kuɗi, wallahi ba zai yiwu ba ya daidaita da ƴaƴana, kar ta san kar ai".

Rahama ta janyo jaka, suka zazzageta, farida har da ashar, farida ta saka farida ta tsitstsince mata kayan, phants ɗin ma duk ta kwashe ta bar mata uku, Allah ya taimaketa, tana da sauran wanda ta zo da su, da na'ima ta saya mata.

Cikin ikon Allah, Allah ya taimaketa basu lura da ƙullin kayan maganin da ke bayan katifar ɗakin ba, heater da flask ɗin kuma suna cikin banɗaki.

Hatta omo da sabulun da ya saya mata, sai da suka kwashe ta bar mata ɗai ɗai.

Sannan ta sake dubanta a wulaƙance ta ce "Ki buɗe kunnenki da kyau ki saurareni, nan gidana ne, abun da na dama shi ake sha, shima kwana biyu na sarara masa ne, amma tun da haka ya zaɓa zan yi maganinku duka. Ki saka a ranki ke ƴar aiki ce kawai a gidan nan. Kullum da yamma idan yara suka taso daga makaranta, zaki wanke musu uniform ki goge musu shi tas, wanke-wanke da duk wani aiki a gidan nan ke zaki din ga yin sa, idan ki ga dama ki gaya masa babu abun da zai iya yi a kai, bari in gaya miki ƙiri-ƙiri idan ki ka sake kiransa da Abba sai kin bar gidan nan, dan bai haife ki ba.
Kuma wanki ba na yara kawai ba, kaya ko na waye sai kin wanke a gidan nan, tashi mu je ma ki fara aikin ki daga yanzu. mummunar banza kawai".

Rahama ta kwashe da dariya ta ce "Ni wallahi fuskarta ma dariya take bani, wannan baƙi kamar a dangwala".

"Rabu da ita tashi ki wuce" ummi kaf maganganun su babu wanda ya ɓata wa ummi rai, dan ba yanzu aka fara yi mata ba, ƙwace mata kaya yafi komai ɓata rai.
Sai dai wata zuciyar ta ce da kin san zaki samu ne?.

Saboda tsabar mugunta akwai injin wanki a gidan, kuma akwai mai guga, amma farida ta tula wa ummi kayan makarantar su Abdul, na boko da islamiyyar su, kusan kowanne nasa set uku, daga na makarantar boko har na islamiyya.

Ummi ko a jikinta, ta durƙusa ta fara wankin kayan nan.
Tas ummi ta wanke su, kasancewar ta riga ta saba da wahala tun a gaban Iya.

Bayan ta gama cike da mugunta, rahama ta ja ta kitchen, ta sakata sassauke kwanukan da sun fi wata shida ba a saukko su an yi amfani da su ba, ta ce ummi ta wanke.
Babu ƙyuya ko ƙosawa ummi ta wanke su.

Duk yadda suka wahalar da ummi a yammacin nan har zuwa bayan isha'i, ko da wasa bata nuna musu gazawarta ba.

Kwanaki uku da zuwanta gidan, rashin mutunci da kyara, haka babar su Abdul suke yi mata, da yaranta da ƙanwarta, kuma wasu lokutan a hana ummin abincin.

Sai dai lokaci ɗaya kawun nata ya rage bata wannan kulawar da yake bata da farko, hakan sam bai damu ummin ba, dan gani take duk wahalar da zata sha, ba zata kai ta gidan Iya da idris ba.

Ranar lahadi suka koma ganin likita, sai dai ummi ta ji daɗin amfani da magungunan nan, dan kuwa sosai yayi mata sauƙi ba kamar da ba.

Likita ya dubata, ya rubuta mata magunguna, Allah ya sa kawu yahaya bai yi ƙwauron baki ba, ya sanar masa magungunan da take sha, likitan ya ce ta ajiye su ta gama shan na asibiti, idan suka ƙare ta cigaba da waccan.

Yayi masa godiya suka tafi gida, suna tafe yana rarrashin ummi, yana yi mata nasiha.

Sai da ummi ta yi sati biyu cif a gidan, baban su Abdul ya cewa farida zai kai ummi makarantar su Abdul, amma ta ce ba ta yadda ba, sai dai ya nemi wata mai arha ya kai ummi, dan ba zai dai-daita ta da yaranta ba.

Staff school ya saka ummi, ta nan makarantar da yake lecturing, makarantar islamiyya ma, wata daban ya saka ummi, sai dai makaranta ce mai kyau sosai ana karatu, dan akwai ƴaƴan manya a makarantar.

Duk wanda ya shigo gidan nan ya ga ummi, sai farida ta ce musu ummi sabuwar ƴar aiki ta yi, su yi ta yaba ƙoƙarin ummi, yarinya ƙarama amma ba ta jin jikinta.

Ko da ummi ta fara zuwa makaranta, a nan ɗin ma bata sauya zani ba, saboda ba ta tsira daga cin zarafi daga ɗalibai ba, saboda launin fatarta da ta idonta.
Wahala ta ƙara ƙaruwar mata a ka, ga zuwa makaranta, ga kuma aikin gida tamkar jakarsu.

Hatta rahama idan ta dawo daga makaranta, har wankin phant da brezia haka take watsowa ummi, ƙarewar wulaƙanci har da wando mai jini, sai ta cire ta bawa ummi ta wanke mata.

Iya shege da rashin kunya kuwa a wurin su intee, ba a magana, sai ta gyara wuri su ɓata, idan suka ci abinci sai ta bi ta ɗauke musu kwanuka, sai dai kawu yahaya baya iya magana, yana ji yana gani farida da ƙanwarta suka mayar da ummi baiwa, ban da cin mutunci da wulaƙanci da muzanta halittarta. Dan har haramta mata zaman kan kujerar falo aka yi, wai kar ta shafa baƙi a jikin kujerar.

Abdul ne ma ruwansa da ita, dama shi ba wani magana ya cika yi ba sosai.

Yau ma farida ta tafi gida wai suna biki, ga tsohon ciki, amma kamar akuya saboda gantali, gashi tana cikin watanta na haihuwa.

Daga ummi sai Abdul, sai kuma kawu yahaya da yake gida.

Tana ta aikace-aikace, cikin tausayawa kawu yahaya ya ce "Sannu da aiki ummina, ki samu ki je ki kwanta ki huta".

Tayi murmushi ta ce "Kawu na kusa gamawa ai"

"Ummi kin daina kirana da Abba dai sai kawu ko?" Tayi shiru tana murmushin yaƙe.

Bayan ta koma kitchen, ya numfasa ya ce "Yaya" Abdul ya ɗago ya ce "Na'am Abba".

"Yanzu muna tare muna rayuwarmu, gwanin sha'awa kuna rayuwa tsakaninmu cikin jin daɗi, hakan yana yi muku daɗi ko?"

Yayi murmushi ya ce "Sosai makuwa Abba".

"Allah sarki, kamar haka idan Allah ya so, a kowane lokaci zai iya raba mu, muna raye ba tare da wani ya mutu ba, amma zai iya rabamu, kamar yadda ya ɗauke mahaifin ummi, ya rabata da mahaifiyarta, ya kawota zama a cikinmu. Ina kallon duk abun da mamanku take yi wa yarinyar nan, da ita da ƙannenka, ko ban ce komai ba, Allah yana kallon komai, dan Allah ko daga ɓangaren ka ne ta samu sassauci, ba dan Allah baya son ta ya ɗauki mahaifinta ba, ya kawota cikinmu ba, zaka so ayi treating ɗin ƙannenka kamar yadda ake treating ɗin ummi?".

Jiki a sanyaye Abdul ya girgiza kai.

"To dan Allah ka din ga nunawa ƴan uwanka, ummi mutum ce, kuma ƴa ce kamar ku, muzanta ta da bautar da ita, ba shi da wata fa'ida" ya din ga yi wa Abdul nasiha, sai duk jikinsa yayi sanyi.

Sai dare sannan suka dawo, suna dawo gidan kamar sun dawo da dauɗa, suka cire kaya suka zubar, suka ci abinci suka baje kwanuka.

Abdul ya tarar da ita a kitchen, tana ta wanke kwanukan da suka ci abinci, ya kalli ummi ya ce "Ki je ki kwanta, yakamata ki huta".

Ummi ta ce "Kwanukan nan zan ƙarasa wankewa"

Ya ce "Bari na tayaki"

"Maza basa wanke-wanke"

Tun da ta zo gidan nan, maganar kirki bata taɓa haɗa su ba, ba ruwansa da ita, dan haka yau tayi mamakin cewa da yayi zai taya ta aiki.

Shi dai tun da Abba yayi masa wannan nasihar ɗazu, gaba ɗaya sai tausayin ummi ya kama shi.

Kallonsa take yi tana mamaki, yadda yake kikkife mata kwanukan, ummi sai cewa take yi ka bar shi fa yaya Abdul.

"Uban me ka ke yi a kitchen ɗin nan?" Rahama tayi maganar tana shigowa hannunta riƙe da indomie.

"Aiki nake taya ta".

Ta watsawa ummi indomie, ta ce idan ta gama, ta dafa mata guda biyu.

Ko da wasa ummi babu alamar gazawa a fuskarta, ta dafa mata indomie, Abdul yana biye da ita, ta gama yayi zaton kwanciya ummi za ta yi, amma ta kwaso uwar guga ta hau yi, kayan su na babarsu da na rahama.

Abdul ya zuba mata ido, tana ta sauri ta kammala gugar, dan tana da assignment, tana yi yana ƙoƙarin yi mata hira, amma kasancewar ba sabawa suka yi ba, ya kasa ya saukko ya ce bari ya taya ta.
Ba iya gugar yayi ba, ummi tana nuna masa yadda zai yi, sai dai bisa tsautsayi Abdul ya ƙona rigar babarsa, ta lace babban lace ba ƙarami ba.

Hakan yayi dai-dai da fitowar rahama, ta gansu a tare Abdul da dutsen guga. Ta buɗe murya ta ce "Anty farida, zo ki ga bariki, aikin da ake sakata take rabawa da ƴaƴan gida".

Abdul ya ce "Ni ne na ce zan tayata fa"

Farida da ƙyar ta ƙaraso falon, saboda ciwon baya da mara da take yi.

"Uban me ka ke yi a nan a wannan daren?".

Ya ce "Bakomai".

"Tashi ka wuce ka je ka kwanta" ya tashi ya nufi hanyar ɗakinsa.

Idonta ya sauka a kan rigar leshinta, da sawarta uku an ƙona rigar.

Ashar ta lailayo, ta ɗago rigar ta ce "Rigar ta wa ki ka ƙona mini? Dan ubanki dan baki da mutunci ba ki da hankali?"

"Anty dan Allah ki yi haƙuri, tsautsayi ne, ban san zata ƙone ba"

"Wallahi sai na ƙona ki da iron ɗin nan, ke wallahi sai na fanshe rigata, kut lallai baki da hankali"

Miƙews ummi tayi, ta fara kuka tana bata haƙuri, amma rahama ta danƙota, ta danne ta farida ta sake jona iron ɗin ya ɗau zafi, ta nufo ummi.




(*Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ina amfani da wannan dama wurin miƙa saƙon ta'aziyyata, ga ɗaukacin marubuta, na rashin ƴar uwa marubuciya, maryam nasir marsad, dan girman Allah duk wanda ya karanta page ɗin nan, muna barar ƙulhiwallahu ƙafa uku, Ubangiji Allah ya yi mata rahama, ya kai haske kabarinta ya sanya bakin wahalarta kenan, idan ta mu ta zo ya sanya mu cika da kyau da imani Amin*)

(MASU NEMA DAGA FARKO, KU DUBA A WATPAD PLEASE 🙏)

Ayshercool
What's app only please 🙏
08081012143.
                            *CUTARWA!*

   

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

BRIGHT PENS
FREE BATCH

P15

Ihu ummi take yi, tana yi musu magiya su yi haƙuri, amma cike da mugunta da zalunci, rahama ta danne ummi a ƙasa, ta cusa mata ɗan kwali a baki, ta yadda sautin ihunta ba zai fita sosai ba, ta ɗage wa ummi riga, farida ta din ga nana mata iron ɗin  nan a cikinta da zafinsa da komai.

Wata irin miƙa ummi take, saboda azabar da ta ratsata, take ta saki fitsari, saboda azabar zafi da ya ratsa ta.

Abdul har ya je ɗakinsa ya tuna ya ƙona rigar maama, kuma ƙila ummi zata hukunta, dan haka ya juyo da sauri, ya dawo falon.

A gigice ya ƙarasa wurin, ganin bala'i da izayar da ake yi wa ummi.

"Maama dan Allah ku bari, ba a yi wa mutum azaba da wuta".

Fitsarin da ummi ta saki, ya sanya rahama cikata, ta rufeta da duka, saboda ta ɓata mata jiki da fitsari, ta fizge hijjabi da hular kan ummi, a take dogon gashin ta mai matuƙar santsi ya zubo har fuskarta.

Rahama ta ce "Kut, wannan gashi ko attach" tayi maganar tana jan gashin ummi da ƙarfin gaske, ummi jikinta ya din ga rawa, ta kasa ihun saboda azaba, ta riƙe gashinta da rahama ta cika hannu da shi.

Abdul ya fara ƙoƙarin ture rahama daga kan ummi, farida ta kai ƙafa zata daki ummi, ta zame da ruwan fitsarin da ummi tayi, ta faɗi.

Wani irin ihu ta kurma, rahama ta ɗaga ummi, ta nufeta a gigice, ummi ta samu ta lallaɓa ta tashi da gudu, ta tafi ɗakinta.

Banɗaki ta shiga, ta cire rigarta ta din ga zuba ruwan famfo a cikinta, tana jin tamakar wurin ci yake yi da wuta, ga wani irin azaba da kanta yake yi, har wani jiri take ji.

Kan ka ce kwabo jini ya fara zuba daga jikin faruda, jikinta ya fara kakkafewa, rahama ta ce "Abdul yi sauri ka je ka taso abbanku" Abdul ya tafi da gudu ɗakin da mahaifinsa yake ta bacci, saboda a gajiye yake sosai, duk wainar da ake toyawa bai sani ba.

"Abba, Abba ka tashi maama ta faɗi ƙasa"

Da ƙyar ya buɗe ido, ya kalli Abdul ya ce "Meyafaru?"

"Maama ce ta faɗi a falo" agogo ya kalla, ɗaya saura na dare, me ta je yi falo a yanzu?". Ya saukko daga kan gadon, suka fito falon tare, falon sai ƙauri yake yi saboda iron da aka bari a jone.

Jini take zubarwa sosai cikin gushewar hankali, da sauri kawu yahaya ya ɗaukko mukullin motarsa, da ƙyar suka ɗaga farida, saboda nauyin cikin ta suka bar Abdul a gida suka tafi asibiti.

Ummi ba ta san abun da ake ciki ba, tana can tana jinyar cikinta da suka ƙona da dutsen guga.

Ta zauna ta yi shiru tana ta tunanin, me ta aikata da ya sanya kowa ba ya son ta ji daɗi, kowa babban burinsa shi ne ya ga ya cutar da ita ta yi kuka?

Ta ɗauki vasaline ta shafawa wurin, duk da haka sai da ya fara ɗurar ruwa, duk fatar cikin ta tashi.

***
Idiris a tunaninsa tafiyar ummi, shi ne samun sassauci a gare shi, ya yar da ƙwallon mangwaro ya huta da ƙuda.

Hashim kuma Iya ta sako shi gaba da cin mutunci, ko gaisuwarsa ta daina amsawa, saboda haushin gayawa kawu yahaya abun da ake ciki da yayi, ya sanya yahayan yana yi musu kallon azzalumai.

Idiris ya lallaɓa ya cigaba da zuwa wurin hindu, yana son ya hilace ta su aikata alfasha, tun da iyayenta sun ƙi ya aureta.

Gulmace-gulmace suka din ga yawo, a kan azabtarwar da Iya ta yi wa ummi, da wanda idris ya yi wa ummin, tare da ƙoƙarin bankaɗa asirin dalilin da ya sanya aka fasa auren idiris da hindu, ana ta zaginsu a unguwa, aure wata ɗaya ya mutu.

Haka nan sai ummi ta din ga yi wa Idris gizo, idan ya je gidan da suka zauna.

Ko kuma yayi ta mafarkinta tana yi masa mugun kallo tana kuka. Gashi duk wannan abun da ya faru, ya kasa daina jin sha'awar ummi, ya kuma kasa manta yadda jikinta ke da matuƙar taushi kamar auduga.

Tun da yake leƙe-leƙnsa, bai taɓa taɓa mace mai laushin fatar ummi ba, gashi dai ko man shafawar kirki ba ta da shi, amma fatarta har wani irin santsi take yi.

Ya din ga tuhumar kansa, da ganin wautar sa na kasa daurewa ya sauke abun da yake damunsa game da ummin kan su rabu, amma da ya tuna annakiyar dauɗar da ke jikinta, da kuma warin da take yi sai yayi tsaki.

A rashin ummi ya cigaba da ƙoƙarin hilatar hindu, yayi lalata da ita, hindu yarinya ce ƴar shekara goma sha shida, gidan su suna da tarbiyya sosai, dan haka sai wahalar da Idiris take, taƙi bashi haɗin kai, sai dai tana matuƙar ƙaunar idiris.

***
Likitoci suka rufu a kan farida, ana ta ƙoƙarin ceto ranta, sai
End Ads