x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 22 - CUTARWA

  • 63001 words
  • 66000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 504

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
ke dukanta da muciya"

"Dalla rabu da ni, na gaji da abubuwan da yarinyar nan take yi mini"

"Amma maama bai kamata ki dake ta da muciya ba, idan kuma ki ka ji mata ciwo fa?"

Cikin ko in kula ta ce "Na daki banza"

Tayi maganar tana sake kwaɗawa ummi muciyar iya ƙarfin ta.

"Maama dan Allah ki daina cin zalin anty ummi, wannan CUTARWA! ce, maybe tsautsayi ne ya sanya ta yi miki laifin"

A fusace ta ce "Ni ka ke gayawa ina cin zalinta?" Tayi maganar tana nufo shi.

Babu tsoro ko fargaba ya ce "Idan ba CUTARWA! ba ce dai-dai ne Allah ya sa a yi wa intee ko kausar abun da ki ke yi mata" sak tayi tana kallon Abdul, ba ta taɓa zaton wannan maganar daga bakinsa ba.
Ta ji jikin ta ya yi sanyi, ta jefar da muciyar ta fice.

Ya girgiza kai shi ma ya fita, dan kunyar ummi ma yake ji, bai san me zai ce mata ba, saboda abun da mahaifiyar su take mata.

BAYAN SHEKARU BIYU
***

Ummi na tsaye a gaban mudubin ɗakinta, tana ta aikin taje gashin ta, ta nemi wuri ta zauna tana kallon kanta a mudubi, gashin duk ya rufeta, ta sunkuya tana cire gashin da yake jikin comb ɗin, ta tare shi a gefe sannan ta nannaɗe gashin kanta ta tufke shi.

Ta sanya doguwar rigar shadda brown, ta kawo dogon hijjabi milk ta saka, ta ɗauki niƙabinta ta sanya.

Ta shashshafa turare, tafin hannunta har ɗaukar ido yake yi, saboda tafin hannunta fari ne ƙal, kamar mata jini a jiki, kuma aka ɗora mata jan lalle a kai.

Ta ɗauki ƴar ƙaramar jakarta ta fito, Abdul ya ce "Inyee ka ga amaren sauka"

Kawu yahaya ya dube ta cikin fara'a ya ce "Congratulations dear, Ubangiji Allah ya sanyawa karatunki albarka, ya ƙara hasken makaranta" ta risuna ta ce "Amin kawu, na gode sosai da sosai"

Ya kalli farida da ƴan matanta da suke ta sabgoginsu, kamar ba su san da zaman su a falon ba ya ce "To mu mun tafi wurin saukar"

"Allah ya tsare" ta faɗa a yatsune.

Kawu yahaya yaji babu daɗi, da yaransa ko mutum ɗaya babu wanda yayi saukar nan, idan baya nan sai sun ga dama suke zuwa makaranta, dan kuwa farida wurin koyon kwalliya ma ta sama musu, maimakon zuwa makarantar.

Ummi gaba ɗaya bakinta yaƙi rufuwa, kaf a ƴan saukar ita ce ƙarama, danma tana da jiki ne, dan ko Maryam shekara biyu ta bata, itakaɗai ce mai shekaru sha shida a cikinsu, maryam na da sha takwas.

Aka gabatar da abubuwan da suka kamata, sannan aka fara raba musu alluna.

Ana bata nata ta nufi rumfar iyaye maza, har da gudu, wurin kawu ta ƙarasa ta durƙusa a gabansa tana cewa "Kawu ka ga"

Ya karɓi allon yana murmushi ya shafa kanta ya ce
"Allah ya sanya albarka ummana"

"Amin kawu na gode" tayi maganar cikin tsantsar farinciki.

Abdul ya ce "Rufe bakin mana"

Ta kalleshi ta ce "Ta ina ka san bakina a buɗe yake a cikin niƙab".

"Yadda ki ke magana ne ya sa na gane"

Ta ce "Bari Yaya Abdul, Alqur'ani da daɗi wallahi".

"Wannan gaskiya ne ummana, kalli baƙin ki na waccan rumfar" ummi ta waiwaya ta ɗaga kai.

Wa zata gani? Yaya Magaji da auwwal, har da su Alhassan.

Maimakon ta yi murna sai gabanta ya faɗi, ta kasa magana, dan fatanta Allah ya sa babu Idris suka zo, dan bata ƙaunar ganinsa.

Sunanta aka din ga kira a speaker, ta zo ta karɓi kyautarta ta ɗaliba mai hazaƙa.

A hankali ta tashi ta nufi in da ake kiranta, tafiya take cikin nutsuwa, shugaban makarantar ya ce "Ƙaramar su babbar su, Salma Muhammad Bashir, kun ganta nan duk ita ce ƙarama a ƴan sauka, amma babu ɗalibar da ta kai ta cin maki lokacin screening"

Ummi ta karɓi kyaututtuka daban-daban, na hazaƙa, ladabi da biyayya da sauransu.

Mamin su maryam ummi ta hango, ta tafi wurin da take, dan jan lallen da aka yi mata ma, gidan su maryam ta je, mamin ce ta biya.

Mamin ta rungume ta tana faɗin "Allah yayi albarka ummi, Allah ya sanya wa karatunku albarka"

Ta risuna ta ce "Amin ya Allah"

Sau ɗaya ya ɗaga kai ya kalleta, ya lura da yadda ko iya haɗa ido da mamin ba ta yi, saboda tsananin tarbiyya da girmama manya, ya so ta ɗaga niƙabin ya ga ainihin fuskarta.

Ya dubi Maryam ya ce "Ke ba uban da aka baki? ba na ƙoƙarin, babu na ɗa'ar" yayi maganar yana sake gyara zaman face mask ɗin sa.

Cike da tsiwa Maryam ta ce "Ina ruwanka da ni? Ba a bani ɗin ba sai ka ƙwace allon saukar ma gaba ɗaya, mami ki rabani da shi wallahi, ai da yake ma ba gayyatarka na yi ba, waye ya ce ka zo?"

"Rufen baki kan na ɓarar da ke a wurin nan"

Ummi dai murmushi kawai take yi, duk ta san yayyen Maryam, wannan ne dai bata sani ba, kuma da alama maryam ɗin ta raina shi.

Aka tashi daga filin sauka, su yaya magaji suka nufo su, "Ummi masha Allah, kin ga yadda ki ka girma?" Magaji Yayi maganar yana kallon ta.

Alhassan ya ce "Ummi har kin yi sauka anya ba zuƙu ba ce ba?".

Ummi ta yi murmushi ta ce "Ai makarantar nan ba a saukar zuƙu"

Suka rankaya zuwa gida, suna komawa gida ta tarar da Iya, sai da ta ɗan ci burki, domin kuwa ba ta zaci Iyan za ta zo ba.

Ta ɓoye mamakinta ta ce "Iya sannu da zuwa, dama zaki zo?"

Ta harari ummi ta ce "Eh, da ki ka ce ke ba zaki zo in da nake ba, kar na yanka ki na cinye ko?"

Ummi ta girgiza kai ta ce "A'a makaranta ce take hanani zuwa, ya gida ya kowa da kowa?".

A ciki Iya ta amsa mata da lafiya lau.

Dai-dai gwargwado kawu ya yi wa ummi ƙoƙari, dan naman kasuwa ya sayo fal, ya bata tayi girkin da zata rarrabawa mutane da ƙawayenta.

Ita ummi ma kasancewar ba ta da ƙawaye, sai maƙwabta ta babbawa, sai su Iya da suka zo.

Sam farida ba ta bi ta kan Iya ba, ummi ce take ta ɗawainiya da su, suna ta hirar makaranta da su magaji, sai dai ko da wasa, ba ta nuna musu tana shan wahala a gidan ba ko kaɗan.

Kawu yahaya ya ji daɗin yadda ummi ta samu sakewa yau cikin ƴan uwa, tana hira ba kamar da da kullum a rakuɓe take ba.

Iya kuwa ba dalilin saukar ummi ne ya kawota ba, balli ne ya tashi, Idris ya mayar da hindu tamkar matar da ya aura, tun bata saba ba har suka saba da sheƙe ayarsu.
Kwatsam ciki ya bayyana a jikin hindu, suka rasa yadda za su yi da cikin, har sai da iyayen hindun suka farga.
Dan haka zance ya fasu a gari, sai faɗuwa ta zo dai-dai da zama, domin kuwa iyayen hindu sun ce sai ya auri hindu, shi kuma ya ce ba ya son ta.
Dan kuwa zance ya fara fasuwa, an fara zunɗensu a garin.
Baban hindun kuma ya dage ba za a zubar da ciki ba, sai an haifi wannan ɗa ya riƙe, kuma sai ya aureta.
shiyasa Iya ta lallaɓo wai kawu yahaya ya ɗauke shi ya sama masa sana'a a nan Kano, a mayar da aurensa da ummi!!!

Iya a ɗakin kawu yahaya ta same shi, ta kora masa wannan jawabin.

Yayi ƙuri da ido yana kallon Iya, har ta gama jawabinta.

Kasancewar ummi na wurin, gabanta yayi wata irin mummunar faɗuwa, kawu yahaya ya kalli Iya ya ce "Amincewar ummi zaki nema, ni ba zan yanke mata hukunci ba, abun da take so shi nake so".

"Zancen banza kenan, wane irin sai ta yarda ko ba ta yarda ba? Ba ɗan uwanta bane ba, rufin asirinmu ba nata bane ba, idan shi ma ya baro garin, suka neme shi suka rasa ba shikenan ba, asiri ya rufu, ai rufa masa asiri za ta yi,  ai umarni nake bayarwa ba shawara ba, dauɗar gora ai ciki ka sha ta!"

Ayshercool
08081012143.
WHAT'S APP ONLY PLEASE 🙏

18

Kan ka ce kwabo, hawaye ya wanke wa ummi fuska, har wata irin sheshsheƙar kuka take yi, dan kuwa da ace ta koma gidan Idris, gara a yanke mata hukuncin kisa, dan tana kyautatawa Allah zato a dukkan lamuranta, tayi imanin za ta dace da rahamar sa.

Iya cikin masifa ta ce "To kukan uban me ki ke yi, ba taimaka miki zai yi ba? ke a wannan munin naki uban waye zai aure ki? Kalli fuskarki fa kamar buredi ya ƙone ƙurmus, har wani zaɓi ne da ke? Ke gaki nan ba ke ba mutum ba ke ba aljana ba".

Kawu yahaya ya ce "Iya, lokacin da Allah ya halicci ummi fa, bai yi shawara da kowa ba, balle ace laifinta ne, ko wani abu ne ya sanya ubangiji yin halittarta a haka, halittar ummi hurumin ubangiji ne, dan haka bai kyautu a din ga ci nata fuska ba, kuma wallahi ummi ba ta da muni".

"Ka ga ni kar ka yi mini wa'azi, ai maganar gaskiya ce, tun da Allah ya sa ita ba wata mamora ce da ita ba, balle ace za a samu mai kwasa ai duk sai a manta da abun da ya faru a baya ko? Tun da har da kansa ya ce ta dawo ɗin, sai a ja masa kunne"

Dr. Ya kalli in da ummi ke zaune tana ta sheshsheƙar kuka ya ce "Ummana, jeki ɗaki abunki kin kwaso gajiyar sauka" ummi ta tashi zuciyarta na harbawa da sauri, ta tafi ɗakinta tana kuka, tare da adduo'i kala-kala a zuciyarta, tana fatan Allah ya sa kar kawu ya amince da abun da iya take faɗa. Dan har ta mutu ba za ta manta da azabar da ta sha a gidan idris ba, ko maƙiyinta ba ta fatan yayi rayuwa irin wadda ta yi a gidan idris.

Noor ta bita ɗakin tana kiran sunanta.

Kawu ya kalli Iya ya ce "Iya, ko ummi ta amince ko bata amince ba, ba zan sake bawa Idris ita ba, yaron nan gaba ɗaya jahili ne, wallahi da mutumin kirki ne, idan ta gama sakandare sai a mayar da auren, amma ni ba zan goyi bayan a cuci ɗan wani ba, yadda ya yi wa ƴar mutane ciki, ku je can ku nema masa mafita, dan baban yarinya bai yi laifi ba.
Iya kin manta lokacin da ya din ga terere da ummi, yana tona mata asiri ga larurar da ke damunta? Shi meyasa ba a tursasa shi ya shanye dauɗar gorar ba, sai ummi?
Allah da ya halicceta a haka in dai muna raye, zai bata abokin rayuwa na gari, haka zalika ba zan riƙe ƙato da bai san ciwon kansa kamar idiris ba, can ƙauye ya gagareku balle ni a nan, dan Allah kiyi haƙuri a bar wannan zancen. Ummin ma da kanta ta nuna ba ta so, dan haka dan Allah dan annabi a bar wannan maganar. Kuma ina baku shawarar mayar da idris makaranta kan a kuma bashi wata matar ya aura, dan kuwa jahilci ke ɗawainiya da shi".

Cike da takaici iya ta kalle shi ta ce "Haka ka ce?"

"Ba faɗa na yi dan na ɓata miki rai ba, amma gaskiya ce" Iya ta yi ƙwafa ta ce "Shikenan na tabattar da uwarka ce ba zaka tsallake umarninta ba, kuma da cikin ku ɗaya da baban Idris ba zaka so asirin sa ya tonu ba".

Ya girgiza kai ya ce "Iya ai kin san mu kallon uwa muke yi miki, amma kowa ya ɗebo da zafi bakinsa, kin riga kin sangarta Idris, komai yayi ba zaki bari duniya ta hora shi ba, sai kin kare shi, kema yakamata ki hutawa ranki, ba shikaɗai ne ɗa a dangi ba".

Ba ƙaramin takaici Iya ta kwasa ba, yadda ƙiri-ƙiri yahaya yayi burus da maganarta, ya zaɓi tonuwar asirin su.

Dan haka ta ce masa babu ita babu ummi, tun da haka suka zaɓa, ya ce bakomai, Allhan da ya yi ummin zai kula da ita.

Ko zama ba ta sake yi ba tun da ta tashi, ta ce magaji ya samo musu mota a tasha, kawu yahaya ya biya kuɗin motar, ya basu kuɗin kashewa, suka tafi.

Ummi sai da tayi sujjadar godiya ga Allah, ga saukar Alqur'ani mai girma, ga kuma fasa mayar da aurenta da idris da aka yi.

Duk da kuɗin da yahaya ya bawa Iya sun saka ta ɗan sassauta fushinta, amam ta sha takaicin rashin amincewa ya ɗauki Idiris a mayar da aurensa da ummi, ta din ga zagin ummi tana tsine mata, tamkar ba ita ta haifi baban ummi ba, tare da janyo mata jafa'i kala-kala.

Ko da suka koma gida ta sanarwa Idris da babansa cewa yahaya ya goya wa ummi baya, yaƙi yadda da magabar da ta je masa da ita.

Hankalin Idris ya tashi, dan kuwa baban hindu ɗan bala'i ne, ya ce ba zai yadda ba, ba za a zubar da cikin jikin hindu ba, sai ta haife shi, kuma sai sun karɓa sun riƙe, hindu na da wani yaya da yake soja, kurtu nema a cikin sojojin, amma ya zamewa su Iya barazana, dan kuwa shi ma cewa yayi sai ya saka bomb a gidan su iya, ko ya kama Idris ya harbe shi, tun da aka taɓa ƙanwarsa.

Magaji ya san duk barazana ce, babu ɗaya da zai faru, amma yayi shiru da bakinsa, saboda sun cancanci koma menene ya same su, dan da idris bai taɓa ƴar mutane ba, babu mai ɗaga musu hankali, kuma ya danganta hakan da alhakin ummi

Babu yawon da Iya ba ta yi wurin malamai ba, a kan a rufe bakin baban hindu, da ita kanta hindun da yayanta, amma abu ya ci tura, dan har barzanar kai su gaban hukuma baban hindu yayi idan suka cigaba da takura masa a kan maganar cikin nan, ko kuma ya saka ɗan sa ya ɗauki duk matakin da ya ga dace a kan su.

***

Tafiyar rahama daga gidan dr., Bayan an yi mata aure bata sauya zani da komai ba, daga wahalar da ummi take yi, dan har undeas ɗin su intee ba zasu wanke ba, sai a haɗa mata a kayan wanki, duk ta haɗa ta wanke su.

Sai dai tun ba aje ko ina da tafiyar rahaman ba, ta fara sintirin kawo ƙara wurin kawu yahaya, dan dama mahaifinsu ya rasu, duk wani abu na jin daɗi da ta sanya ran samu a gidan mijin, sai ta ga akasin haka, yana da hali ba bashi da shi ba, amma hatta shinkafa da man da za ta ci, sai ya ƙulla mata, ba yadda da zuwan baƙi gidansa ba, sai an kira shi ya bayar da iznin a zo, idan bai bayar ba kuwa babu mai zuwa.

Kawu yahaya ya kira shi, dan a samu masalaha amma ya nuna shi tsarin gidansa ne a haka, dan haka dole a bar shi yayi yadda yake so.

Haka nan kawu yahaya ya ce sai dai tayi haƙuri, yace shi tsarin gidansa ne a haka.

Tun da shekaru goma sha shida, samari suka fara bin intee, hakan ba ƙaramin farantawa farida yayi ba, tana ganin intee mai goshin arziki ce, shekara goma sha shida, samari sun fara sintiri, dan ma dr. Yana korarsu ya ce yarinyarsa tayi ƙanƙanta sai ta fara karatu idan ma auren zai yi mata.

Lokacin da ummi ta fara period babu wanda ta gayawa, dama ta riga ta san shi tun a karatuttukansu na makarantar islamiyya da na boko ana gaya musu shi, sannan an koyar da su tsabta a lokacin da mutum yake cikin jinin  haili. Dan har wata ƙungiya ta je makarantar su suka wayar musu da kai, a kan jinin haila da tsafta, dan haka babu wanda ta gayawa da ya same ta.
Ta samu kayanta da suka ɗan kwana biyu, ta yayyanka ɗankwalin, take amfani da shi.
Idan kuma Allah ya sa dr. Ya bata kuɗi, babu abun da take fara saya sai pad, tana iya haƙura da kowace irin buƙata ce da ita, ta sai pad ɗin da za ta yi amfani da ita da kuma farin muski.

Sintirin samari zuwa wurin intee, ta din ga wani iyayi tana yauƙi, ya sanya aka fara yi wa ummi gori da habaici, domin kuwa babu wanda ya taɓa zuwa ƙofar gidan ya ce yana sallama da ita, ko a hanya ma babu wanda ya taɓa biyota ya ce ya na so.
Su yi ta yi wa ummi wulaƙanci, wai farar mace Alkyabbar mata, baƙar mace bolar maza.
Kodayake bolar akwai wadda ake iya recycling, wata ta riga ta zama waste gaba ɗaya bata da mamora.
Ko sai sun ga ummi su fara wankan baƙi asarar ruwa, ko yayi ma kamar bai yi ba, blaki kalar dauɗa, su din ga yi suna tuntsura dariya.
Ummi kuwa sai ta yi kamar ba ta ji ba, ta cigaba da sabgoginta, duk da a ƙasan zuciyarta kalaman na su na tasiri a cikin zuciyarta, tana jin babu daɗin cin mutuncin halittar ta da suke yi.

Haka Maryam ma, kasancewar ta kyakykyawa, kullum ba ta da aiki sai bawa ummi labarin saurayinta kaza yayi mata kaza, ko ya bata abu kaza.
Ba maryam kawai ba, ƴan ajinsu ba su da aiki, sai hirar samari, ita kuwa da ta san ba ta da kowa, ta rungumi litattafanta yadda yakamata.

Idan suka so yin dariya kuwa, sai su yi ta zungurar ummi, suna tambayarta wai ita waye nata saurayin, ta gaya musu fari ne ko baƙi, dogo ko siriri.

Kawai sai tayi murmushi ta yi musu shiru, taƙi kula su.

Maryam ce ta fara bata shawara "Ummi, yakamata ko ɗan mayukan nan na zamani ki ɗan din ga shafawa, ko kema kya yi haske, maza ba sa son baƙar mace, ummi kin yi duhu da yawa, duk kwatancen baƙin da za ayi a makarantar nan da ke ake yi, idan ki ka shafa mai ki ka ɗan yi haske, ko yaya zaki samu saurayi, ko zaki ji daɗi duk mu yi aure mu bar ki? Ni fa mami ta ce ina candy aure za ayi mini, na cigaba da karatu a gidan mijina, amma ke kullum kin ƙi wayewa, ga uban hijjaban da ki ke sawa, ba kya kwalliya kamar mu, bayan hijjabi har da wani uban niƙab, to waye zai ce yana son ki, kalli ranar da muka je barkar gidan su Saratu, kowa yayi kwalliya amma ummi ke kin
End Ads