x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 43 - CUTARWA

  • 126001 words
  • 129000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 502

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
na cigaba da kusantowa, ga pressure office, ga ummi gaba ɗaya ta canza ta koma masa kamar wata baƙuwa, taƙi sakin jiki da shi, kamar ma ƙara nesanta kanta da shi take yi.

Yanayin aiki ya ƙara takura raihan, dan haka ko wurin aikin bai fiye samun damar binta ba, ga yawan barin ƙasar da yake yi.

Gefe guda maryam ta saka ummi a gaba da cin mutunci da zagi na cin zarafi kala-kala, ban da saƙonni da kuma barazana da take yi mata, ummi ta rasa in da za ta saka kanta, daga kuka sai addu'a, dan ta rasa yadda za ta yi da al'amarin gaba ɗaya.

Duk da mami ba ta shiga harkarsa, hakan ba ya hana shi zuwa in da take, da la'asar bayan ya dawo daga aiki, yayi niyyar zuwa yau ya je ya ga ummi, ya nufi sashin mami ya je ya tarar da maryam ta zo gidan.

Sanin halinta ya sanya ya tsuke fuska, dan ya san ba wai zuwan Allah da annabi ba ne ta yi shi haka.

"Mami barka da yamma" banza ta yi masa, daga baya kuma ta ce "Kar ka sake zuwa gaishe ni, muddin ba ka aiwatar da umarnin da na baka ba, bana buƙatar ganinka a sashina ma gaba ɗaya"

Maryam ta kalleshi ta ce "Wallaahi ka bayar da maza raihan, me aka yi aka yi ummi? Meye da ita meye abun burgewa a tare da ita? Sannan menene aibun Safiyya, amma na lura kamar ba a hayyacinka ka ke ba, wannan annakiyar baƙin zaka ɗaukko ka kawo mana mugun iri cikin family, wannan yarinyar da mujiya.....

"Dalla malama dakata!" Ya yi wa maryam tsawa.

"Islamiyyar da ki ka yi ba ta amfane ki da komai ba, da baki san daraja karramawar da Ubangiji ya yi wa ɗan Adam ba, ki tsaya iya matsayinki, idan mami tayi matsayinta ne, ke kuwa ko kusa ko a nesa ba ki da alaƙa da aurena, dan haka ki zuba ido idan zaki iya idan ba zaki iya ba ba zan juri cin zarafin matata ba, idan kin yi mata a baya ba ta da bakin ramawa, ni dai-dai nake da ke"

A tare suke shiga karanto "Innalillahi wa Innalillahi raji'un"

Mami ta ce "Au raihan har ta zama matarka ma ashe? Yanzu a gabana ka ke gaya wa ƴar uwarka haka saboda yarinyar da ba ka aureta ba ma? A wayance kana nuna mini babu gudu ba ja da baya kenan sai ka aureta" raihan ya yi shiru yana huci.

Maryam ta ce "Taɓɗijan, akwai ƙura mami, ita ma munafuka na kirata a waya ta ƙi magana, da yake ba ta da gaskiya, munafuka uwar son abun duniya, sumi-sumi da ita garin yayime-yayime na, na yayimo mana masifa"

Cewar ta kira ummi ya fi komai ɗaga masa hankali, ya san dole sai ta yi wa ummi rashin mutunci.

Juyawa yayi da sauri ya fice, ya tafi ɗakinsa ya sauya kaya, ya ɗau babur ɗin sa ya fita.

Gidansu ummi ya tafi, ya yi sa'a security yana nan, ya ce masa ya yi masa sallama da ummi.

Jin ana sallama da ita, ya sanya farida kallon ummi da take ta aiki a falo.

Farida ta kwaɓe baki, haka ma kausar, kausar ta ce "Ohh su mujiya an yi abun arziki, kowane mai tsautsayin ne? Na ga dai wancan tsohon ya ce ya fasa"

Farida ta ce "Oho dai, ni dai ayi a tattara a bar mini gida"

A gaggauce ummi ta gama, ta je ɗakinta ta shirya, ta fito harabar gidan, ya mayar da hankali a kan wayarsa yana dannawa.

Ƙamshin turaren wurinsa da take yi, ya sanya shi ɗagowa, ya zuba mata ido.

Duk ta yi wani iri, alamu sun bayyana ƙarara a cikin damuwa take.

"Sannu da zuwa" ta faɗa a hankali.

"Yauwwa, ya ki ke ya gidan?"

"Lafiya ƙalau" ta amsa tana murza yatsunta.

"Kwana biyu ayyuka sun yi mini yawa sosai ban samu na zo na ganki ba, zuciyata duk a takure"

Ita dai ummi ta yi masa gumm, taƙi magana.

"Yaya ummi" ya kirata da sunan da ya saba a baya.

Ta ɗago ta kalleshi, ya ce "Meyafaru ne? Duk kin canza mini, kamae an canza mini ke, meyafaru ne?"

Kamar ya soso mata in da yake yi mata ƙaiƙayi, ta ce "Dan Allah, ka taimaki rayuwata ka fasa auren nan raihan, wani ƙalubalen ne yake tinkaro ni, kamar ba zan iya ɗauka ba, Astagfirullah idan ka aureni kamar sabon babin ƙaddara zan buɗe, da alama kai kaɗai ka ke so na, gidanku ba zasu karɓe ni a matsayin sirika ba"

Ya jinjina kai ya ce "Eh, thank God tun da ina son ki ni, na san akwai ƙalubale, maryam na san ta kira ki, haka zalika na san mami kin ji abun da ta ce ranar, amma duk ba matsala ba ne ba. Salma ki canza rayuwarki ki koyi tsayawa a kan ra'ayinki da abun da ki ke so duk tsanani duk ƙalubale. Ke kin san ko mata huɗu na ce ina so za a bani a garin nan, amma na tsaya kai da fata na ce sai ke, ni meyasa zaki watsa mini ƙasa a ido? Ummi ba wasa nake yi ba da nake nanata miki ina son ki, ni kaina fa a cikin ƙalubalen nake, amma na ji zan jure saboda ke. Dan Allah ummi kema ki koyi tsayuwa a kan ra'ayinki ba ra'ayin wani ba, ita maryam ɗin waye ya hanata auren wanda take so, sai ke?
Dan Allah ki manta da wani ƙalubale mu tsara rayuwar mu, jarrabawa ba ta ƙarewa a rayuwar mumini.
Ai ki na so na ko? Tayi shiru tare da haɗe rai.

"Ba kya so na saboda na yi miki yarinta ko? Headmaster ki ke so?"

Ta ɗaga kai alamar eh.

"Ko gidan tsohon mijinki ki ke son komawa" yadda ya ga ta razana ne abun ya bashi mamaki.

Ya kawar da zancen ya ce "Ni a wani bugiren ki ka ajiye ni?"

Bai yi tsammanin za ta bashi amsa ba, ya ɗora da cewa "Ƙanin ki ko, wanda ki ka raina da aure?"

Zumɓura baki ta yi, tana juya ƙwayar idonta a hankali.

"Ummi wai meyake damunki ne? To mu yi hira ta yaya da ƙanwa kamar yadda muka saba"

Ta ce "To, ya gida ya office?" murmushin yayi ya ce "Ita ce hirar da ki ka fi so take yi miki daɗi kenan?"

Ta jinjina kai alamar eh.

"Office aiki ya yi yawa ba hutu"

"Ina su Yaya sagir? Kun shirya kuwa?"

Raihan ya ce "Mun shirya, amma ba ya kulani"

"To kai ka din ga kula shi mana ai kai ne ƙarami"

Ya ɗan shafi sajensa ya ce "Gayen nan ɗan wulaƙanci ne fiye da tunaninki, yanzu sai ya yarfa ni, har gara Salim wasu lokutan"

"Ai gani za su yi kamar idan suka sakar maka fuska zaka raina su, ka cigaba da jan su a jiki, kar ka nuna musu ƙyama saboda abun da suke yi watarana sai labari, ka gayyace su cikin ayyukan kamfaninku, ko ba ka sakar musu komai ba, ka ja su a jiki sosai".

Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Gaskiya ne, sai ma kin ga hajiya, ta fi bani tausayi wallahi, tana iya yin ta a kansu, amma kullum kamar ana tura su dawa, amma zan yi ƙoƙari in yi abun da ki ka ce in sha Allah"

"To Allah ya baka iko"

Ya amsa da amin, "Bari na je, zani wani wuri zo mu je ki karɓi saƙon ki"

Ya tashi ya yi gaba ta bi bayansa, a jikin babur ɗin sa suka tsaya, ya kalleta ya ce "Alhaji ya ce na zo na fara gini, a wace unguwar ki ke son mu zauna? Sannan wane irin gida ki ke so, flat ko mai bene?"

"Kowanne ka yi shikenan, Allah ya yassare"

"Salma kenan, haryanzu kina doubting idan ni zan aure ki, kuma ko zan iya riƙe ki, abun da muke shirin yi ba zunubi bane ba, hasali ma yana da asali a addinin musulunci, dan haka ki manta da batun al'ada da surutun mutane kin ji sweetheart"

Ta jinjina masa kai, tana wasa da hannun babur ɗin.

"Salma" ya kira sunanta a hankali, ta ɗaga ido ta kalle shi.

"Ina sonki sosai saboda Allah" tsigar jikinta ta tashi, ta kawar da idonta gefe.

"Ko sau ɗaya ki gaya mini wani abu mai daɗi da zai bani ƙwarin gwiwar cigaba da gwagwarmayar neman aurenki, dan nima ina fuskantar ƙalubale"

Jiki a sanyaye ta ce "Dan Allah raihan ka yi abun da zaka zo ka cutu daga baya, ka ƙara tunani a kai".

"Ni na riga na roƙi Allah a kan lamarin nan, kuma shi so baya bayar da ƙofar tunani, ba abu ne da yake bamu damar yin shawara ba, ki tausaya mini ummi" jikinta yayi sanyi, wani irin tausayin su ya kama ta.

"Ban san me zan ce ba, zan yi mana addu'a iya yi na, Allah ya zaɓa mana abun da ya fi alkhairi"

Ya ce "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum. Gobe in Allah ya kaimu ki yi mini girki dan Allah, zan biyo ta wurinku na ci"

"Me ka ke so" tayi maganar tana murmushi.

"Ke nake so"

Ta yamutsa fuska ta ce "Ina nufin me zaka ci?"

Yayi dariya ya ce "Abinci mana, ko me ki ka dafa zan ci da yardar Allah" yayi maganar yana miƙa mata ledar hannunsa ya ce "Ki koma gida ki huta, duk da ban gama ganinki ba, zamu yi waya, dan Allah kar ki kashe waya kin ji baby"

Ta karɓi ledar ta juya tana murmushi.

Sabuwar waya dalleliya raihan ya gwangwaje ummi da ita, irin wayar da ba ta taɓa zaton zata riƙe irinta ba, bakinta ya ƙi rufuwa sai da ta kira shi ta yi tayi masa godiya, ya ce shi ba godiya yake so ba, kawai ta ce masa tana son sa shi zai sa ya ji daɗi ya tabbatar da ta ji daɗin kyautar da yayi mata.

Aikuwa ta yi gumm, ta kasa magana.

Da kuɗinta tayi cefane, washegari da safe ta sheƙa masa girki, bai kira ta a waya ba, sai fita tayi ta ganshi a waje yana jiranta.

Suna tafe yana yi mata normal hira, tare da nuna mata yadda za ta yi amfani da wayar da ya saya mata.

A mota ya ci abinci, yana ci yana yi mata hira, ta buɗe ruwa ta bashi, ta duba jakarta ta ɗaukko tissue, ta warwro masa ta bashi ya goge hannu.

Yayi murmushi ya ce "Ka ga mace ta gari, ta fara aikinta tun yanzu".

Ta haɗa kan kwanukan ta ta ce masa "Sai anjima, Allah ya kiyaye"

"Amin ya rabb, yakamata mu koma ayi siyayya, mayukan nan kamar sun karɓe ki, na ga kina ta glowing"

Da sauri ta ce "Fari na yi?"

"A'a kyau ki ka ƙara, ban sani ba ko idona ne"

"Kar ka saka mu makara, sai anjima" ta fice daga motar, ya zuba mata ido, har ta shige shagonsu, sannan ya ja motar ya tafi.

Duk wata hanya da mami za ta bi, ta rusa maganar auren raihan, abu ya gagara ta kaɗa ta raya, amma raihan ya dage, ya samu goyon baya ɗari.

Dr. Ya sanar da su kawu Ilyasu, zai karɓi kuɗin auren ummi, dan haka mutum biyu daga cikin su su zo ranar juma'a.
Hatta kayan soye-soye da zai karɓi baƙi, daga waje ya yi order abun sa, dan sai saura ƴan kwanaki, sannan ya gaya wa farida.

Farida ko a jikinta, tana ganinsa yana ta shige da ficensa shikaɗai, ya shirya komai.

Kafin sallar juma'a, su kawu Ilyasu suka zo gidan, bayan sallar juma'a, su Alhaji Tahir suka zo.

Bayan gama tattaunawar da duk yakamata, dr. Ya gabatar da su kawu Ilyasu ga su Alhaji Tahir, tare da gaya musu matakin karatun ummi, tare da tabattar musu da binciken da yayi a kan Raihan, bai samu wata matsala ba.

Alhaji Tahir ya sake gabatar da kansa ga su kawu Ilyasu.

Sannan ya kalli dr. Ya ce "Ban sani ba ko kun yanke kuɗin aurenta da sadakin?"

Dr. Ya ce "A'a, duk abun da Allah ya sa ku ka bayar, zamu karɓa fatanmu ubangiji Allah ya sanya alkhairi"

Alhaji Tahir ya jinjina kai, sannan ciro kuɗi a aljihunsa ya ajiye kuɗi dami guda a tsakiyar falon, ya ce "Ga su nan, dubu ɗari biyar ne, mun saka watanni huɗu idan Allah ya sa zamu gani, amma idan kuna ganin mun saka da yawa kuna iya ragewa".

Dr. Yayi murmushi ya ce "Bamu nemi ƙari ba ma nemi ragi? Allah ya nuna mana"

Kawu Ilyasu ya ce "Amma ranka ya daɗe har naira dubu ɗari biyar, kun kuwa san yarinyar nan bazawara ce? Kuma auren da ba a tsauwwala almubazzaranci ba yafi albarka, bazawara ce ta taɓa aure shekarun baya".

Ayshercool
08081012143

FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya

Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.

And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ayshercool.

PAID ADVERT!.

Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku

Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi
Man garan gashi
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921

*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*

BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.
                          *CUTARWA*




33
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

33

Tsit suka yi gaba ɗaya, suna jiran abun da Alhaji Tahir zai ce, dr. tamkar ya nutse saboda takaicin abun da kawu Ilyasu ya yi.

Alhaji Tahir ya yi murmushi ya ce "Ɗan uwa, ita bazawara ba mutum ba ce ba da ba za a kyautata mata ba? Shi ya ga yana son ta ai, ni mutum ne mai matuƙar ƙaunar ƴaƴana duk abun da suke so, sai ya saɓa wa addini ne zan ce a'a, amma dan bazawara ce ba shi yake nufin a aureta a wulaƙance ba"

Kawu Ilyasu ya ce "Ai dama kar ku ga an rufe ku ne, ku kallemu a matsayin mutanen banza, shiyasa na bayyana komai ko ba gaskiya ba? Kar ku zo a saka yaro yayi ta kashe kuɗi, tun da an ce shi bai taɓa aure ba, kar ya narka dukiya a auren bazawara ya zata budurwa ce, amma dubu ɗari biyar sun yi yawa a kuɗin auren bazawara, kar a cutar da shi"

Alhaji Tahir ya gyara zamansa ya kalli kawu Ilyasu ya ce "Ka san da wa ka ke magana kuwa? Bana alfahari da fariya, amma ko yafi haka ya bayar in kawo zan kawo, ba bazawara ba ko da tsohuwa ce kuwa, ka kuwa san wa ƴar ku zata aura ne? Da alama dr. Shikaɗai yayi binciken nan yakamata ya faɗaɗa muku bayanin waye Muhammad Raihan Tahir, zuriyarmu mun gaji yi wa iyali hidima. Ai ni da raihan ya ce mini mahaifiyar ta ƴar maiduguri ce, na yi zaton zaku yanka mana sadaki ne da sisin gwal, dan an ce auren ƴaƴanku sai jarumi" yayi maganar cikin barkwanci.

Dr. Da kunya kamar ya nutse ya ce "Ai kamar yadda na gaya maka, mu ƴan jigawa ne gagarawa, mahaifiyarta ce ƴar maiduguri"

"Allah sarki, to ace wa sirikata ina nan ina jiran turaren wuta, dan mutanen barno akwai ƙamshi"

Kawu Ilyasu ya ce "Kuma akwai ta'addanci da surkulle ba, ai da yake ma babartata ba wanda ya san a in da take yanzu, shekarun baya aka ce mana ta haukace ma"

Alhaji Tahir ya yi masa banza ya ce "Yanzu kun amince a kan watanni huɗun?"

Dr. Ya ce "Ubangiji Allah ya nuna mana, ya sa zamu gani"

Suka kammala, suka tashi suka tafi, suna tafiya dr. Ya dirar wa Iliyasu da bala'i.

"Wane irin mutum ne kai mara mutunci, ka ke tozarta yarinya a gaban sirikanta, wannan ai ba daidai bane ba"

"A'a yaya yahaya, haka shi ne kankaro mutuncinmu da kimar mu, haka kurum su gano daga baya, su ga mun zalunce su ai gara mu faɗa"

Kawu Saminu ya ce "To yanzu da ka faɗa ɗin me ya sauya?"

Cikin takaici kawu yahaya ya ce "Auren na ta na fari, ba a gabanku Idiris ya saketa ba, ko kusantarta bai taɓa yi ba ya ce saboda larurar da take fama, ya tozarta ta da bakinsa ya faɗa, da na taho da ummi daga gagarawa na kaita asibiti a kan larurar da take damunta, shi ma da bakinta ta tabattar babu mu'amalar aure a tsakanin ta da idiris ba ta da iddarsa.
Idan ka tona wa ummi asiri meye ribar ka? Sigar yadda ka faɗi maganar salon tozarci ne kawai, In da na gode wa Allah mutumin wayayye ne, kuma magana ake ta zunzurutun ilimi, kuma wannan maganar duk mun yi ta da shi, na gaya masa ummi bazawara ce
End Ads