x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 40 - CUTARWA

  • 117001 words
  • 120000 words
  • Out of 215027 words

Category: Tale Stories

Views 526

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
wata.

Kwanaki huɗu rabon raihan da ummi, yayi ƙoƙarin sanya abun da ta gaya masa a matsayin hujjar da za ta rabu da shi, amma shi sam bai ji hakan a matsayin hujja ba, dan damuwa yake ƙara shiga na rashin ta, ya zuba mata ido ya ga iya gudun ruwan ta, ko za ta neme shi, amma ya ji shiru.

Hakan ya sanya ya fara zargin anya ba da gaske take ba ta son sa ba, tun da ta iya gaya masa cewar su rabu, kwanaki huɗu amma ba ta sake nemansa ba, dan haka tsoro ya sake shiga zuciyar sa, ummi ba ta son sa.

Ƙasan zuciyarsa yana mamakin yadda ta ce masa ta taɓa aure, shi ba auren ta ne ya dame shi ba, meya kashe auren? A yadda ummi take har ace namiji ya sake ta?.

Daurewa yayi, ya sake bawa ummi kwana ɗaya, ya zamana kwanaki biyar, amma shiru ba ta neme shi ba.

Kwana na biyar, da yamma ya koma gidansu ummi, sai dai ya kira wayarta amma ba ta shiga.

Yana tsaye sai ga motar dr. Raihan ya risuna ya gaishe shi, dr. Ya amsa masa, yayi parking a waje, ya shiga cikin gida.

Raihan ya dudduba, mai gadin gidan ma baya nan, yayi ta kiran lambarta amma shiru ba ta shiga.

Ya samu wuri ya zauna a ƙofar gidan, yana cigaba da dannan wayarsa.

Dr. Ya sake fitowa,  ya ga raihan, ya kalli raihan ya ce "Yarona wa ka ke nema ne? Ko wurin Abdul ka zo?"

Raihan ya ce "A'a Abba, wurin Ummi na zo"

Dr. Ya ce "Too, ummi kuma lafiya dai ko?"

"Eh lafiya ƙalau, wurinta dai na zo, na kira wayarta ba ta shiga ne"

"Amma wani abun tayi maka ne?"

Ya girgiza kai ya ce "A'a, ba ta yi mini komai ba"

Dr. Ya jinjina kai ya ce "Yaron kirki, ai babu lallai ummi ta tsaya ta saurareka, a yanzu mijin aure ne ya dace ya zo wurinta, ba wanda za a yi soyayya ba kawai, wannan idan ba ku yi sa'anni ba, ba zaka girmeta da yawa ba.
Ka yi haƙuri ka ji ɗana.

Cikin girmamawa raihan ya ce "Abba ummi ta sanni, akwai alaƙa tsakani na da ita, wallahi abba ba ɓata mata lokaci zan yi ba, aurenta zai yi, ina son ta wallahi".

Dr. Yayi shiru yana kallonsa, sannan ya yi murmushi ya ce "Meye matakin karatunka?"

"Na yi degree a ɓangaren Business administration, a ATBU"

"Idan da gaske ka ke zaka aureta, ranar lahadi ka turo mini mahaifinka mu yi magana da shi"

Raihan ya washe baki ya ce "To Abba, in sha Allah zan gaya masa, na gode sosai da sosai"

Dr. Yayi murmushi yayi gaba, a tunaninsa yayi maganin raihan, dan ya zata irin yaran nan ne marasa ji, amma duk da haka nutsuwa da kamalar raihan ɗin.

Raihan tafiya yayi yana murmushi, yana ganin abun kamar a mafarki, yau ya tsinci dami a kala, abun kamar a shirin film, wai ya tura Alhajinsa a nema masa aure? Kai tsaye gida ya tafi.

Sai dai ƙasan zuciyarsa yana tunanin, ummi za ta amince ko kuwa za ta cigaba da gardama ne? Dan ya ga kamar ta raina shi ne a matsayin mijin aure, yayi mata ƙanƙanta.

Yana zuwa ya tafi sashin Alhaji, dan kwanakin nan kusan kullum Alhajin yana gida, ya daki sa'a shikaɗai ya tarar a sashin nasa.

Alhaji Tahir ya gyara zaman tabaran sa, ya ce "Ya aka yi ne? Yanayin farinciki haɗe da damuwa a fuskar babban mutum"

Raihan ya je ya zauna a kusa da shi, ya ce "Kowanne akwai Alhaji"

"Bani labari"

Ya ciro wayarsa, ya nemo hoton ummi da yayi mata, lokacin da suka sayo dogwayen riguna, ya ce "Alhaji ka ga wannan"

Alhaji ya karɓi wayar, ya ƙare wa hoton kallo ya ce "Na gani, meyafaru?"

"Alhaji tana da kyau?"

Ya ce "Masha Allah, very beautiful kuwa, da gani kuma tana da kunya"

"Ita nake son aura Alhaji, zaka nema mini aurenta?"

Alhaji Tahir ya kalli raihan yayi murmushi ya ce "Babban mutum wannan ai matar manyan ce, anya ba ka yi tsaurin ido ba kuwa?"

"A'a Alhaji, ai nima babban mutum ne, dan Allah tayi? Wallahi mutuniyar kirki ce"

Alhaji ya yi shiru ya ce "Ai ni kallon sani nake yi mata ma"

Raihan ya ce "Eh, ƙawar maryam ce, amma ita ba ta girme ni ba, shekrunmu ɗaya da ita, kuma mutuniyar kirki ce ka tambayi Hajiya ma ka ji"

Alhaji Tahir ya dafa kafaɗar raihan ya ce "Easy my dear, in dai kana son ta tayi mini, za a nemi aurenta in dai za a bamu"

Raihan ya washe baki ya ce "Babanta ya ce ranar Sunday wai ka je ku yi magana, gani yake yi kamar ba aurenta zan yi ba, Alhaji tana bani shawarari masu kyau, tana da kirki sosai"

"Allah ya kaimu lahadin, zan je in sha Allah, ko a lokacin suka ce sai a ɗaura, Ubangiji Allah ya sa abokiyar zama ta gari ce"

Raihan ya sosa kai ya ce "Alhaji saura abu ɗaya"

"Ok to ina jinka"

Raihan ya ce "Dan Allah kar ka gaya wa mami sai maganar ta faɗa, ban san yadda za ta karɓi maganar ba.
I really have to marry her, Alhaji rayuwar ummi akwai ƙalubale da ban tausayi, dan Allah ka tsaya mini"

Alhaji Tahir ya jinjina kai ya ce "In dai ni ne ka san baka da matsala da ni, ko tsohuwa ka ce kana so, zan wuce maka gaba in dai tana da tarbiyya, kuma ko a hoto, ni yarinyar ban ga aibunta ba, ko ta girmeka in dai kana son ta shikenan, ai soyayya ba ƙarya ba ce raihan, mune muke barin al'ada na rage mana jin daɗin abun da addini ya halatta mana. Allah ya sanya alkhairi ango"

Raihan ya sunkuyar da kai yana murmushi, wani irin farinciki na ratsa zuciyarsa.

Dr. Ya manta da batun haɗuwarsa da raihan, dan ko ummi ma bai nema da maganar ba, sai dai ya rage ganin gilmawarta ko a gidan, ya bar hakan a wataƙila takurar farida ce ta saka ta ƙara takura kanta.

Washegari raihan ya tafi wurin aikin Ummi, amma manager ya ce "Ai ummi yau kusan kwana uku ba ta zo ba, ni ban sani ba, ba ta da lafiya ne ko ya aka yi ban sani ba, kawai ta ce mini za ta je screening, tun ranar ba ta sake zuwa ba, na zata ma ko ba ta gama ba ne ba".

Raihan ya yi shiru ya ce "kira ta a waya ka ce ko ta dawo aiki, ko zaka koreta".

Manager ya zare ido ya ce "Yayarta ka za a kora? Idan ban koreta ba ni ai yayana ya kore ni, ka san yadda yake yabawa ƙoƙarin ta, da yabawa amanarta"

Raihan ya ce "Dan Allah ka bar wannan maganar, kawai ni dai taimakon da zaka yi mini kenan, ka ce lallai ta dawo aiki.

"Ba zan yi ba, ba kun fi kusa ba"

Raihan ya sassauta murya ya ce "Haba manager, dan Allah ka taimaka Please"

"Da ka ce ba ka ji? Zan yi mata magana, amma ba dan halinka ba, kuma ba zan ce zan wani koreta ba, zan dai yi ƙoƙarin ta dawo ɗin"

Raihan yayi dariya ya ce "Allah ya bar mini manager"

Manager kawai yayi murmushi, ya cigaba da aikin da yakamata ace ummi ce ta yi.

Sai dai manager bai kai ga yin hakan ba, washegari sai ga ummin ta zo aiki, sai dai ta rame sosai, kallo ɗaya zaka yi mata ka san akwai tashin hankali a fuskar ta.

Manager ya kira raihan a waya, ya gaya masa ummi ta zo.

Bai ja dogon lokaci ba, ya daidaici lokacin tashin ta ya kusa, sannan ya tafi.

Ta fito daga wurin aikin, yana nesa kaɗan da ita yana kallonta, tana tafe a hankali kamar mara lafiya.

Zuwa yayi ya sha gabanta da motar, ta tsaya tana kallon motar, ya sauke glass ɗin motar suka haɗa ido, sai da ta ɗan razana, ya buɗe mata motar ba tare da ya ce mata uffan ba.

Jikin ummi ya yi sanyi sosai da ganin raihan, dan ba ta taɓa tsammani ba, kamar mai jin tsoro haka ta ɗosana ta shiga motar.

"Ta tabatta dai ba kya so na ko ummi? Kina iya rabuwa da ni, baki damu da halin da zan shiga ba, kin ce mu rabu, ko nema na baki sake yi ba, rashin muhimmancina har ya kai haka kenan ko Salma?" Ta girgiza masa kai alamar a'a.

"Shikenan, ni gashi na sake biyo ki ai, ranar lahadi Alhaji zai zo wurin dr."

A razane ta kalleshi, tana ƙifta ido.

"Eh, mun haɗu da dr. Shekaranjiya, na zo wurinki kin ƙi ɗaga wayata, mun yi magana ya ce Alhaji ya zo su yi magana"

"Wai da gaske aurata zaka yi?" Tayi maganar cikin matuƙar rauni.

"Gashi ina gaya miki, kin zata da wasa nake yi? Na san wataƙila ba ni ne irin mijin da ki ke so ba, na san zaki ga na yi miki yarinta da yawa, amma har cikin raina nake jin zan iya aurenki na riƙe ki da kulawa da girmamawa".

"Raihan zaka aureni ina bazawara"

"Kar ki sake kawo mini maganar kin taɓa aure, zuciyata zata fashe, ummi kina wasa da son da nake yi miki kina ganin kamar wasa ko? Hubban shadidan na kira shi, ban taɓa jin damuwa da takura a kan son wani abu ba kamar ke, kawai in ganki a kusa da ni, shi zai kawo mini cikakkiyar nutsuwa"

Tayi shiru tana wasa da zoben hannunta.

"Meya rabaku da tsohon mijinki?"

Tayi ajiyar zuciya ta ce "Kakarmu ce ta haɗa auren, ba ya so na, an kai kuɗin aurensa aka fasa, shi ne ya aure ni"

Ya ce "Ya yi wa kansa, ni ina so. Ki saka aurenmu a addu'a salma, in sha Allah zai yi albarka, wata nawa ki ke so a saka na ji kin ce a matse ki ke ko?"

"Ai wannan maganar dr. Ba tawa ba"

Ya ce "Haka ne, nima na matsun ne, in ga kin zama tawa" ummi dai ta yi shiru tana tunanin ko dai ba da gaske raihan yake ba.

"Na ga gidan tv nan sun kira screening, manager ya ce mini kin je, ya ku ka yi da su?"

Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Kyawawa suke so, ba wanda sai an ta saka musu filter ba"

"Kamar yaya kenan?"

"Haka mai wurin ya ce"

Kawai ta ga yayi parking ɗin motar, ya kalli ummi ya ce "Ke kuma ki ka ce masa me?"

Tayi shiru tana kallon sa.

"Magana nake yi miki?"

"Ni ban ce komai ba"

Raihan ya ce "Sai ki ka tsaya kina kuka ko? Gwanar kuka"

Ta ce "A'a ai ban yi kukan ba"

Ya danƙo kunnenta ya ce "Wallahi ummi, duk wanda ya kuma kushe mini ke, ki ka tsaya kina kallonsa, baki ɗau wani mataki ba, sai na huce a kan ki, kamar na fi ki jin takaici idan aka kushe mini ke. Ke kina da baki, amma ba zaki iya magana ba? Tun da ba aikin zai ɗauke ki ba, sai ki wanke shi tas ki bar wurin, atleast ai kya ce masa Allah ya sa kyawawan su durƙusar da tashar, ko ki ce masa ya koma islamiyya a karanta masa Allah ne mahalicci"

Sosai ya riƙe mata kunne, ta kai hannu ta riƙe hannunsa da ya riƙe mata kunnen cikin muryarta mai cike da iyayi da shagwaɓa ta ce "Babba ne fa"

Ya sakar mata kunnen ya ce "Babban banza ba, tun da ba shi da hankali"

Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "My wife"

Ta ce 'Na shiga uku"

"A'a ko ɗaya baki shiga ba, ko ba ni ki ke so ba, dan Allah ki yi haƙuri mu karɓi ƙaddara a yadda ta zo mana, bamu san dalilin da Allah ya sa ya haɗa mu ba, kar taurin kanki yayi delaying zuwan wasu bayin Allah duniya" tayi burus kamar ba da ita yake magana ba.

"A haka kamar saliha, nan kuwa taurin kai a cikin ki kamar me".

Ranar lahadi gaba ɗaya dr. Ya manta da batun zai yi baƙi, dan ya faɗi maganar ne dan ya kori raihan, ummi ma ta kasa zaune ta kasa tsaye, dan raihan ya tabattar mata da ranar lahadin Alhajinsu zai zo.

Ƙarfe sha ɗaya na safe, Abdul ya je ya sanarwa dr. Yayi baƙi.

Ya fita ya ga manyan mutane a manyan motoci, suka gaisa, Alhaji Tahir ya ce "Ka manta zaka yi baƙi ne? Kodayake ƴan boko sai kun bawa mutum lokaci yake zuwa, Tahir ne baban sirikinka Muhammad da ka ce kana son ganina".

Dr. Ya ce "Subhanallah, Allah sarki bisimillah ku shigo"  suka bi bayan dr. Zuwa cikin gida.

Har cikin falo, ya fita da sauri ya samu Abdul ya bashi kuɗi, ya ce ya sayo musu ruwa da lemuka.

Sun daɗe suna hira da Alhaji Tahir, da wasu mutane su biyu ɗaya ƙaninsa ɗaya abokinsa.

Dr. Ya sha mamakin jin waye raihan, tare da yi wa ummi fatan, Allah ya sa ƙarshen wahalarta ne ya zo.

Nan Alhaji Tahir yake gaya wa dr. Tuni ya saka an gama yi masa bincike a kan ummi, kuma ya ji daɗin sakamakon binciken, dan haka ko yanzu aka ce su bayar da kuɗin aure dr. Ya yanka za su biya, idan kuma shima zai yi bincike a kan su tukuna shikenan.

Dr. Ya ce "Eh to, ina son a bani damar binciken tukuna, sannan kamar nan da sati biyu zan yi magana, saboda in kira wasu daga ƴan uwana a karɓi kuɗin auren"

Alhaji Tahir ya ce "Babu laifi, Allah ya kaimu"

Ba tare da wata alkunya ba, suka ci abin da dr. Ya gabatar musu, suka yi masa godiya suka tafi.

Farida ta din ga bin sa tana tambayarsa suwaye wannan baƙin, amma yaƙi gaya mata ko suwaye.

Ummi ta sha mamaki, ba ta zaci da gaske ba, sai da ta ga su Alhaji Tahir sun zo.

Alhaji Tahir ya koma gida, ya kira mami sashinsa, Hajiya na tare da shi, sai dai bai gaya mata ba ita ma, sai da Mami ta zo, ta tarar da su ta wani haɗe rai tana harare-harare.

Alhaji Tahir ya ce "To ke fa abun arzki ya same mu, ban sani ba ko mun yi laifi"

Mami ta ce "Meyafaru?"

"Babban mutum ya zo mini da magana, ya je zance an ritsa shi an ce in je in gabatar da kaina idan da gaske yake, dan yau ma daga can nake da ni da su Alhaji Hamza, nan da sati biyu zamu koma mu kai kuɗin aure"

"Ikon Allah, kuma shi ne ba a saka ni a maganar ba sai yanzu?"

Hajiya ta ce "Masha Allah lallai babban mutum an girma, Ubangiji Allah ya sa abokiyar arziki ce, Alhaji a ina take zan yi shishshigi"

Alhaji Tahir ya ce "Au kema babbar aminiyar ta sa bai gaya miki ba? Wai wata yarinya amm.. ammi ne sunan nata ne ko ummi ne, wai ƙawar maryam ce dai".

Hajiya ta ce "Laaa ko dai Ummi, Ummi dai da suka yi islamiyya tare?"

Ya ce "Yes of course haka ya ce mini"

Cikin tsananin mamaki da takaici mami ta ce "What! Wannan kwazgwamar yarinyar baƙa ƙirin?"

Ayshercool
08081012143



FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya

Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.

And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ayshercool.

PAID ADVERT!.

Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku

Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi
Man garan gashi
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921

*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*

BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.
                         *CUTARWA*


*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)



MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.





31

Har raihan ya bar harabar gidan bayansa ummi take kallo, ko sau ɗaya bai waiwayo ba, ita kuma ba ta daina zubar da hawaye ba, gani take kamar kallon ƙarshe take yi masa, ba zai sake dawowa rayuwarta da sunan yana son ta ba.

Ta tashi jiki babu ƙwari, ta tafi ɗakinta, ta rufe ɗakin ta saka sakata, saboda kar noor ta zo ta isheta da surutu.

Ta zauna ta din ga kuka, ta ma rasa kukan me take yi.

Ta yi shiru tana tuno irin rayuwar auren da ta yi a gidan idiris, ta kasa manta irin wulaƙantar da ta yi a gidan idiris, irin tozarcin da ya yi mata, tamkar ya auri mushen dabba ba ɗan Adam ba, kuma ɗan Adam ɗin ma ƴar uwarsa.

Ta tuna yadda abokansa suke zunɗensa da angon ɗoɗɗoya, ba zata manta tonon asiri da wulaƙantarwar da Idiris yayi mata ba.

'To idan kuma haryanzu ban warke ba fa'?" Ta tambayi kanta.

Ta dafe ƙirjinta
End Ads