x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 26 - AGOLA free pages

  • 75001 words
  • 78000 words
  • Out of 196927 words
Start ads
After Image Ads
"How can I face her?" Daga Jiddah har Sultan sake baki sukayi suna kallon sa speechless Jiddah za tayi magana Sultan yayi saurin taɓa ta da kafa alamar tayi shiru duk suka ɗauke kai su ka cigaba da cin abincin su Sadeeq ya ajiye spoon ɗin hannun sa ya mike ko kallon su be sake yi ba ya wuce upstairs Sultan yace "Ji ɗan rainin hankali, mu ze rainawa wayo? Idan ta ta're ma sai ya dinga zuwa muna koya masa maganar da zai na mata" Jidda ta dinga dariya tace "Wallahi kai mugune" yace "in banda rainin hankali ko yaushe fah idan na masa magana akan ta sai kiji ya wani ce min 'who is she ko waye ita kuma?' imagine fah" sai kuma ya fara dariya yace "I will love to see them as couples wollah, kin san Leena bata son sa ta sha cewa 'sai yana feeling kansa, I hate him' chap akwai aiki a gaba kuwa" Jiddah tace "Believe me ganin idon mu ne Ya Sadeeq ke wannan abun amma wallahi tsab ya san yadda zai canza Leena a lokaci kan Kani". Zuwa yanzu Rayyan ya fara samun salama wa zuciyar sa, dan har sannan baya barin bakin sa shiru ba tare da ambaton Allah ba, duk da hutun da aka basa a wajan aiki amma hakan yaji gwara kawai ya koma bakin aikin sa dan zai fi saurin healing dan zaman sa a gida ban da tunani ba abinda ze haifar masa, ya same su Mummy da ƴan matan ta biyu suna breakfast ya karasa ya gaishe da Mummy da cin abincin kawai take absent-minded ga Niswa ma kamar she's lost in thoughts Nisreen ce kawai ke karyawan ta peacefully, suma duk gaishe sa suka yi ya zauna yana kallon Mummy yace "Mummy baki da lafiya ne?" ta girgiza masa kai sannan ta mike tace "zan tafi office" suka mata Allah kiyaye hanya, Niswa tace "Yaya jikin naka da sauki yanzu ko?" ya gyada mata kai, tayi murmushi ita ma ta mike gudun kar tayi latti. Daddy da ke rike da hannun Ayaan fitowan sa kenan daga parlorn Ammi ya dinga kallon sa kamar wadda aka jefo haka ya shigo gidan yana karasa inda Daddy yake ya durkusa kan kan gwiwowin sa ya rike kafar Daddy yace "Daddy ban san ta ina zan fara maka bayani ba, amma kayi hakuri ka bani Leena karkace zaka raba mi da ita" Daddy kallon sa ya keyi babu kiftawa Hajiya da zata shiga duba Leena ta tsaya kallon Daddy tace "waye kuma wannan?" Still Muhammad yaki sake sa yana ma Daddy magana kar ya raba sa da Leena Hajiya ta sake baki tace "kar dai shi ne yaron da yaso kashe mana 'ya?" Hajiya tayi kicin kicin da ido tana nuna masa yatsa tace "Toh shi be faɗa maka cewa yanzu ta maka nisa bane ? Yanzu maganar da ake ma Leena matar wani ce" a mugun razane Muhammad ya sake Daddy yana kallon Hajiya baki a bude sabar shock, Anty Binta da anty Mairamah da suke jiyo sa ta parlorn duk abin tausayi ya ba su Anty Binta tace "wallahi ba haka nan ya ki ƴar nan ba, makircin wancan matan ne" Muhammad yace "Dan Allah kar ku min, kar ku ce an ɗaura mata aure saboda ba ku son gani na" Hajiya ta hayyako tace "Da karya nake maka ne? Ko kaga kalar wasa a fuska ta?" daga haka ta wuce parlorn Ammi tana banbami, Daddy ya ɗago da Muhammad Rayyan dake tsaye yana jin su ya karasa jikin Motar sa kawai dan shi reaction din Muhammad ne yake basa mamaki Daddy na kallon Rayyan yace "Please Rayyan kayi dropping Ayaan a school" kai kawai ya gƴaɗa masa Daddy yace ma Ayaan "je yayan ka zaiyi dropping ɗinka ko?" ya daga wa Daddy hannu yana masa bye-bye Daddy na rike da hannun Muhammad suka shiga parlorn sa yana kallon sa yace kayi breakfast kafin ka taho?" Muhammad ya girgiza kai yace "Banda appetite, and ina kan drugs ne". Ammi tayi shiru tana kallon Hajiya dake magana Anty Binta tace "wallahi irin haka na faruwa Hajiya, kila an gusar masa da hankalin sa ne sai bayan tayi aure tunanin sa ya dawo" Anty Mairamah tace "ya wuce Uwar Rayyan ɗin ne ta masa, ai shiyasa naji dadi da ba'a ba ɗanta ba dan saf sai ta iya kashe Leena, ina ana gobe biki kama ta mukayi ta zuba mana abu a cikin abinci" Hajiya tayi shiru sai yanzu kuma tunanin hakan yazo mata duba da yadda baki da baki Mummy ke son mata wayo wai kar ta bari ayi auren Leena idan Daddy zai yi garda ma idan tace zata masa baki ai zai hakura Hajiya tayi murmushi tunawa da tayi har abinci Mummy da dinga yi tana kawo mata da kanta tana gaishe ta amma tun daga lokacin ta dena ma shiga sashin ta tana kallon su tace "Toh Allah ya kyauta, duk wanda yayi nagari dan kansa" ta mike zata fita sai kuma ta tsaya tana kallon su tace "kar wanda ya sake ya fadawa Leena da zuwan yaron saboda kar a sake firgita ta dan tun juya hankali na be kwanta ba da Daddare takanas nayi naje a roka mata Allah ta dawo daidai" Ammi na kallon Hajiya da jin tunanin su ya zo daya, su anty Mairamah suka ce in shaa Allah, Ammi ta mike ta leka dakin ta ganin har sannan Leena na bacci ita kuma hakan daɗi ya mata atleast zata samu ta huta. Daddy na kallon Muhammad daya ka ma kansa da hannu bibbiyu ya dafa sa Muhammad ya ɗago amma ya kasa hada ido da Daddy, Daddy yace "baka ce komai ba son" Muhammad da kyar ya iya cewa "Haka ne, ba rabo na bane" Daddy yace "Good, Allah baka wacca ta fi Leena da komai, Allah cire maka son ta, Son." Muhammad sai a wannan ranan ne ya san cewa shi ba ba jarumi bane Daddy da tausayin Muhammad ya gama cika sa yace "Idan kuma kana so, tana da Sisters duk wacca kace kana so a cikin ƴaƴana zan baka Son" Muhammad tunawa da yadda Leena ta taɓa basa labari yadda Mummy da yaranta mata suka sata gaba tun lokacin yaji ya tsane su with passion, yace "Dama da wacca aka bani a gida, nace sai Leena" Daddy na patting bayan sa yace "It's Okay" Daddy ya raka sa har inda drivern Muhammad yayi parking shi ya buɗe masa car door din da kansa ya shiga har sannan Muhammad kana ganin yanayin sa kasan yana cikin damuwa ainun Daddy ya koma cikin gidan sa da tausayin Muhammad, tun daga inda yayi parking yake kallon su, dama ganin Motar a kofar gidan yasa yayi parking gaba da gidan nasu, tun da Daddy ya fito yana rike da hannun sa har ya sa shi a mota be ɗauke idon sa a kansu ba, kallon su yake ba kiftawa har Daddy ya koma cikin gida sannan suma suka bar wajan, be taɓa jin yanayin da yake ciki a yanzu ba, nan da nan idon sa yayi mugun ja, saboda tsab ya gane sa, dan yana yawan ganin a Quarters ɗin su Jiddah and she once told him shine Fiancee din Leena, be san sannan ya kunna motar a mugun speed ba yabar layi. Jidda da ke zaune ita kaɗai a gidan sai cook ɗin su, tana game a wayan ta taga credit alert kuma daga Sadeeq, kiran sa tayi yana daga wa tace "Ya Sadeeq alert ɗin mene?" Murya sa kamar mara lafiya yace "duk abinda ake bukata a kara a kwatinan nan Please ki samu kije mall yanzu duk ki tsiyo" tayi shiru tana mamaki yanzu kuma, murya shi taji yace "Please Jiddah, wani abun nake yanzu ba zan iya zuwa be ne, ko Sultan ki roka ya raka ki" tace "Sultan ai ya tafi aiki dama ni da kaine muke hutu ai ka manta shi a gari yake, it's Okay zamu tafi da mai aiki" yace "thank you, idan kuɗi be isa ba just call me" tace "toh" bayan ya kashe tana mamakin sa, yau kuma?" Daga haka ta mike zuwa sanar da Cook ɗin su ta shirya kafin itama tayi wanka". Daddy da ke kallon Ammi yace su Binta fah yaushe zasu koma?" tace "sun ce sai an kai Leena, saboda jiya Mami ta kira akan Saturday ɗin Leena zata tare inji Sadeeq, nan da sati dai za'a ce" yace "Okay, dama driver zan sa da su din dan Allah su samu su taimaka mana su mayar da kayan Lefen da suka kawo" sai yanzu Ammi ta tuna da maganar Lefe tace "Ai kuwa ya kamata a mayar, toh zan musu magana sai su shirya zuwa gobe" Daddy yace "toh barin leka office sai na dawo". Ammi ta shiga dakin ta taga fitowan Leena kenan daga wanka tana shafa lotion Ammi ta karasa jikin dressing mirror ta dauki comb ta shiga gyarawa Leena gashin ta daya har gitse, bayan ta gama tana kallon 'yarta ta cikin mirror tace "Ma sha Allah, ai hakan kin fi kyau amma kullum baki son kamawa" ta ɓata fuska tace "Toh ai Ammi da zafi ne" Ammi tace "lalaci dai, amma ina zafi anan, haka zaki nayi a gidan miji kai a hargitse" Leena ta kalli Ammi sai kuma tayi frowning face dinta nan take ta tunowa Ammi memories ɗin baya, yadda take mata shagwaɓa da yadda Abban Leena ke biye mata, sak fuskan Leena daya da baban ta, hatta bakin su ɗaya, kawai ta kawar da wannan tunanin, tana kallon Leena tace "kisa kaya barin baki waje idan kika gama zamu yi magana" daga haka ta fita daga dakin after some minutes sai ta kara komawa cikin dakin ta zauna tana facing Leena ta rike hannayen ta tace "Leena ki faɗa min me damuwar ki? har yanzu baki san cewa Allah be ƙaddara Muhammad ba mijin ki bane" ta tsunkuyar da kanta tace "Ammi ai na riga da Nasan haka Nima kai na inason naga na daina tunanin sa ma, kawai dai da ba'a daura min Uncle Sadeeq bane" Ammi na kallon ta still tace "Saboda me? Leena Kiga kaunar da ƴan gidan su suke nuna Miki, tun kafin su san mu, ji yadda suka rike min ke lokacin tafiya na Niger, Leena shine ke zaki ki jinin su? me shi Sadeeq din ya nema ya rasa?" Leena ta sauke kanta kasa tace "Ammi shi fah baya so na, ko da yaushe baya son kula ni, dama Uncle Sultan ne sai Anty Jidda mu ke shiri" Ammi tace "baki fahimce sa bane, ni kuma inaga kamar nature ɗinsa ne haka Leena, da baya son ki ba zai nema a basa ke ba, dan Mami sai da tayi ta roko na akan a daura da Sadeeq dan ta dade da fahimtar yana son ki, kuma da bakin sa ma ya faɗa mata" Leena ta tsaya kallon Ammi jin wai Sadeeq da kansa yace yana son ta. sai kusan karfe biyar Jiddah ta dawo gida likis ita da mai aikin su suna shiga kuma suka ga Sultan har ya dawo daga aiki da alama ya sake wanka fita zai yi ganin su ya sa ya tsaya, Jidda ta buɗe bayan booth din motar mai aiki ta fara kwasa tana kai wa ciki, Sultan ya karasa har inda ta ke yace "daga ina kuma, kayan nan fah?" tace "wallahi Yaya ne fah ya sani wannan aikin, na gama wahala yau nake baka labari" Sultan ya sake baki yana kallon ta sai kuma yayi dariya yace "kin san yanzu haka shine ya dame rayuwa ta wai nazo can gidan nasa, ina wajan aiki ma ya dame rayuwa ta wai anemo masa masu aiki" Jiddah tace "baka ji yadda baya na ke min ba, Allah saboda Leena ce shiyasa na fita" yana kallon ta yace "toh Nima raka ni mana" ta dade kirji tace "ina?" yace "gidan Sadeeq din mana, muje muga kiran menene" tace "Allah kiyaye hanya amma ni na gama wahala ta yanzu" da kyar yayi convincing dinta ta yarda Amma sai da ya jira ta sake wanka taci abincin kafin suka fita, basu suka isa gidan nasa ba sai Magrib har wasu masallatai sun idar, Bayan Sultan yayi parking a kofar gidan suna kan sauka sai ga Sadeeq daga masallaci kusa da su yana tahowa alamar dai anan yayi Magrib, bayan ya karasa inda suke yace "Jiddah kin gama?" tace "eh, amma sai ka biya ni" Sultan yace "Uban me zaka nuna mana kasa muka taho da magrib ɗin nan" ya buɗe gate ɗin gidan ya shiga suma suna biye da shi a baya tun daga bakin gate suke kallon yadda gidan ta sake zama wata sabuwa suna shiga parlorn daga Jiddah har Sultan sake baki su kayi suna kallon sa Jiddah tace "yaushe akayi jere?" yana shafa kansa yace "Ɗazu masu Company suka zo suka yi" Sultan yana ta rike dariyar sa Sadeeq dake kallon Jiddah yace "an sa Everything a gidan, yanzu zaki je ki taho da ita?" Sultan da ya mike zaije yayi alwala ya jiyo da sauri jin furucin Sadeeq suka kalla juna da Jiddah kamar hadin baki suka fashe da dariya Jiddah harda hawaye tace "aina aka taba yin haka?"  Sultan yace "yaushe kuma ka canza ra'ayi, kace shiyasa baka ji zafin girgiza acc dinka ba yau kenan" ko kallon su be sake yi ba, shi da da hali ma yaushe zai kula su ai sai de yaje ya dauko ta ya kawo ta da kansa.


Thank you Noor Imaan
*AGOLA (Behind the palace walls)*



31......
Har suka bar gidan Sadeeq yaki kula Jiddah da Sultan suma ko ta kansa basu bi ba suka kama hanya abin su suka tafi. Jiddah dake zaune gefen Mai tace "Mami kiji min fa an taɓa haka ne, kuma ai ana zuwa godiya toh shi yaje ne" Mami tace "toh in banda abun sa ai wannan ba abun fushi bane ni sai da kaina naje na sanar da Ammin ta yace gobe zata tare, shi kuma sai ya hakura goben kawai tunda suma zasu so ace su ɗan kimtsa tukun, da yamma kuma shi da su Sultan sai suje godiya" sallama suka yi alamar sun dawo daga sallar isha'i ne anan parlorn suka tarar da su bayan sun zauna suka gaishe da Mami, Mami na kallon Sadeeq tace "Ka ce yaushe kake son ta tare?" ya ɗan saci kallon Mami sai kuma ya sauke kai, da ya tuna yaga Muhammad a kofar gidan sai yaji hankalin shi ya tashi yace "Mami yau" Mami ta sake baki tana kallon Sadeeq da shock tace "ban gane yau ba?" Sultan and Jiddah couldn't help but burst out laughing Mami ta musu wani kallo wanda hakan yasa sukayi shiru amma suna kunshe dariyar su Mami na kallon Sadeeq tace "Sadeeq, To 9pm fah yanzu, kuma haka kawai sai aje ace a baka mata, kaje godiyan da ango ke yi ne na al'ada?" sai yanzu shima yaji yayi sounding so dull yace "toh Mami ko gobe da safe" duk mamakin Sadeeq ya cika Mami tace "Toh zan fada musu" daga haka ya mike ko kallon Sultan dake masa magana be kula sa ba ya haura stairs. Muhammad dake zaune duk kallon sa suke cike da tausayi Nimrah tace "Toh Meyasa zasu aura mata wani?" Nawaal tace "Lallai, baki san abin da ciwo bane yanzu kila wani ɗan-uwan ta ne saboda tausayi yace zai aure ta" daga Ummu har Abbah duk sun zauna Lost of thoughts can Ummi tace "kai ma baka jin magana da ka hakura ace ku tafi tare da Uncle dinka atleast su san ba wai ki kayi ba" Muhammad yace "Shi mijin Maman nata ma ya tausaya min" Sai sannan Abbah ya kalle sa yace "i think zaka koma Netherlands kafin kayi healing " Muhammad yayi shiru dan shima yasan idan yayi nisa da gida abin zai zo masa da sauki than yana nan Nawaal tace "Wallahi ai Ummi da kin bari yayi amfani da back to sender din, In shaa Allah, Allah zai saka masa". Bayan Mami ta sanar da Ammi, Ammi ta sanar da su Anty Binta tace "bari nake da kaina na fadawa Hajiya kar sai gobe taji ranta ya ɓaci" daga haka ta wuce sashen Hajiya. Washe gari bayan Leena ta idar da Sallah Ammi ta zauna gefen ta tana kallon ta tace "Leena in shaa Allah, anjima za'a kai ki" Leena tace "Dan Allah ba yanzu ba Ammi " ta rike hannun Ammi cikin lallami, Ammi tace "ba yanda muka iya ne Leena, shi Sadeeq din ne da kansa ya bukata kuma kinga yanzu yafi mu karfi a kan ki" Leena ta fara kuka Ammi ta mike ta fita ta barta a wajan, Anty Binta tayi ta rarrashin Leena da bata baki har nasiha ta mata amma ina Leena gaba daya bata gane kan zancen ta kukan ta kawai take yi. Da yamma Sadeeq da few friends din sa suka shiga gidan su Leena gaisuwan angwaye, bayan sun gaishe da Ammi suka wuce part ɗin Hajiya, Hajiya tayi ta sa musu Albarka tayi wa Sadeeq nasiha mai ratsa jiki kuma ta gwada masa dole sai yayi hakuri da Leena saboda ita yarinya ce, kuma nasihan yayi tasiri akan sa, dan ya ratsa shi, wata cousin ɗin Daddy ne tace saura part ɗin Mummy ganin idanun su yasa Hajiya bata ce komai ba, suka ajiye gift ɗin da suka kawo mata suka wuce part ɗin Mummy, bayan sun shiga suka gaishe ta Mummy na zaune tana girgiza kafa cike da kasaita tace "toh waye angon a cikin ku?" Sadeeq da kansa ke kasa ya daga yana kallon ta hakan abinda tayi wa Leena few years back ke dawo masa yaji ya kagu su bar parlorn wani abokin sa yace "wannan ne" ya karasa maganar yana pointing Sadeeq tace "Oh Ayyah, toh sai dai kayi hakuri da yarinyar fa, kasan de cewa yarinya ce kamar yadda ake cewa a gidan nan komai tayi na
End Ads