uwar karuwai ta dakatar dasu “ ke kadai nace miki ban da ita”, girgiza mata kai ilham ta somayi, tana ‘kara rike hannunta, zasu gudu kamar na d’azu sai ganin uwar karuwai sukai a bakin kofa gadan dagan ta nufosu bayan ta saka lock a d’akin, da Sauri Abla ta kwance karara d’inta itama ta saka mata a jiki , uwar karuwai
Bata san me Abla ta saka mata, ta d’auka kasa ce ta d’an watsa mata, zata cafkosu taji bayanta kamar yana mata ‘Kai’kayi, sosa war da zatayi taji wani wajan ya fara yi mata, ga shi towel ne a jikinta, wani irin azababben ‘kai’kayi jikinta ya somayi mata, sosawa kawai take a hau kace ,zata riko abla towel dinta ya soma kwance wa sai kwanta tayi a kasa duk da girman jikinta, Abla na ganin haka ta kama hannun husna suka fito babban falon gidan, a tsaye suka ga Zinariyya da yar shila rike da katako ko wannansu susar jikinsu suke ta ko ina , gabaki d’aya kitsan attachment din da sukayi saida ya baci a garin susa, yar shila ce ta hango Abla da Sauri ta nuna wa wasu yan mata ita “ gata cab ku kamo ta”, abla na jin hakan tayi ‘ko’karin guduwa da sunzo zasu kamata zata zulle musu, Zinariyya gani take wasa kawai take shiyasa ta saka wa duk Wanda ya kama Abla zata bashi dubu goba, ai kuwa gabaki d’aya ba mazan ba bamatan ba suka rufu zasu kama Abla amma duk da haka kufce musu take , duk Wanda ya kusa kamata karara take fesa masa shima sai ya hau susar jiki, duk da haka wasu daga cikin yan matan basu daddara suka cigaba da bin Abla , itama Abla dataga bazasu ‘kyaleta ba kawai sai ta soma yi musu feshin karara, gabaki d’aya falan sai ya har zuke kowa ne man wajan susa yake , tun tana fesa musu har kararan nata ya ‘kare , sai a lokacin ta zuba musu kyawawan idanuwan masu d’auke da dara daran eye ball kalar ash me duhu kadan, cikin tsakiyarsa kuma sai ya kasance kamar adon black colour , tana juya idanunsa tauwadarta dake cikin idanta me kama da zallan madara fitowa sosai tas. Yadda ta tsaya kallansu suma haka ko wanne ya zuba mata ido cikin jin haushi, banko ‘kofar d’akin uwar karuwai gabaki d’aya kowa ya mayar da hankalinsa kan kofar, Itace kuwa har yanxu sanye da towel dinta ko kunya bataji tafi da d’aukan kirji, hannunta d’aya kuma ta kalmine data ke Susa dashi, idanuwanta bai sauka a ko ina ba sai akan kyakkyawar fuskar Abla, a zuciye ta nunata “ duk Wanda ya kama mun wannan shegiyar yarinyar zan bashi mace d’aya yayi lalata”, mutanan Wajan suna jin Hakan suka soma suwa da kururuwa, husna na ra’be a jikin bango yanda baza a ganta ba ,gadan gadan mutanan falon Suka fara nufo inda Abla take itama tana Jan baya,zata taka step ta sauka ‘kafarta yayi skipping step d’aya take a kan stairs d’in ta soma gangarawa , mutanan falon na ganin haka suka soma sheya, ita kuna Abla tana kai karshen stairs d’in ta buge kafar ta, dan karamin ‘kara ta saki zata mi’ke taji an take mata kafar, cikin azabar data fita farko aka ‘kara take kafar damun karfi,’karar wahala Abla tayi tana d’ago fuskarta, bata gama kallon fuskar wanda ya taka taba taji gigitaccen mari a kumatunta, duk da zafin marin da taji ko gezau batayi ba sai ma kyalli da iya nuwanta suka soma,a karo na biyu ta ‘kara d’ago fuskarta, wacce ta gani ne yasata bin ta da kallon sakanni bata auneba aka fara ihun kiran sunan “ DEBEKA!!DEBEKA!!.wacce aka kira da debeka na kalla, ba’ka kirin ce sosai gashi bata da tsaho ko kadan musamman ‘kibarta d’aya kara munanata, debeka muguwa ce sosai , ta dalilinta uwar karuwai ta hana ayi adunga yi mata sallah a gida musamman Lolita da addinin Abla datafi komai tsana wato musuluncin, shi yasa duk lokacin da take nan Abla ba ‘karamin wahala take sha a wajan taba musamman yadda tafi kowa tsanar Abla. Yanxun ma suna gama kururuwan suna dabeka ita kuma sai faman hura gajeren hancinta take , kamar wata kayan wanki ta dam’ki kan Abla , Allah ya te maketama hijab ne a jikin da ba abunda zai hana d’an kwalinta cirewa. Yadda ta janyo hijabin Abla ne yasa ta fara nishi kad’an dan ba ‘karamin sha’keta yayi ba , haka debeka ta cigaba da jan Abla a kasa har zuwa wani ‘kofa , Abla na ganin kofar ta soma girgiza kanta a tsorace , batayi auneba taji debeka ta jefata cikin dakin ta kulle ta waje , da karfi Abla ta soma bubbuga ‘kofar Sabida duhun wajan ga wani irin wani da matsin ‘beraye da ya ‘kara tsoratata, jikinta ne ya fara rawa ganin duhun daki, da ‘karfi ta soma furta “ duhu !! Ku bud’eni bana so, da duhu, zasu cinye ni!!! Ku bud’eni”, ita kadai sai faman surutai take cikin d’akin da ko hannunka bazaka iya ganiba wai warin kazantar dake tashi cikin wajan .
Cikin mugun tsorace Abla take maganar subud’e ta amma ko mutum d’aya babu a wajan, duk da haka bata gaji ba sabida yadda take a mugun tsorace , da ‘karfi taci gaba da furta “ banasan duhu , please ku bud’e ni , ku bud’eni”, d’an abinda taji ya ta’ba mata ‘kafane yasata sakin ‘kara da karfi ta matsa daga wajan amma duk da hakan bata tsira ba sabida yawo da berayen Wajan keyi da kukansu daya cika mata kunne , ga warin datti dake kokarin sata a mai , cikin ‘kan’kanin lokaci tafita hayyacinta, abin jikin katakon wajan ne ya ta’bata ta ‘kara hargitsewa a rufe ta soma neman haryar da zata fita , jitayi tayi karo da abu zata saki ‘kara cikin ambaton sunan Allah, jelar Beran data daka ne ya sata saki ‘kara bata aure ne ba taji beran ya dafe kafarta , tsalle kawai Abla ta soma tana san cire beran, cikin rashin sani ta daki wani d’an katako a cikinta da mugun ‘karfi take a wajan ta fad’i tana fad’in “ cikina !!! Cikina !! Ku bud’eni please bana san duhu”, tun tanayi da ‘karfinta har muryarta ya soma dusashe wa gabaki d’aya sannu a hankali idanuwanta suka soma rufewa.
IBTISSAM NA KUDINE , Kİ BIYA 500 KIKARANTA SHI HAR KARSHE . 2681892316 Aisha umar zenith bank , sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581
https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA
IBTISSAM
( A heart touching story of love and destiny)
Story & written
By
Mss Lee
PAID BOOK:
Littafin IBTISSAM na kud’ine akan 300 kacal , me ‘bukatar karantawa har ‘karshe zai biya kud’insa ta wannan bankin : 2681892316 Aisha umar, zenith bank , sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581.
___💞💞 Ya Allah,Alhamdulillah for the unlimited blessings that I was unable to thank you for__💞💞
💕__BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM__💕
BOOK 1
( The beginning)
Season__ 7
🍂🍂🍂🍂
🍃🍃🍃🍃🍃
UNITED STATES 🇺🇸
FIFTH AVENUE __!
Bobo yana shiga cikin falon ya tarar da bakowa a ciki, direct d’akin uncle iron man ya nufa, yana shiga ya tarar dashi a zaune kan dadduma hannunsa d’auke da Alkurani mai girma , sallama yayi masa saida ya ga ya amsa masa tukunna ya shigo cikin d’akin, kan dannuman da uncle yake zaune shima a kai ya zauna tare da d’ora hansa a kan kafad’ar uncle din, “ kayi kewar sa kenan”, murmushi bobo yayi duk da ya gane me uncle din yake nufi amma be ce masa komai ba, shima uncle din be sake ce masa wani abuba sai tray d’in da ya nuna masa “ Little yace na tabbata kaci abinci, if not bazai yi bacci ba “, tray d’in bobo ya kalla shima tare da janyoshi “ uncle kaima kasan shiriritan little da yawa yake, ni ya fara samun ciwan kai , and yasan bazan zauna ban ci abincin ba kamar Big boss “, rufe Akur’anin uncle yayi” Little kenan! Yayi missing d’in babban yayansa,and shine auta ka bari duk lokacin da kashirya aure zai dena sa maka ciwon kai,” kallan uncle yayi ya d’auke kansa Sabida maganar auren da yayi , sosai yaci abincin da James suka dafa ya kora fresh juice yana hamdallah, ganin uncle yana ‘ko’karin zama a ‘kasane yasa bobo yayi saurin mi’kewa “ uncle ya kamata ka huta haka , dare nayi ya kamata ka kwanta ka huta”, jinjina masa kai uncle din yayi kafun ya furta” shikenan amma bari naje na ‘kara duba yaran nan”, da Sauri bobo ya girgiza masa kai “ No uncle , bari zanje na duba maka su,kaima kana bu’katar Hutu”, be jira amsar uncle d’insa ba ya zaunar Dashi kan gado kamar Wanda ya samu little , har da lullu’ba masa tattausan blanket d’insa fari me shegen kyau da laushi. Saida bobo ya tabbatar uncle ya kwanta kafun ya fito daga d’akin hannunsa ri’ke da tray abincin da yaci, yana fitowa James dashi da wani soja maisuna Samuel suka ‘karasa inda bobo yake da Sauri suka sara masa zasu Amshi try din hannunsa ya girgiza masu kai , “ u can all go now (zaku iya tafiya yanxu )” , yana kai karshen maganarsa ya ajje tray din akan dinning, ya wuce elevator , duk sai da suka ga wucewarsa babu Wanda ya motsa sai bayan mintu na biyu , cikin Sauri James ya wuce dinning yana ‘kara gayawa .
Bobo kai tsaye d’akinsu Little ya shiga gaba ki d’aya sun kwanta sabida yadda d’akin yayi duhu, light d’in d’akin ya kunna, da sauri ya ‘karasa shigo ciki sabida ganin yadda little yake bacci a zaune , prince kuwa baccinsa yake hankali kwance cikin half gareran wando ko singlet be saka ba , ga Acn d’akin sosai yake fitar da sanyi, gyarawa little kwanciyarsa yayi bayan ya Tottofa masa addua, gadon prince ya nufa shima, 2 fingers dinsa ya had’a ya daddage ya d’akawa prince a damtsen hannunsa, da Sauri ya farka kamar zaiyi kuka ganin Bobo tsaye a kansa yayi saurin kallan jikinsa, bashiri ya nufi d’akin dressing d’in su ya shirya cikin night wears d’insa cikin d’an sosa kai ya furta “ good night yaya bobo”. Kanshi bobo ya d’aga masa kafun ya furta night too , yana kwantawa yaci gaba da baccinsa , girgiza kai kawai bobo yayi saida ya tabbatar they’re all safe sannan ya bar d’akin, duk da dare yayi sai da ya ‘kara tabbatar da lapiyan komai kafun ya nufi bedroom d’insa , shaf shaf wanka yayi ya shirya cikin flannel pajama ash colour , Daidai bakin windows d’akinsa ya tsaya ko alamar gajiya babu a tattare dashi, motocin da su Robbert suna fita ne suka shigo cikin gidan , cikin low speed, direct wajan wani parking spaces suka nufa inda jerun manyan motoci suke , cikin sauri Robbert da captain suka nufi motar bayansu, wasu samari biyu yaransu suka fito dasu waje d’aya sai faman zaginsu yake cikin turanci yake furta “ kasan ko ni wanene da zaku kama ? Dukanku sai kunyi na dama daga rana irin tayau dukan ku sai kun bar aiki har banzan o ganku…” be kai ‘karshen zancan ba Sabida naushin da yaji a both side dinta , cikin azaba ya bud’e baki zaiyi ihu Robert ya fesa masa wani abu me shegen d’aci da yasa ihun guduwa , d’aya guy din kuwa gabaki d’aya a maye yake sai faman tangad’i yake ,duk abunda suke bobo yana kallansu , one of his work phone ya d’auka tare da danna number 1 , cikin ‘kan’kanin lokaci phone work d’insu Robert ya fara aiki ,muryar bobo da suka ji yasa suka ‘kara daidaita da sara masa dan sunsan yana ganinsu “ina cikon na ukun?”, sarawa Robert yayi cikin girmamawa ya furta “ baya town sir “, daga ‘bangaran bobo yana jin hakan ya saki wani simple smile da ya ‘kara masa kyau , kit ya kashe wayar ya nufi bed d’insa.
🍃🍃🍃🍃🍃
THE NEXT DAY
Tun kafin bobo ya fito ko ina na gidan angyarasa cikin zafin nama sabida gabaki d’aya cikin gidan babu mace ko d’aya a gidan koda masu aikine , gabaki d’aya sojojine suke aiki a gidan hatta abinci da gyaran gidan sojojine sukeyi babu single mace a cikin gidan da sunan mai aiki. Kamar yadda suka saba kullum , musulman cikin za a yi sallah tare dasu, ragowar kuma suna kula da tsaran gidan , kamar Robert da kullum in bobo zaiyi sallah shima yana bakin masallacin ri’ke da bindigarsa.
Ana idar da sallah kowa komawa yayi ya shirya cikin kayan training d’insu, sojojin gabaki d’aya dogon wandan sojojine a jikinsu sai singlet da suke sawa sanyin safiya na Busasu amma ko a jikinsu, prince da little ma gabaki d’ayansu yau sun shirya da wuri har sun Riga uncle iron man shiryawa, ‘karfe 8:30am suka gama motsa jikin su, little sai faman duba inda bobo yake amma be gansaba tunbayan idar da sallar asuba, prince kam ko ajikinsa dan yasan inda yake, kai tsaye dinning ya nufa yana jiran uncle da su little.little Kuwa bedroom d’in bobo ya’kara duba wa still baya ciki.”yaya prince ina yaya bobo ? Banganshi ba ?”, banza prince yayi masa tare da danna wani abu kamar bell dake kan dinning da Sauri wasu sojoji sanye da black suit su biyu suka fito atare ko wannansu cikin girmamawa suka sara masa“ serve me “, kawai prince yace musu sabida gabaki d’aya bashi da jumurin yunwa, cikin cika umarninsa suka fara bud’e masa manyan warmer din kan dinning , saida ya za’ba abunda ya keso tukunna suka fara serving d’insa cike da ‘kwarewa, be dad’e da fara cin abincin ba uncle da little suma duk suka ‘karasa , ynxu su james ne suka yi serving d’insu duk yadda akai da little ya Za’bi abunda zaici ‘kin kula kowa yayi , hatta abincin ‘kin ciyayi sai hot coffee da shima ko rabi besha yace ya ‘koshi, gabaki d’aya Prince da uncle kallansa sukai basu ce masa komai ba musamman “ wannan rigimammen yaron yanxu ma wata rigimar kake shiryawa ko, toh wallahi ba ruwana a ciki tsakaninka da yayyunka “ duk cikin zuciyar sa prince yake wannan maganar , shi kuwa uncle murmushi kawai ya saki dan yasan inda rigimarsa ta dosa.mi’kewa little yayi ya nufi wata door , prince zai tsayar dashi uncle ya hanashi .
BOBO
Yana shiga wajan da prince yayi wa la’kabi da “ THE DEATH PRISON” daki daban aka sa samari biyun jiya da’aka d’akko, duk da wannan d’akin da suke ciki yafi na farko amma shi wannan cikin d’akin wasu ‘kofofine a cikinsu har guda hud’u biyu ‘kanana, biyu manya sai wasu ‘katan abu fari da bansan menene aciki ba , d’aya daga cikin samarin ne ya taso azuciye cikin turanci ya soma magana “ kasan wanene ni?Kasan wanene mahaifina ? Me mukai muku zaku zo ku d’akko
mu? “ wani irin kallo bobo ya jefa masa da ya kasa ‘karasa maganganun sa , kallansu bobo yayi d’aya bayan d’aya musamman d’ayan saurayin da ya fi tsorata jikinsa har ya fara karkarwa sabida kallan da bobo yake bunsu dashi,har ya ‘karasa wajan wani table masu d’auke da box’s akai , cikin cool voice ya furta “ yana ina ?”, gudun kar Logan ya tona masu asiri , cikin Sauri Dylan ya furta “ wa kake magana akai ? Mu bamusan komai ba kuma zakuyi danasanin kawo mu nan gabaki d’aya..” be ‘karasa zancansa ba sabida wani irin azaba da yaji a ‘kafarsa , da Sauri ya d’ago kansa cikin zabura ya ja baya ganin bobo tsugunne a gabansa , sai kuma cikin Sauri ya kalli ‘kafarsa , ‘karar azaba ya kuma saki Sabida yadda tools d’in da bobo ya caka masa shiga cikin ‘kafarsa sosai , yanxun ma kallansu ya ‘karayi ganin Logan tun ba ‘a je ko ina ba ya soma fitsari a wando , cikin cool voice bobo ya furta “ my last question! Yana ina?”,cike da tsoro Dylan ya kallo bobo ganin fuskarsa ba fara’a kwata kwata, kafun ya kalli Logan da gabaki d’aya ya rud’e , duk da haka baya tunanin zai fad’i inda yake , saidai kome zasuyi masa saidai suyi masa , Girgiza wa Logan kai yayi alamar karyayi magana , cike da tsoro Logan ya kalli bobo da Robert da yake tsaye bayan bobo da bindiga kafun ya ‘kara kallan Dylan , bai sai lokacin da bakinsa ya furta “ NEW ZEALAND” lallausan murmushi bobo ya saki kafun ya kalli Robert “ a mayar musu da kayansu su saka , and then ka sasu cikin “ THE EVIL ROOM”, da Sauri Logan ya ri’ko kafar bobo hawaye harya fara ‘bata masa fuska “ we’re sorry please! Munsan munyi lefi but a mistake is not a mistake until you repeat that mistake is called a mistake ( kuskure ba kuskure bane har sai ka maimaita wannan kuskuran yake zamowa kuskure )”, yanxu kam ran bobo ya fara ‘baci dukda yadda yake ‘ko’karin controlling kansa , sha’ko wuyan Logan da Dylan yayi a lokaci d’aya ya buga kansu da bango , babu Wanda kansa be fasheba, sai dafe kansu da sukai waje d’aya gabaki d’aya Logan ya gama rud’ewa har hawaye sun fara sakko masa a kumatu, Dylan kuwa gabaki d’aya fuskarsa ja tayi sosai kasancewarsa farin Bature , kallansu bobo yayi har yanxu yana ‘ko’karin controlling kansa , “ kuna kiran abunda kukayi a matsayin kuskure ? Wanne daga ciki ? Dilar kwayar ? Ko kuma raping d’in mata da kuke kuna bugar dasu?” Girgiza masa kai Dylan yayi dan shima ya fara tsorata sosai “ please kayi hakuri ka fad’i ko nawa kake so zamu baka , ka kashe wannan maganar”, kallan baku da hankali bobo yayi musu, tabbas sunyi nisa basa jin kira , be ‘karabi ta kansu ba yabar d’akin duk da ro’kan da Logan yake masa . Suna fitowa cike da girmamawa Robert ya mi’ko masa wata ‘karamar