hannunsa, azabure Prince ya furta “ su wanene suke shirin yin yaki”, be karasa zancan saba yaga bobo tsaye a kansa, ga Adil dake faman kumshe dariyarsa. “Just 5 minutes na baku, if you like ku koma and see”, yana kammala zancansa ya bar dakin, bashiri kuwa sukai brush da Alwala ko wanka basu tsaya yi ba , a ‘kasa suka tarar da bobo da uncle iron man , gabaki d’aya masallacin dake cikin gidan suka nufa, sojojine suma cike a wajan suna jiransu, musulman ciki suka shiga masallaci, ragowar kuma suka fara motsa jiki. Ana idar da sallah kowa ya koma masaukinsa, su Prince ma basu tsaya a falour ba suka nufi d’akunansu , Prince ya zo zai kwanta Adil ya tsayar dashi,”yaya Prince kasan yaya bobo yana jiran muko , wallahi ka koma bacci babu ruwana kasan babu abunda zai hana a nunka maka wani motsa jikin”, yana kammala maganarsa ya shigo toilet, tsaki Prince ya ja kamar yayi kuka , Adil na fitowa shima ya shiga wankan, shaf shaf suka shirya cikin kayan motsa jiki, a tsaye suka tarar da bobo shima da nasa kayan motsa jikin , sa’banin nasu shi kayan motsa jikin sojojine a jikinsa, sakkowa sukayi inda yake kafun su sara masa” Salute”, shima hannunsa daya ya d’aga batare da ya sara musu ba ya furta “salute, kun ‘kara 2 minutes Menene hukuncinku “, gabaki dayansu sakin baki sukayi suna kallansa “ Yaya” eyes dinsa ya zuba musu , gabaki d’aya saurin sunkuyar da kai sukai kamar abun tausayi,girgiza kai kawai yayi “ let’s go” wata iriyar ajiyar zuciya suka sauke gabaki dayan su, cikin d’an gudu gudu suka fara tafiya , suna fitowa harabar gabaki d’aya sojojin suka sara wa Bobo kafun su hada baki wajan furta “Salute” hannu ya daga musu, kafun su Prince su fara motsa jiki , sai da sukayi 2 hours suna motsa jiki kafun su koma part Dinsu.
9:30am James ya serving Dinsu breakfast , Tunda suka fara Breakfast gabaki d’aya babu Wanda yayi magana saida suka kammala.
07041879581
MSS LEE
https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA
IBTISSAM
( Heart touching story of love and destiny)
Story & written
By
Mss Lee 💖
BOOK 1
( The Beginning)
Season _3
3:00am nayi ko munti d’aya be gotaba aka bude kofar shirgin da aka kulle Abla, Zinariyya ce tashigo sai tangad’i take Ganin yanda Abla bata motsine yasa Zinariyya sanar da Uwar karuwai, umarni ta bada Akawo mata ruwa masu sanyi a fridge guda biyar, hakan kuwa akayi cikin d’an karamun roba Zanariyya ta juye ruwan masu bala’in sanyi. Dakin shirgin suka nufa ita da Zinariyya sai wata da ake cewa Yar shila , a yadda zinariyya ta barta a haka sukazo suka sameta, kar’ban ruwan uwar karuwai tayi cikin rashin imani ta juyewa Abla shi a jikinta.A gigice Abla ta farka tana Ambatan sunan Allah , gabaki d’aya jikinta rawa ya d’auka sabida wani irin sanyi dayake ratsa jikinta, kallanta uwar karuwai tayi a wulakance “ ku tashi ku fara aikin da kuka saba dan ba Hutu ne ya dace da kuba, matsiyata kawai”, tana kai karshen zancenta ta kalli ‘Yar shila “ jeki taso mun ragowar tsinannun yaran, lokaci kankani na baku su kammala ayyukansu, idan ba haka ba ku zanesu suji a jikinsu “ tana kai karshen zancanta tayi waje , a duniya idan akwai wacce ‘yar shila ta tsana be wuce Abla ba , shiyasa uwar karuwai na fitowa taja ta kamar kayan wanki , Daidai lokacin da Zinariyya ta fito dasu Anee suma ko wannansu a jike sai rawar sanyi suke . Cikin kuka arwa ta karaso Inda Abla take ,”Abla sanyi nake ji , ga yunwa ina ji, ga bacci da be isar mu, jikina duk ciwo yake mun ga wasu cunnaku dasuka cijeni “, kwallarta Abla tayi saurin gogewa “ wata rana sai labari, kafun su dawo ku tashi muyi aikin mu ko zamu samu in lokacin sallah yayi muyi kafun musamu na abincin, kunsan idan bamu kammala ba, bazasu ta’ba bari muyi sallah ba” gyada mata kai sukayi gabaki d’ayansu,Babban falon da ya baci da kwalaben barasa da abubuwan sigari suka fara gyarawa , gabaki d’aya falon wari yake amma duk da haka sai da suka gyara shi tsaf sai faman haki suke sabida galabaitar da sukayi, d’akuna Biyar da suke jere a kasa ko wannansu ya nufi d’aya da niyar gyarawa, d’akin da Abla ta shiga wani irin amaine ya taso mata sabida kazantar da ta dunga cin karo dashi a dakin, gabaki d’aya d’akin a har gitse yake , da kyar ta Samu ta gyara d’akin kafun ta nufi toilet. Tana shiga aman da take rike wa ne ya kwace mata Sabida karo da ta dungaci dasu condom gawani uban Kazan tar dake cikin nan dakin, da kyar ta samu ta wanke ban dakin, tana fitowa sai da ta jira su Husna suka fito Suma , ko wannan su a waji gace sai faman toshe hanci suke, sama suka nufa shima saida suka gyara falon tass da ya fi na kasa baci kafin su gyara rooms din cikin falon, lokacin da suka gama wani irin juwace ta soma kamasu ga kiran sallah da ake faman yi amma badamar suje suyi.Inda kwanukan wanke wanke suke suka nufa, sosai an ‘bata kwanuka haka suka zauna suka fara wankewa, sai wajan 8:30 na safe suka kammala wanke wanken, Dole su gyara kitchen din gidan ga tsakar wajan da zasu gyara shima , ga lokacin sallah na tafiya, murya a dusha she da ‘kyar take magana ta furta “ Lokacin sallah na tafiya , ya kamata muyi sallah “ a tsorace suka kalleta gabaki d’aya “ Abla kinsan hukuncin da zasuyi mana idan suka san munyi sallah ko”, manyan idanuwanta Abla ta saka musu,” kuna nufin mu zauna karmuyi sallah sabida hukunci “, da Sauri duk suka d’aga mata kai kamun ilham tafurta “ sai muyi sallar daga baya danni tsoron muguntar su zinariya nake “, same Arwa ma abunda ilham ta fada shi ta maimaita, Anee ce ta kalleta “ Abla Nima zanyi sallah , Taho muje “, kallan Husna Abla tayi ko zataje amma ko kallan inda Ablan take batayi ba, a d’arare Suka samu suka fita daga cikin gidan, saida sukai tafiya me Nisan gaske kafun su samu wani masallaci da suka ga butocin ciki da ruwa, Alwala suka samu sukayi kafun Suje bayan masallacin su tayar da sallar su, suna idarwa tsoran hukuncin da za ayi musu ya kamasu. Cikin fargaba suka nufa Gidan, tsallan kwado suka tarar ansaka ilham da arwa , fuskarsu gabaki d’aya ta baci da hawaye, yar shila tana ganin su Abla ta rufe su da duka da wata jungegiyar doruna,kafin suma akasu tsallan kwad’an, tun sunayi da karfin jikinsu har suka somayi a hankali kafun su fadi a kan tiles din suna nun farfashi, yar shila ta daga hannu zata kara zuba musu wani bulalan uwar karuwai ta fito cikin wankanta da kallo d’aya zaka mata kasan cikakkiyar karuwa ce, “ ya isa haka yar shila so kike ki kashe mun kasuwa ne , ga kosai can ko wanne ki basa guda bakwai kafun ku basu wankin da aka had’a kunsan yau akwai casu, ko bara banaso suje yau sabida akwai aiki”tana kammala zancanta tasa kai ta bar gidan, kosan yar shila ta dakko amaimakon ta basu kamar yanda aka umarceta sai ta bawa ko wannansu biyar biyar, tana zuwa kan Abla ta Wulla mata guda uku ba kamar sauran ba, Husna ce kawai babu a cikin falon, ayun wace suka fara cin kosan da ko rabin cikinsu be zoba , banda abla da take bun kosan da kallo, tayi wa kanta alkawari bazata kara cin abinda ya fito ta kazamun hanya ba , shiyasa ta rabawa su arwa kowa daddai, harda murnarsu suka amsa kuwa kafun a tulo musu uban wanki me shegen yawa, basu suka kammala ba sai wajan 2:30, anan ma satar hanya ilham da Abla sukai sukaje sukai sallah suka dawo , a wannan karan Allah ya temakesu ba aga dawowarsu ba, har lokacin su Arwa kuwa basuyi ko sallahr asuba ba duk yadda Abla take musu magana har ta gaji . Wata iriyar masifaffiyar yunwa suke ji , Ga uwar karuwai ta hana su zuwa baran da suke nemo abinci, La’asar nayi Abla takara guduwa wannan karan itama ilham bata bita ba. Tana idar da sallah ta ta’be jikin masallaci ko zata Samu sadaka amma har tagama bulayinta bata samu ko biyar ba , shiyasa ta nufi hanyar komawa gida abunta, tana shiga ta tarar da abunda ya tada mata hankali, da sauri ta karasa Wajan su tana tanbayarsu ina zasuje da wannan shigar, Anee na kuka ta soma magana “ Abla nagaji, bazan iya rayuwar yunwar nan ba, idan na kara awa d’aya banci abinci ba mutuwa zanyi , shiyasa na yadda da bukatar su Zinariyya, Sunce ba sex zasuyi damu ba, wasa ne kawai zasuyi, kuma zasu dunga biyan mu”, A firgice Abla ta saka salati “ Innalillahi wa inna ilaihi raji’un,me kuke kokarin yiwa rayuwar ku,bakusan hakan wata Babbar illace ba arayuwar ku, me zakucewa mahaliccin ku”, a kufule Husna ta kalleta“ Ya isheki haka IBTISSAM, ke komai kinfi kowa sani, ko ca’akai miki mu bamu da addinin ne, kullum mutum zai yi abu sai kin kawo naki, idan muka zauna da yunwa zaki bamu abincin da zamu dunga cine,ko zamu zauna kina hanamu abu yunwa ta kashe mu, na dad’e da fahimtar dama ba san cigaban mu kike ba , in baki sani ba ki sani yau bazan kara zama yunwa ta kashe niba , Nima dole na samu kudi, ga hanyar samun kud’i cikin sau’ki , idan ke bakya san rayuwar ki to mu muna so “ tana gama maganar ta taja dogon tsaki tayi wucewarta, Arwa da Anee ma bin bayanta sukai, ilham ce kadai ta Matso kusa da Abla “ kuncin rayuwar nan ta ishe mu Abla , Bamu da gatan da ya wuce mu samowa kan mu ‘yancin kai, bazan iya rayuwa cikin yunwa ba, duk da bamu dad’e da sanin juna sosai ba amma tabbas ke din Ablan muce me Kaunar mu, kin nuna mana soyayya irin yanda yaya take nuna wa kannanta” itama tana kai karshen zancen ta tabi bayansu Husna , zubewa Abla tayi a kasa tana faman nanata sunayen Allah, babu abunda bakin ta yake furtawa sai “ Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un” wannan masifa har ina,batasan lokacin da wani kukan ba’kin ciki ya kwace mata ba.
✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨✨
UNITED STATES
Zaune Adil yake cikin shigar kayan ball a ‘kayataccen filin ball da yake cikin gidan , ball d’in hannunsa yake ta faman bugawa shikadai, yana cikin bugawa Prince ya karaso inda yake cikin shigar kananan kaya masu shegen tsada, “yaya Prince “cewar Adil, shima Prince gira d’aya ya d’aga wa Adil yana zama gefen sa , cikin rad’a rad’a ya furta “Little Yaushe zamu je siyayyar da mukace zamuje kafun after your graduation “, kallansa little yayi kamar me tunani kafun ya furta “ kasan ko mun tanbayi Big Boss zai ce mu lissafo ko me mike so, amma bazai barmu mufita ba “, gyada masa kai Prince yayi , kafun little ya cigaba “ yaya bobo ma bazai barmu ba , Indai ba wani muhummanci ne da abun ba , shima sai an had’a ka da sojoji sai kace wani ‘barawo”,lallausan gashin kansa Prince ya taba “ Little let’s go to uncle iron man, kasan yaya bobo yanajin maganarsa sosai,kawai yawon 2 hours zamuyi mu dawo”. Mikewa sukai gabaki d’ayansu ba yan Adil ya ajje ball din hannunsa , cikin kayataccen babban falourn su suka nufa kafun su karya kwana Zuwa wata kofa, suna shiga nan ma wani kayataccen falo ne babba a wajan da taya tara kayan more rayuwa a cikinsa , falon ba karamun kyau yayi ba , cikin d’aya daga cikin kujerun falon suka tarar dashi yana karatun jarida , “Assalamu Alaikum “, suka hada baki wajan fada, d’an Dago da fuskarsa yayi kadan kafun ya amsa musu salamar tasu “ oh my boys sai yanxu ake ganin ku ko “, sosa ke ya suka fara yi kamar marasa gaskiya kafun Adil yayi saurin zama kusa dashi “ my iron man , you know I don’t have any one like you ko “, sakin baki Prince yayi a zuciyarsa kuwa yana auna irin ma yau darin yaro da za’a yi meshegen wayo , murmushi iron man ya saki “ daga baya kenan , yanxu kana ganin big boss zaka nuna baka sanni ba”, dan karamun mursushi Adil ya saki “No uncle , you know kaima ina sanka , I don’t have any one like you guys “, girgiza masa kai uncle kawai yayi kafun ya kallesa shida Prince “ tunda naganku ku biyu akwai abunda kuke bukata, just ku fadamun ,if not ku tashi ku bani waje “, suna jin haka suka kalli junansu , kafun ko wannan su ya gyara zama , Prince ne ya soma magana “ uncle please munaso mu d’an fita yin siyayyane , and kasan yaya bobo bazai bari muje ba sai dai yace mu lissafo abinda mukeso “, sai da ya gama sauraransa tsaf bece musu komai ba , ya dakko wata telephone room, number 7 Kawai ya danna, kusan mintuna 2 , “ ina falona , am waiting for you “, yana fadar Hakan ya kashe kiran , ba Prince ba hatta Adil dake zaune kan kujera sai da ya sakko kasa kamar zaiyi kuka ya kalli uncle iron man “ yanxu uncle cin amanar mu zakayi , ai se kace mana baza muje ba , ni wallahi ban shirya yin tsallan kwado ba , “be karasa kalamansa ba yaji saukar muryar bobo “ you are very stupid”, a mugun tsorace Prince da Adil suka mike tsaye , kallan bobo da ke sanye cikin half wando da ya kai masa har gwiba black colour da wata white T-shirt da ya fito da murdaddun muscle dinsa waje , fuska a had’e ba fara’a ya karaso cikin falon,ko kallan inda suke be ‘karayi ba , sai sassauta face din shi da yayi kafun ya furta “ uncle gani”, shima uncle din nuna masa su Adil yayi da ko wannansu ya dukar dakansa kasa ,” they want to go out“ batare da bobo ya kallesu ba ya furta “ su lissafa abunda suke so, captain zai karbo musu” yana fadar hakan ya juya ya bar falon, hawaye ne suka fara sakkowa Adil , gabaki d’aya yaji besan zuwa shopping d’in , tsoran shi d’aya ma kar yaya bobo yayi fushi da su, kallansu uncle iron man yayi “ why the pity face kuma, kuje kuyi masa magana , zai barku “, cikin dan marairaice Prince ya furta “ uncle yanxu muna zuwa Wajan sa idan Bamuyi wasa ba sai mun fito da kunburarrun fuska”kallan baku daddara ba Uncle ya bi Prince dashi , wato ya mayar da bobo boxer kenan , “uhm “ kawai yace tare da mayar da hankalinsa kan jaridarsa. Jan hannun Prince , Adil yayi har suka fito falo babu kowa a ciki sai sanyin Acn da yake busosu, direct inda zai sadasu da bangaran bobo suka nufa , suna isa Daidai part din ko wannansu ya ja burki kowa na kallan dan uwansa akan ya fara yin gama , cikin dan rad’a rad’a Prince ya rad’a wa Adil abu a kunne, gyada masa kansa yayi kafun suyi knocking , kusan tsawan 2 minutes ba a amsa ba , kara knocking din kofar Adil yayi nan ma shiru ba a amsa musu ba , kamar zai yi kuka Adil ya kallin Prince , shima Prince din kallan Adil yayi cikin fuskar tausayi ,”come in “, sukaji muryar bobo , babu Wanda bai saki a jiyar zuciya a cikin su ba , a hankali Adil ya tura kofar falon bobo, ko wanne bakinsu dauke da sallama , a hankali ya amsa musu ba tare da ya kallesu ba ,gabaki dayan su shan Jinin jikinsu sukai , tsugunnawa sukai kasa kowannansu ya rike kunnuwansa “ we’re sorry yaya bobo “, cikin had’e rai yace “ get out “, Adil kamar zaiyi kuka ya kara cewa “ we’re sorry please “, a zafafe bobo ya daka musu tsawa “ I said get out “, ba Adil ba hatta Prince mikewa yayi da Sauri suka nufi hanyar barin part d’in, cikin dan sakin murya bobo ya furta “ come back”, cikin sanyin jiki ko wannan su ya koma inda yake a tsugunne, hannunsa bobo ya miko musu , da Sauri ko wannansu ya rike hannun kafun a hankali su kara furta “ kayi hakuri yaya bobo “, da ido ya kallesu kafun cikin dan sassauta murya ya soma magana “ where are your manners , haka aka koya muku magana “, girgiza masa kai sukayi “ speak “ cewar bobo , “ sorry sir”, Prince be kai karshe ba yaji saukar rankwashi akan sa , da sauri ya dafe wajan yana furta “ ouchhh yaya da zafi”, shima Adil yana cikin kumshe dariyarsa yaji saukar nasa rankwashin, “ naga Alama harynxu baku horuba “ ya nuna Prince “ you bari yayanka ya dawo horon LTG zansa yayi maka “ and you , ya nuna Adil “ baruwana kai dashi”, sassaita muryarsa Adil yayi “ yaya bobo kasan Little dinka yana sanka , please karka fadawa yaya big boss ,munyi alkawari zamu zama Good Samaritan kaji best yayan mu “, sakin baki Prince yayi yana kallan Adil , cikin zuciyarsa yake furta “ wai yarannan shi zasuyi wa bariki, Allah ya dawo da big boss hmmm “, ganin yanda yake kashe masa ido ne shima Prince ya kara da “ yes yaya bobon mu zamu zama Good Samaritan “ Sarai yasan halinsu sun fara saka masa ciwan kai shiyasa ya furta ,” go and get ready captain zai kaiku” kafun ya karasa yana jan kunnansu “ and if you guys misbehave, kunsan sauran “, kallan Dagaske kake Adil ya bishi dashi,