x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 6 - IBTISSAM BOOK 1

  • 15001 words
  • 18000 words
  • Out of 200864 words

Category: Romance Story +18

Views 262

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
amsa maka , Gift d’ina ne fa ,and wannan gift d’in bakamar sauran gift bane wannan har abada kadunga sashi a hannunka “, kallansa prince yayi , shima Adil jinjina masa kai yayi “ dagsk nake yaya prince , babu me irin design d’innan da kaina na bada idea d’in yadda nake so a zanamun lokacin da mukaje Russia , and Duk inda kake a fad’in duniyar nan Indai wannan abun hannun yana hannunka zan iya nemo inda kake , please karka cire kaji”, rungumeshi prince yayi cikin farinciki “ wow wow, gaskiya Little ya girma , yanxu kam na yadda you’re not a baby but you’re still a baby to us”, shima Adil cike da farinciki ya rungume prince “ ina sanka yaya prince d’ina “ , jinjina masa kai shima prince yayi “Nima haka “, saukar muryar uncle sukaji abayansu “ Ni kuma fa “, wajan shi suka ‘karasa shima suka rungumesa “ kai ma muna san ka uncle iron man “, suna raba jikinsu Adil ya d’auko p-cap Green sak irin ta Prince ya mi’kawa uncle tare da ‘karamin box d’in da ya bawa prince “ uncle wannan naka ne “, murmushi Uncle ya saki ,cikin English ya furta “ wani lokaci in kayi abu sai ka tunamun yayanku, sak halinku yazo d’aya , prince kuma sai yayo wasu halayen na bobo” yana bud’e box d’in irin chain d’in prince ne sak me shegen ‘kyal’kyali sabani na uncle wasu ‘kananan Harufane a jiki da aka sa uncle iron man , cikin wani irin salo, p- cap d’in prince yasawa uncle akansa , abun hannun kuma Adil yasa masa “ uncle please karka cire wannan abun, duk lokacin da ka gansa ko bana Wajan zaka tuna dani kaji” gashin kansa uncle ya shafa “ ka fara girma yanxu Little , Allah ya albarkaci rayuwar ku gabaki d’aya “ gabaki d’aya a falon suka zauna Little da prince suna gefe uncle kuma yana tsakiyarsu .


✨✨✨✨✨✨

NIGERIA

ABUJA

ADEMOLA ADETOKUMBO STREET

Karfe 3:30am na safe uwar karuwai ta banko d’akin dasu Abla suke a kwance ita da ilham , ruwan fridge d’i data shigo dashi me shegen sanyi ta watsa musu, a firgice suka farka sabida yanda ruwan sanyin ya sauka a jikinsu ga sanyin asuba daya fara busosu, cikin karkarwa ilham ta kalli uwar karuwai a tsorace , Abla sosai jikinta ya soma karkarwar sanyi, cikin wani irin shegen kallo uwar karuwai tabi kirjin abla da kallo gabaki d’aya hankalinta yana kan ‘kirjin Abla da ruwa ya ta’ba , fahimtar hakan Yasa Abla tayi saurin saka hannunta cikin hijabinta tana adduar neman tsari daga sharrinta ,dogon tsaki uwar karuwai taja “ dan ubanku sai nace muku ku Tashi ku fara aiki? Tsinannun yara da basu san hanyar arziki ba, daka yanxu tsarin aikin ku ya canza , dake da wannan shed’aniyar yarinyar ku zaku dungayin aikin komai da komai na gidan nan tunda kun ‘kibin hanyar arzikin da na saku sannan kullum zaku dinga kawo mun 500 kud’in zaman d’aki , duk ranar da kuka kuskura baku kawo ku d’innan ba ku tabbata ranar sai nayi kud’i daku dan akwai Alhazawa dayawa da suke kwad’ayinku, shegun yara masu kashe wa mutum kasuwa , idan kun gama ke “ ta nuna husna “ ki sameni a d’akina “‘kara kallan ‘kirjin Abla tayi da kallo kamar idanuwanta zasu fad’o ‘kasa kafun ta bar d’akin tana sakin ajiyar zuciya . Hannu ilham ta d’ora aka “nashiga ukuna”, sauke mata hannu Abla tayi, kuka ta fashewa Abla dashi “ na shiga uku Abla , matarnan bata tsoran Allah babu Allah aranta, Kema kinsan duk Wanda takira d’akinta toh ba abun alkairi zatayi dashi ba , Abla ina tsoron matar nan , ki temakamun Abla dan Allah “, idanuwanta da suka fara ‘kan’kancewa kamar zatayi kuka Abla ta lumshe kafun ta rungume ilham “ karki damu ilham, insha Allahu Allah yana tare damu babu abunda suka isa suyi mana , ki share hawayenki da yardar Allah ita bata isa tayi miki komai ba kinji?”, girgiza mata kai ilham tayi zata kuma magana itama Abla tayi saurin dakatar da ita” Karki damu babu abunda zai sameki kin manta kina da Abla “, ajiyar zuciya ilham ta saki “ nagode Abla “ hawa yan idanuwanta abla ta goge mata “ karki damu insha Allah babu abunda zai sameki, har yanxu su Anee basu dawo ba? Allah yasa suna lapiya suma “ hawayenta ilham ta share “ Amin Abla Nima nayi mamaki danaga har yanxu basu dawo ba “, jinjina mata kai Abla tayi kafun ta mi’ke tsaye “ ya kamata mu fara gyaran gidan nan kafun su dawo , ki fara gyara d’akunan ‘kasa ni sai na hau na yi nasa kafun ayi kiran sallahr asuba “, toh kawai ilham tace mata lokacin gabaki d’aya baka jin motsin kowa sai su biyu da suke aiki tun kafin Garin Allah ya waye, Tun wajen 4:00am na asuba suka fara aiki lokacin da kowa yake runtsawa har akai kiran sallah asuba basu gamaba sabida ydda d’akunan suke a har gitse, basu suka kammala ba sai wajan karfe 9:00am, ganin lokacin sallah na kurewa ne yasa sukabar aiki suka shige d’akinsu, saida suka tabbatar sun kulle yadda su Zinariyya bazasu iya bud’esu ba tunda dokar uwar karuwai ne ,duk wacce aka kama tana mata sallah a cikin gida sai tasa Ammata dukan kawo wuka kamar ba musulma ba, suna idar da sallahr azkar d’in safe da maraice sukayi kamar yadda Abla ta saba koya musu, cikin Sauri suka mi’ke zasu fito ilham ta tsayar da Abla , inda ta ajje musu ledar jiya ta bud’e tare da d’akko musu manyan biscuit da zasuci “ Abla wallahi yunwa nake ji ki bari idan munci Abinci sai mu cigaba da aikin”murmushi Abla ta sakar mata “ Tohm kiyi sauri ki kammala kinsan ako da Yaushe zasu iya dawowa”, gyada mata kai ilham tayi kafun ta miko mata ledar biscuit d’in guda d’aya “ da Sauri Abla ta girgiza mata kai “ Azumi nake “, sakin baki ilham tayi, itama Abla manyan idanuwanta ta lumshe mata , gudun karta ‘kara wata maganar yasa tace “kiyi sauri bamu da lokaci”, da Sauri kuwa ilham ta soma cin biscuit d’in, saida ta cinye manyan biscuit d’in kafun ta soma ajiyar zuciya , da sauri kuma ta tattara ledojin biscuit d’in ta Mayar cikin ledar data ‘boye cikin wani fasash shen gini daya lalace. Cikin sand’a suka fito daga d’akin gabaki d’aya ajiyar zuciya suka sauke ganin su Zinariyya basu fito ba, uban kayan wanke wanken da aka ‘bata masu shegen yawa su Abla suka fara had’a ita da ilham, basu suka kammala wanke wanken nan ba sai wajan karfe 12, lokacin da su Zinariyya suka fito kowa yana hamma acikinsu . Kallan su Abla Zinariyya tayi kafun ta ja wani dogon tsaki “ matsiyata kawai “, acikin su babu Wanda ya tanka mata saida suka kammala komai , sai alokacin fargaba ta soma kama su Abla , musamman da ilham ta tuna mata kiran ta da Uwar karuwai take , Jim kad’an Abla tayi kafin ta kalleta cikin ‘kasa ‘kasa da murya “ mu gudu sai mu dawo anjima “ da Sauri ilham ta girgiza mata kai cike da tsoro” a’ah Abla Nidai ina tsoro wallahi”, kama hannunta Abla tayi “ idan bamuyi hakan ba kinsan me zatayi miki idan kika shiga d’akin? Ko kin manta lokacin datasa kawayen ta su danneki tana ‘ko’karin farka miki kaya Allah ya ceceki daga cikin zaluncinta ?” Ajiyar zuciya ilham ta saki, ganin hakan yasa Abla taja hannun ilham Suka gudu, sunzo fita daga gidan Zinariyya ta hangosu, duk yadda taso taresu abun yaci tura saida suka gudu, tsaki zinariyya ta saki tana taunar le’ben kasan bakinta.

✨✨✨✨✨

UNITED STATES

karfe 6:30pm motocin Bobo Suka shigo cikin harabar building d’in gidan ,gabaki d’aya soldiers d’in kowa yashiga taitayinsa , Adil na jin durar motocin ya zabura zai gudu uncle iron man ya mayar dashi kan kujerar da karfi ya dam’ki hannun uncle kuwa , Adaidai side d’in building d’insu motocin nan sukai parking tsawan mintuna biyu da bud’e masa mota da akai kafun ya fito cikin takun manyan sojoji masu ta’kama da izza , yana fito wa daga cikin motar gabaki d’aya sojojin suka sara masa , basu ba hatta wa’yanda suke nesa dashi gaba d’aya kowa sai da ya sara masa , ganin yanda fuskarsa take a had’e ne yasa kowa ‘kara shiga taitayinsa, daga hannunsa na dama wani farin bandage ne daya zagaye tafin hannunsa dashi, a hankali ya soma taku kamar bayasan taka ‘kasa, duk daku d’aya da zaiyi da bugawar zuciyar Adil da gabaki d’aya ya dure, yana zuwa daidai bakin kofar shiga wani green d’in abu ya haska kafun ya fara kiran sunan “Bobo is back”, . Kara damke hannun uncle , Adil yayi gabaki d’aya tausayinsa ne ya kamasu shida prince ganin lokaci d’aya yana neman rikicewa , Bobo na shigowa cikin falon ya tarar dasu su uku a zaune da Sauri ta saka hannunsa me bandage d’in a aljihu, dukda yadda ransa yake a had’e hakan be hana yasassautashi ba , cike da girmamawa ya gaishe da uncle d’insu batare da ya kalli inda prince da Adil suke ba , cikin yar in ina prince ya furta “ welcomed back yaya bobo “, batare da ya kalli inda prince yake ba ya d’an jinjina masa kai, Adil ma kamar zaiyi kuka magana a rarrabe ya furta “Ya..Ya Bo…” be karasa maganar saba ya had’iye halamansa sabida kallan da bobo ya jefa masa kafun ya nufi inda Elevator d’insu yake . Fashewa da kuka Adil yayi ganin Bobo ya sharesa,gabaki d’aya rarrashinsa su uncle suka fara cikin sakin yalwataccen murmushi uncle ya furta “ Banasan wannan kukan , kaje ka basa hakuri kawai”, kallansa Adil yayi “Amma uncle fushi fa yake dani”, girgiza masa kai prince yayi “ kamanta abunda yaya bobo ya koya mana , idan munyi lefi mubada hakuri? Just kaje babu abunda zai maka kaji?”, kallan uncle da prince yayi lokaci d’aya suka d’aga masa kai, da sauri yanufi elevator shima, Daidai part d’in bobo ya tsaya ya’ki shiga, har zai juya sai kuma yasaka turn print d’insa take a Wajan kofar wajan ta bud’e babban falonsa me shegen kyau da ‘kayatuwa ya bayyana , kamshin freshener d’in lavender cedar leaf linen ne ya doki hancinsa, cikin sand’a Adil yasoma tafiya sabida kar aji ‘karar tafiyarsa, babu kowa a falon, kofar da ya gani a bud’e ya nufa bakinsa d’auke da sallama, da Sauri bobo da ke dressing d’in hannunsa yasaka hannun cikin aljihu yana bun fuskar Adil da kallo, sallama yayi Bobo ya amsa masa yana binsa da kallo, a mara rai ce Adil ya furta “ Yaya bobo kayi hakuri kaji?” ‘Dan harararsa bobo yayi ,” ni babu ruwana tunda baka jin magana , idan mesu ya dawo sai kayi masa bayani”, da Sauri Adil ya shigo cikin d’akin “ Dan Allah yaya bobo na, kawai nayi missing d’insane fa , shine naje na kallesu “, tausayin Adil , Bobo yaji ganin yana ‘ko’karin yi masa kuka “ fine , idan ka ‘kara rashin jinka kuma ni babu ruwana, lokacin sallah ya kusa “, ka hakura ? Adil ya tanbaya , gyada masa kai bobo yayi , da Sauri yazo zaiyi hugging d’insa bobo ya dakatar dashi “ idan na fito sai ayi hugging d’in, lokaci yana tafiya”, toh kawai Adil yace masa tare da barin d’akin fuskarsa a washe tunda bobo ya hakura, hannunsa me ciwo bobo ya ciro yana ‘kara bin yankan da kallo, ko da wasa yasan bazai bari Adil yaga wannan ciwanba, shiyasa ya ‘karasa dressing d’insa , kafun ya shirya cikin wasu Lious Vuitton d’in kaya riga da wando, daga jikin rigar akwai tanbarin VL me shegen kyau d’aya ‘karawa farar rigar jikinsa kyau , damtsen hannunsa sosai ya fito cikin farar jigar jikinsa, yalwataccen ba’kin gashin kansa duk ya kwanta masa a ‘keyarsa kasantuwar baya tara gashi sosai akansa . Kiraye kirayen sallar magariba ne yasa ya fito daga d’akinsa, lokacin gaba ki d’aya su Adil suna tsaye suna jiran sa, yana fitowa masallacin gidan suka nufa , kamar ydda suka saba kullum jam’i suke bi tare da musulman sojojin, wa’yanda ba musulmai bane sukuma suna kula da tsaran gidan. ‘Ka ida idan suka shiga sallahr magrib basa fitowa sai anyi sallar isha’i, suna idarwa Bobo tare da wasu sojoji manya manya suka nufi wata hanya , Adil zai bisu uncle iron man da prince suka dakatar dashi, zaiyi magana uncle iron man ya katse shi “ banasan musu Adil, dare nayi lets go “, girgiza masa kai yayi ya rike hannun uncle na hagu, dayan hannunsa kuma prince ya rike masa . Suna shiga prince ya nufi dinning daman bashi da jumurin yunwa , shima Adil dinning d’in suka nufa shida uncle , James ne yafito yayi serving d’insu , ko wannansu favorite food d’in sa yasoma ci, Adil ne kad’ai be soma cin abincin saba , prince ne ya kallesa “ me yasa baka cin abincin ka ?” , spoon d’in sa Adil ya d’auka “ ina jiran yaya bobo ne “, ‘karamun tsaki prince ya saki tare da ci gaba da cin abincin sa, kallan Adil, uncle yayi “ kaci abincin ka , idan ya dawo zan sashi yaci okay?” , kamar wani ‘karamin yaro ya mikawa uncle ‘karamin d’an ya tsansa alamar Alkawari, shima uncle yatsan nashi ya miko masa suka d’aure waje d’aya alamar promised.


A bangaran Bobo wani d’aki suka nufa me duhun gaske , kamar wani ‘karamin kurkuku haka d’akin yake , ga wasu chains da yawa a ciki , ‘kofofi uku ne a cikin d’akin, d’akin tsakiya Robert ya bud’e masa , nan ma wani duhu ne a wajan sai wani d’an haske kad’an daya haska d’akin, wani abu Robert ya danna take haske ya haska cikin d’akin . Wasu samari guda biyu ne a cikin d’akin ko wannensu da kunburarriyar fuska , suna ganin Bobo suka mi’ke tsaye , d’aya daga cikin sune ya kalli bobo murya bata fita sosai ya soma magana “ mun fad’a muku komai da kuke so ku sani , akan me za Kuzo ku kullemu anan “, be ‘karasa maganar saba sabida naushin da captain ya d’auke fuskarsa dashi, ‘kara ya saki sosai tare da dafe bakinsa da Jini ya fara zuba , kujera robert ya ajje wa bobo, yana zama suka koma bayansa shida captain suka tsaya , da hannu yayi wa samarin alama dasu zauna Bashiri suka zauna , cikin kausash shiyar murya bobo ya soma magana “ Tanbaya d’aya , Amsa d’aya , suwanene suke baku umarni akan kwayoyin da aka shigo dasu, matan da aka samu abuge cikin maye and ko waccen su anyi raping d’inta su wanene sukayi musu haka ?” A zabure suka kalli junan su , gabaki d’aya tsoro da tashin hankali ya bayyana akan fuskokinsu, saurin kallan suna suka kafun su had’a bakin wajen furta “ mu babu Wanda ya samu”tsakanin captain da Robert babu Wanda yace musu komai sai ma fita daga Wajan da Robert yayi, Bobo kuwa tun bayan tanbayar da yayi musu be ‘kara d’ago kansa ya kallesu ba sai ma wata tsadaddiyar waya da yake dannawa hankali kwance, mintuna biyu Robert ya dawo cikin d’akin hannunsa d’auke da wani madaidaicin box me fad’in gaske black colour , kallan juna samarin sukai ganin Robert ya ajje Box d’in a gabansu, numbers guda uku ya saka box d’in ya bud’e , a ido mutum sai ya d’auka ba shi da girma , amma daga cikin sa waje ne me steps uku a jiki, ko wanne kuma da wasu ‘kananan makamai a cikin su kamar na operations , Wani ring cutter Robert ya d’auko tare da kama d’an yatsan d’aya daga cikin guys d’in , a tsorace guy d’in ya soma kuka yanaso ya kwaci hannunsa amma Robert ya rike hannun gagam, a daidai d’an yatsan sa ya saka abun fuska a cunkushe ya kalle su, “ 1…, 2….” Wanda aka rike wa d’an yatsane ya kalli d’aya da shima gumi da tsoro ya gama bayyana a fuskarsa amma taurin kai ya hanasu magana , Robert na furta “3”, Ring cutter d’in da yake hannunsa ya danna take a Wajan ‘karamin finger d’in guy ya cire , gigitacciyar ‘karar a zaba ya saki tare da zubewa wajan a sume, d’ayan da ya fara futsari a wando Robert ya kalla , amaimakon d’an yatsan hannunsa shi d’an yatsan ‘kafarsa Robert ya kama , da sauri ya fara girgiza kansa , cikin ‘kin’kina ya soma magana “ Me .. me zakuyi mun, me nayi muku , kuyi hakuri , please kuyi hakuri “ shima Robert be saurare saba ya yanke masa ‘karamin d’an ya tsan ‘kafa, kasan turar da turanci suke maganar yasa guy d’in sakin ihu shikansa be san me yake furtawa ba sabida azabar da ya ratsa masa ‘kafa “ Wayyo d’an yatsana, zafi, kuyi hakuri , na fad’amuku babu abunda muka sani , Wayyo , Wayyo ‘kafata “, d’an d’ago da fuskarsa bobo yayi kadan tare da kallan Robert, da Sauri Robert ya kalli guy d’in , finger dinsa yasaka guda d’aya alamar yayi masa shiru , da Sauri kuwa ya kama bakinsa ya ri’ke sai faman zazzare ido yake, Wanda ya suma Robert ya kalla kafin ya d’auko wani ‘karamin robber , me cike da gishiri da wasu abubuwa a ciki, d’an kad’an ya dauka ya barbad’awa mutumin cike da mugunta, azabure kuwa ya farka sabida rad’ad’in azabar da ya fi na d’azu zafi har cikin kwanyar kansa , kamar wani ‘karamin yaro ya fashe musu da kuka , kallan da Robert yayi masa ne yasa cikin sauri shima ya kama bakinsa yana nishi azaba, wani fingers d’insa Robert ya kama da niyar yankewa yasaki bakin nasa , cikin kuka ya furta “ ku tsaya zanyi magana , kuyi hakuri zanyi magana , zanyi magana “, shima d’ayan cikin kuka yadunga
End Ads