x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 23 - IBTISSAM BOOK 1

  • 66001 words
  • 69000 words
  • Out of 200864 words

Category: Romance Story +18

Views 264

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
big boss ne ya soma kad’awa har yanxu yana bin uncle da kallo amma bakinsa yayi masa nauyin da ko harshensa bayajin zai iya d’agawa , yadda bobo yaga reaction din big boss ne yasa yayi saurin dakatar da maganar “ uncle please…” cewar bobo duk da shima yana kokarin controlling kansane sabida ran big boss da yaga ya soma ‘baci, a zuciye big boss ya d’auke eyes dinsa daga kansu ya lumshe idanuwansa yana sosa girarsa guda d’aya me tsaga da ‘karamin d’an ya tsansa, da ido bobo ya nuna musu dinning alamar su d’auko abincin sa Dan ko giyar wake suka sha yadda suka ga ransa ya ‘baci idan wani yace zai kaimasa abu zai iya balla mutum a wajan , a hankali su Prince suka cika gaban wani center me fad’i sosai da abinci kala kala gwanin burgewa har suka gama be bud’e eyes dinsa ya kallesu ba duk da motsinsu da yake ji cikin kunnuwansa , cikin kujerar gefansa little ya zauna a hankali ya furta “ yaya yunwa nake ji”, a hankali ya soma bud’e eyes dinsa kallo d’aya yayiwa little kafun ya d’auke eyes dinsa yana zama sosai abincin ya kalla da kansa kafun ya kalli little , inda suke bobo ya nufa da kansa yayi serving d’insu sabida yasan kalan abunda kowa yake iyaci , da ido big boss ya kalli little sannan ya kalli food din da bobo yayi serving dinsa, yagane me yayan nasa yake nufi shiyasa ya janyo abincin nasa ya faraci a tsanake banda big boss da ko farar ta’ba abincin beyi ba , barin wajan bobo yayi tsawan 5 minutes ya fito hannunsa d’auke da wani unique small cup me d’auke da coffee sai faman turiri yake , har inda big boss yake ya karasa tare da mi’ka masa , a hankali big boss ya saka dausasan hannunsa kamar ba soja ba ya karbi cup din yana lumshe wa bobo ido, bobo ya gane me hakan yake nufi shiyasa ya d’anyi knodding kansa kadan , cikin wani irin unique way ya fara sipping coffee dinsa , little ma sosai ya zage yaji abincinsa ganin yadda big boss yake shan coffee ya tabbata yana gama sha zaici abincin ko kad’an ne , hakan kuwa a kayi Belgian waffles kawai yayi cutting kad’an ya soma ci kamar bayasan taunawa, a nutse yake cin abincin hankali kwance , had’ad’d’iyar wayarsa da ta ‘kara Haske alamar kira na uku kenan Sabida yadda take haske tun d’azu cikin silent amma mamallakin wayar ko gefen inda take be kalla ba , wayar bobo ce ta soma ringing , ganin wanda yake kiran sa ne yasa ya kalli big boss yana sakin wani dan iskan murmushi har Wayan yayi cutting a karo na biyu da aka ‘kara kiransa sai da ta kuşa tsinkewa ne yayi picking , banji me aka ce masa ba sai “okay “ da bobo yace yana nufar big boss da phone din hannunsa , tun kafin ya karasa big boss ya dakatar dashi da narkakkun eyes dinsa , a hankali ya zari tissue ya goge bakinsa , phone dinsa kawai ya d’auka ya nufi hanyar fita, sai da Suka ga fitarsa alokacin prince suka saki ajiyar zuciya , murmushi bobo Kawai ya saki daman yasan za’arina ba kowa ne yake kiran big boss ba face president danshi big boss idan rashin mutumcin sa yana kuşa baya ragowa kowa , mayar da wayar sa kunne bobo yayi shima yana bun bayan big boss da ya fita sai a lokacin prince ya Samu damar tanbayar uncle abunda yake san tanbaya “ uncle Menene ma’anar Bubububu d’innan da kake yawan fad’awa yaya and naga duk lokacin da ka fad’a Ransa sai ya baci”, a jiyar zuciya uncle ya saki yana kallan prince da little da suke jiran amsarsa “ it’s a long time Name! Labarine da ayanxu bakwa bukatar sani har sai lokacin da yayi niyyar kusani”. Amma uncle please kadena fad’a masa to tunda ransa zai ‘baci ni bana jin dad’i Allah , shima fa yaya bobo ranshi ya ‘baci amma yake ‘boye “ murmushi me Sauti uncle ya saki batare da ya basa amsa ba suka canza hirarsu zuwa wata davan.


***********
****************
*WASHINGTON*
Abunda ya faru tun lokacin da Alice taji labarin dawowar big boss ta tayarwa da her excellency hankali a kan tanaso ta gansa ko kuma ita ta hau jirgi ta koma New York a yau d’innan , babu yadda her excellency batayi ba itama amma ta tubure har bara zana tasoma yi wa mahaifiyar tata akan zata kashe kanta idan ba ayi mata yadda take so ba , shiyasa kai tsaye her excellency ta kira his excellency, sosai hankalinsa ya Tashi sabida furucin da Alice tayi , da kansa ya d’auki phone ya kira number big amma ba’a picking, sai da yajera masa calls har uku amma babu Wanda big boss ya d’auka shiyasa president ya mayar da called din zuwa bobo amma duk da haka ko uffan be ce musu ba , Alice da ke tsaye a kansa sosai ta kara dubur burce musu har da d’auko wata knife din fruit akan idan bataji muryar saba zata kashe kanta , da ‘kyar suka lallashe ta akan zasu je New York suyi 2 week sabida ita , da wannan dalilin suka shawo kanta da kyar, Alice kuwa sabida murna ko ta kan iyayenta bata sake bi ba ta nufi d’akin ta kamar wata zautacciya ta dunga burkita gabaki d’aya kadan da ko hour 1 ba’ai da gyara su ba , duk da haka gabaki d’aya kayan basu yi mata ba shiyasa ta fara shirin shopping din kayan da zatayi amfani dasu a New York dan acewarta sai ta auri big boss zata dawo Washington tare dashi, su rayu su biyunsu babu takurawa. Alice gabaki d’aya soyayyar big boss ta rufe mata ido shiyasa kome yayi yake burgeta take karajin soyayyarsa cikin ranta .

✨✨✨✨✨✨✨

KANO

9:20pm zaune Eshaal take cikin d’akinta tana duba books dinta duk da basu koma school ba amma hakan ya sabar mata jiki lokaci zuwa lokaci tana ‘kara bitar karatun makarantarta dan sosai take da ‘ko’kari duk da baby itama ba kauwan lasa bace wajan karatu amma rabi da kwata wasa ta saka a gaba , a ya tsine baby ta kalleta tana bin books din ta da kallo “ munafuka wai ke me kokari sai muga uban da za a nuna mana, idan kinga dama kizo dady na kiranki idan kin ga dama kuma ki zauna kinga tafiya ta,” ta karasa tana ja mata tsoki, saida zuciyar Eshaal ya buga lokacin da baby tace mata dady na kiransu tasan tabbas ba alkairi bane may be sunje sun had’a ta fad’a dashi kamar yadda suka saba ne , da Sauri ta d’auki hijab dinta ta d’ora kan kayan baccin jikinta kar baby ta ‘kara kad’ar lefin da bata aikata ba , aikuwa tana shigowa falon da sallama kallan da momy da dad suka soma binta da shine yasa tasha jinin jikinta, a ra’be ta zauna a ‘kasa tana kallan mahaifinta da ko kusa bayaso ya kalli face dinta kamar zatayi kuka ta furta “ Dady gani” a zujiye dad ya kalleta cikin ‘kyama “ saunawa zan fad’a miki idan na Kara Jin kallan dad dinnan a bakinki sai na farfasa miki baki, kije kısa mu wani uban dai naki amma ba ni ba , ni yata d’aya na sani a duniya kuma ita ce baby” sosai baby taji dadin maganar dad shiyasa ta kyal’kyale da dariya , hawayen da Suke ‘ko’karin zubomata Eshaal tayi saurin had’iye kayanta “ muna fuka ba , gabaki d’aya Zubin uwarta ne da ita to Menene baza tayi va ? Shegiya da wani hasken ta sai kace ungulu, Allah yasa ba wani ‘katan kike bawa jikin kiba sabida ni gabaki d’aya ban yadda dake ba , “ fashewa da kuka kawai Eshaal tayi dan ta rasa bakın magana sabida irin cin mutumcin da momy suke mata a kullum a guje ta koma d’akinta ko taka kıran da Dady yake mata bata juyo ba sabida kukan da taji yazo mata , babu Wanda ya damu da reaction din Eshaal suka ci gaba da hirarsu.

*****************
🍃🍃🍃🍃🍃
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

ABUJA
Har ‘karfe shida lokacin da Abla ta dawo babu Wanda ya tanka mata ko yace mata wani abu, abun mamaki yau ko mutanan da ake tarawa gabaki d’ayansu uwar karuwai ta sallamesu sabida plan din da binta ta had’a daman tun asali ba zuwa tayi dan tayi bariki kawai ba , asalin abunda ya kawota ta samu yarinyar da zata siyar ta samu manyan makudan kudi , shine dalilin zuwan ta gidan uwar karuwai, shiyasa tun lokacin da taga Abla tasan ba ‘kananan kudi zata samu ba idan ta tafi da ita , binta shagala irin mutanan nanne masu shegen gaggawa da sun samu wata dama burinsu kawai suyi abun cikin kankanin lokaci karya wuce su shiyasa tun lokacin da ta ga Abla zuciyar ta soma kwad’ai tuwar tayi abunda zatayi cikin kankanin lokaci . Yadda Abla taga su zinariya na binta da kallo duk inda ta motsane yasa zuciyata wası wası ga wani bugawa da taji zuciyarta na mata lokaci guda , tana shiga cikin d’akin ta tarar da Husna zaune akan katifa hannunta d’auke da dan’kareriyar iPhone tana latsawa, tana ganin Abla ta ta’be bakinta , hanyar toilet ta nufa Allah ya temaketa bata shiga cikin toilet dinba sukaci karo da Arwa Itama zata fito Daga toilet, ajiyar zuciya Abla ta saki , itama Arwa murmushi ta sakar mata tana bata hanya “ Abla sannu da zuwa “, kanta Kawai Abla ta d’aga masa Sabida sarawa da kanta yake mata , ga ciwan mara da take ji kad’an kad’an daman hakan ce ke faruwa da ita duk lokacin da zata sake wani period din sai ta dad’e tana ciwan mara kafun Jini ya zo mata shiyasa komai a hankali take yinsa yau, alwalar sallahr magrib tayi tana fitowa ta tarar da Abla a tsaye tana jiran ta, a tare suka kabbara sallar su lokacin har husna ta bar musu d’akin , ganin kamar damuwa tattare da arwan yasa Abla tanbayarta “ meke damunki ne arwa naga duk damuwa tattare da ke ?” Ajiyar zuciya Arwa ta saki “ Abla Nima bansan me ke damu na ba , haka kawai yau naji zuciya ta na bugawa kamar wani abu na shirin faruwa da mu , a duk lokacin da zuciya tayi irin wannan bugawar sai naga abunda nake ji kamar zai zama gaskiya , kamar ana shirin rabamu ne “, murmushin ya’ke Abla ta sakar mata , itama tun safe take jin bugun zuciyarta ya canza amma bata yadda da hakan ba ta kawar da zancan “ karki damu Arwa insha Allah babu abunda zai same mu kinji? Ki dunga addua aduk lokacin da zuciyarki ta buga miki ko ta raya miki wani abun, ba lallene ya zama gaskiya ba kinji?” Insha Allah Abla , gabaki d’aya hira kadan suka ta’ba a tsakaninsu sabida yadda kowa baya cikin mood dinsa kowa da abunda yake sa’kawa, har zasu kwanta zinariya. Tashigo d’akin tana kallan Arwa a yatsıne “ ba’anan zaki kwana ba , a d’aya store din zaki kwana sabida akwai masu kwana a d’akin, da Sauri Arwa ta kalli Abla, itama Ablan batace mata komai ba sai d’aga mata kanta da tayi kad’an , jiki a sanyaye Arwa ta bar dakin , itama Abla tajimatana jiran ganin wa’yanda zasu shigo amma har wajan 10 babu Wanda ya shigo d’akin , sosai hakan ya bata mamaki ga tsoron data faraji dad’inta d’aya ma akwai hasken fitila, tun tana jira taga ko su Anee zasu shigo ko Arwa har bacci ya fara fusgarta, amma duk da hakan bata kwantaba sai da bacci yaci karfinta.

2:00am wasu ba’ka’ken motoci suka shigo layin gidan uwar karuwai sabida ganin a lokacin ne kowa yake runtsa wa , wasu ba’kya’kyan maza ne a cikin motar ko wannansu fuskarsa a rufe take ga wata shegiyar binduga datake hannunsu , d’aya daga cikin su ne yayi dialing wata number , ringing biyu aka d’auka kamar daman jiran kiran ake , cikin hausarsa da bata fitowa alamar ba cikakken bahaushe bane ya furta “ madam we Dey here ooo”, banji me aka ce masa ba sai kalmar “ shikenan muna jiranki yanxu “, ya karasa yana kashe kiran wayar .
Su Binta shagala ne tsaye a falo da ita dasu uwar karuwai, wannan karan harda su zinariyya da yaran binta shagala rike da bag d’inta , plan din yadda zasu shiga ciki suke tattauna har yanxu , mutane hudu binta shagala ta nuna, debeka , Zinariyya , yar shila sai wata yarinyar ta guda d’aya , a hankali suka had’a group din yadda zasu shiga cikin falourn , saida suka gama tsare tsarensu tukunna suka nufi hanyar d’akin da Abla take , Aushe wannan ne dalilin da yasa aka raba musu wajan kwana ita da Arwa sannan aka hana kowa kwana da ita . Allah sarki Arwa tunda ta shiga store din da aka mayar da ita ta kasa zaune ta kasa tsaye haka kawai ta kasa samun natsuwar zuciya , ga baki d’aya bacci ya ‘kaurace mata , da ta zauna zatayi Tunani babu abunda yake fad’o mata cikin zuciya sai tunanin Ablanta. Motsin da taji tun d’azu ne yasa ta saka kanta wajan kofa ko zata ji meke faruwa , ganin bata jin komai ne har zata hakura zuciyarta ta kasa ha’kura da hakan , Daidai lokacin da su uwar karuwai suka nufi d’akin da Abla take , sosai tsoro ya kama Arwa ganinsu da yawa cikin sand’a tabi bayansu gudun karsu ganta .
Allah sarki lokacin da suka shiga cikin d’akin bacci me d’an nauyine ya d’auke Abla shiyasa ko motsin bud’e ’kofar da akai bataji ba sai d’an motsawa da tayi kad’an, powder din hannun ta binta shagala ta bud’e tana faman sakin wani shegen murmushin mugunta, dukda karfinsa haka ta zubasa a hannuta, tana nunawa su zinariyya su rike mata Abla , d’an ta’bata da yarinyar binta tayi ne yasa Abla farka wa , yadda ta gansu a kantane yasa ta ware manya manya eyes d’inta akan su muryarta har rawa yake wajan furta “ me.. me zakuyi mun?… me .. kuke shirin yi”da Sauri suka fara kici niyar ri’keta amma tana kwace hannunta, Ance sarkin yawa yafi sarkin karfi gabaki d’ayansu sai da Suka jigatu amma duk da hakan basu riketan da suke soba shiyasa binta shagala ta shaka mata powder din hannunta da yasata sakin azababbiyar ‘kara Daidai lokacin da Arwa tazo bakin kofar dakin, ihun Abla da tajine yasa tayi saurin bud’e d’akin gabaki d’aya binta suka soma binta da kallo cikin Tashin hankali, itama hakance ta kasance da ita cikin tashin hankali take bunsu da Kallo kafun ta d’ora eyes dinta kan Abla da fuskarta tayi mugunja ga kanta da take faman duka , kamar mahaukaciya ta d’ago da eyes dinta muryarta kamar zata shid’e da kyar take iya bude baki “ ki.. gudu.. zasu kasheki… ki gudu” Abla ta karasa a zabure sabida yadda suka shaka mata powder din me shegen yaji, cikin tsananin Tashin hankali binta shagala tasaka su zinariyya su kama Arwa , da Sauri Arwa ta soma ja baya tana girgiza kai , bazata iya tafiya ta bar Abla a cikin wannan yanayin ba , amma yadda taga Abla tafice daga cikin hanyacinta ne ya kara tsoratata gadan gadan su zinariya sukayi kanta , itama da Sauri ta bude kofar fita ta saka gudu ko kallan gabanta batayi waya binta shagala tayi wa mutanan dazu akan su kamo Arwa, Allah ya temaketa sai data fata wuce su tukunna suka ankara da ita da gudu suka biyota amma babu damar suyi harbi sabida kar asamu matsala , gudu sosai Arwa take ko kallan gabanta batayi haka suma kattın mazan nan suke binta abaya , da iya karfinta take gudu kafarta ko takalmi babu duk ya fashe sabida lungun da ta ke shiga , tana gudu tana wai wayan mazan da suke binta a baya bata san lokacin da ta fito babban titi ba Adaidai lokacin da wasu manyan ba’ka’ken mota kusan guda 7 suka shararo kantitin driver da yake driving din motar baisan lokacin da Arwa ta shigo gabansa ba shiyasa be aune ba yabi ta kanta saida tayi sama kafin ta fad’o kasa babu alamar rai tattare da ita , lokacin da karatan nan suka ga abunda ya faru shiyasa suka dakata tare da kiran binta shagala suka shaida mata yarinyar da suka bi ta mutu, suna barin wajan driver da yake tu’ki yayi saurin Jan burki hakan ya bawa ragowar motocin Jan burki suma , da Sauri y karasa wata mota dake bayansa ya shaida musu abunda ke faruwa , wata katuwar sojece da take driving mota ta biyu tayi saurin fitowa ta d’auki Arwa tasaka ta cikin motar su ka bar layin gabaki d’aya.
Allah sarki Abla gabaki d’aya tafi ce daga hayyacin sai faman zabura take lokacin da binta shagala take fad’awa uwar karuwai mutuwan Arwa wani irin zaburowa da Abla tayi saida ta firgita su, yadda ta sha’ke Wuyan binta sai ya raza mutum , a haukace take furta “ sai na kasheku, sai na kashe ku kamar yadda kuka kashe mun ita,sai na kasheku…” bata karasa ba Sabida kwalbar da zinariya ta buga mata akai da Sauri abla ta dafe da take ganin yadda ta fara ganin su dishi dishi, cikin rawar jiki da muryar ta furta “ nayi muku alkawari wannan shine kisa mafi muni da zaku karayi a rayuwarku idan har ina raye sai kunyi mutuwa irin mutuwar da Baku tava tsammani, sai na zama sanadiyyar rugujewar gabaki d’aya farin cikin ku wannan alkawari ne na d’auka “, tana kaiwa ‘karshe ta zube kasa ita ma babu alamar rai a tattare da ita, cikin zufa uwar karuwai
End Ads