x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 7 - IBTISSAM BOOK 1

  • 18001 words
  • 21000 words
  • Out of 200864 words

Category: Romance Story +18

Views 261

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
d’aga kansa, “susu uku ne “, ya furta da’kyar Sabida zafin da ‘kafarsa ke masa , shima Wanda aka yanke wa hannun jinjina kansa yayi alamar Hakane da ‘kyar ya furta “ Logan ,Dylan,Nicholas” a zuciye Robert ya ‘kara rike d’an yatsan sa daniyar yankewa guy d’in yayi saurin furta “ Logan d’an Governor, Dylan dan mayor , and … and “, ya kasa ‘karasa cikon na ukun, Gigitaccen mari Robert ya d’aukesu dashi , lokaci d’aya suka furta “Nicholas d’an matemakin shugaban kasa “, sai kuma suka fashe da kuka suna bawa bobo hakuri. Wayarsa Bobo ya mayar cikin aljihu , kafin ya mi’ke tsaye , ko kallan inda suke beyi ba ya bar d’akin su captain suna Goya masa baya har zuwa building d’insu, yana shiga captain da Robert suma suka shiga cikin wata ba’kar mota, bayansu kuma wata mota ce guda biyu da manyan karatan sojoji a ciki sukabar gidan.

ME BU’KATAR KARANTA IBTISSAM ZAI BIYA KU’DINSA TA WANNAN ASUSUN 2681892316
AISHA UMAR , ZENITH BANK , sai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581. https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA


IBTISSAM
( A heart touching story of love and destiny)

Story & written
By
Mss Lee

PAID BOOK:

littafin Ibtissam na kudine akan 300kacal , me bukatar ya karanta har karshe zai tuntubeni ta wannan number tawa :07041879581.
Ko aturo kud’in book d’in ta wannan bank d’in: 2681892316 Aisha umar, sai a turo mun shedar biya ta wannan number : 07041879581.


Dedicated this page to the family of MAI INGILA , love you all my parents 💞💞💞.

💞💞__ All praises are due to ALLAH, the forgiver and concealer of fault, The Guide to Repentance, The one who responds to duas . AMEEN 💞💞__.


__BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM __


BOOK 1
( The beginning)

Season__6

ABUJA STATE , NIGERIA .

Tun da su Abla suka fita daga gidan karuwai gabaki d’aya barin unguwar sukai, sai da sukayi tafiya mai Nisan gaske kafin su zauna suna hutawa , ilham kamar zatayi kuka ta kalli Abla “ yanxu Abla kinga abunda muka jawo wa kanmu yanxu me kwatar mu a wajan shegiyar matar nan sai Allah”, kallanta Abla tayi kafin ta d’an ta’be bakinta ,cikin siririyar muryarta me dad’in gaske kamar sarewa ta furta “kome zatayi mana Allah na tare da mu ai , kuma ita bata isa tayi mana abunda Allah be nufa ba, kwanda ma ki kwantar da hankalinki”hawayenta ilham ta share duk da har yanxu akwai tsoro a tattare da ita “ Abla kinsan halin matar nan, bata da Imani musamman ke da ta fi nuna wa tsana , bansan Sharrin da Zinariyya zataje ta ‘kulla mana ba , shegiya kanta kamar duwawun d’an buri”, dungure mata kai Abla tayi “ kar ki wani dasu, ki tashi muyi abunda zamuyi kafin yamma tayi, kina an fara kiran sallar‘karfe d’aya , damun idar zan ‘karasa layin Formella , idan basu gama karatun suba , na saurara ko Allah zaisa na iya wasu abubuwan, Allah yasa Malam Sule yayi Tarihi yau”, shiru ilham tayi kamar me tunani kafin tace “ Amma Abla me zai hana yau muje kasuwar kubwa ,ko kayan kwanjone mu siya”mi’kewa tsaye Abla tayi , tare da zubawa ilham manyan dara daran milky eyes d’inta, dukda tana cikin halin rayuwa amma babu abunda ya canza daga kyawunsu,daga cikin idanuwanta har wasu d’igon tauwadane guda biyu da suke ‘kara Haska kyawun kwayar idanuwanta da suke zara Zara kamar wacce ta saka kwalli a cikin idan, ‘kara ‘kiftasu tayi akan ilham take a Wajan dogan gashin idanunta suka soma sama da ‘kasa ba’ka’kye Wuluk kamar tasaka , cikin daddad’ar muryarta me kama da na sarewa ta cewa ilham “idan kika kashe su ranar da kike bu’katan kudin ya zakiyi kenan? Karki manta su kad’aine dake duk duniya yanxu, na d’auka zakice zakisi wani abu ki kwada siyarwa? Ni kam babu ruwana babu wani kubwa da zanje, kinga biyu ta kusa ki taso muje muji karatun malam sule , banaso tarihin Annabi ya wuceni yau” Amma abla idan bamu je kasuwar ba Wana irin abu kikeso musiyar?” Soma tafiya Abla tayi ilham tabi bayanta da Sauri “ Allah zai haska mana ai, Kema kuma kinsan akwai sana’a sosai da mutum zai iya farawa , Nidai yanxu damuwa ta, kar agama karatu banjiba, ga tarihin da nakeson ji, ki bari zan fad’a miki Wana irin kasuwanci zamuyi kinji?” Jinjina mata kai ilham tayi tare da kama hannunta suka soma tafiya , saida suka ‘karayin tafiya me Nisan gaske kafun suzo wata makarantar Almajira da ke cike da maza, can gefe dasu Ilham da Abla suka ra’be suna sauraran karatun Malam suke dayake ‘karawa almajiran, ganin lokacin sallah yayi ne suka samu wani guntun ruwa sukayi alwala da sallarsu, kafin su ci gaba da sauraran karatun. Karfe 3:00 daidai Malam sule ya dakata da karatun ya soma yi musu tarihin annabi yusuf, gabaki d’aya nutsuwa Abla tayi tana sauraran tarihin, ita kadai sai faman murmushi take , 4:00 ya dakata musu, d’an ‘karamin tsaki Abla taja tare da kama hannun ilham suka bar wajan” wallahi Malam sule wani lokaci bashi da M, saida na nutsu ina jin tarihi zai katse mana “, dariya ilham ta saki daman tasan za a rina , duk lokacin da zasu zo jin karatun Malam sule a’karshe sai tayi complain musamman idan tarihi ake yi lokacin , Kiraye kirayen sallar la’asarne yasasu tsayawa daidai gefen wani masallaci, saida suka tabbatar sun shiga sallah kafun su samu suma suyi Alwala da ragowar ruwan butocin wajen, can gefe da masallaci su bi jam’i suma , ana idar da sallah muma suka tashi suka soma tafiya , wani dakali da Abla ta hango ta nufa, itama ilham zama tayi a gefenta, cikin nutsuwa suka soma karanto adduar safe da maraice, duk inda ilham tayi kuskure sai abla ta sake gyara mata , har suka gama sai lokacin ilham ta fara ri’ke cikinta “ Abla wallahi yunwa nake ji,”duk da itama Ablan yunwa take ji sai bata nuna hakan ba ita , cikin tsokana ta ce wa ilham “ toh taho mu koma kurkukun mu”, tsallan data ga ilham tayi ne yasata ‘kyal’kyalewa da dariya da har dimple dinta na both side suka lo’ba, “ wallahi Kema kinsa in muka koma zamu san sauran balalle ma musamu abinci ba, ga me awaracan dan Allah ko na d’ari musamu muci”, ‘karar da cikin abla yayi ne yasa ilham ‘kara kallanta “kinga Kema yunwa kikeje, karkimun musu kawai ki taso muje muci awaran”, batayi mata musu ba kuwa suka tsaya wajan me awara saida suka ci ta d’arinsu suka kora da ruwa kafin su fara tunanin komawa gida , wata bishiyar KARARA Abla ta hango da sauri ta nufeta ilham na binta abaya , saida suka ‘karaso wajan ilham ta zaro ido “ Abla me zakiyi da karara kinsan ‘kai’kayine dashi fa sosai, dariya mugunta abla ta saki kafun ta samo wasu manyan ledoji guda uku, biyu ta saka a hannunta,d’ayar kuma ilham ta rike mata ,tsabar mugunta irin na abla wad’an da Suka bubbushe ta tsutstsunka, sai da ta tara masu yawa sannan ta dakasu da dutse , ilham gabaki d’aya ta tsorata batasan me abla zatayi dasu ba , saida ta tabbatar ya mata yanda take so kafun suka nufo hanyar gida lokacin magariba ta kusa, a farkon layin suka hango husna ita da wani a tsaye daga jikin bango sai wani mammanne mata yake, tana ganin su Abla ta d’auke kai,kamar Abla zatayi mata magana sai itama ta shareta, hannunta ilham ta kama “ Abla ki ‘kyalesu, duk wanda yace baya bu’katarki a rayuwarsa Kema ki rabu dasu, kinyi iya kokarin ki akansu amma basa ganin haka “, d’an murmushi Abla ta sakar wa ilham kafun ta furta “insha Allahu “ . Kid’an da Abla ta somajine yasa ta girgiza kai, haka suke tun farkon magariba suke sa kid’a har isha’i, a Wajan gidan kuwa kamar yadda tayi tsammani mata da maza ne kowa tare da ‘yan matansa, wasu kuma matane kawai, ko wannen su da ‘yar iskar shiga , suna shiga Sukatar da abun yafi worse ma dan gabaki d’aya daga wacce zaka ganta kwance jikin namiji sai wanda suke kiss da shafe shafe ba ko kunya, kauda kanta Abla tayi tana neman tsari daga sharrinsu, da Sauri ta kama hannun abla kada su Zinariyya su gansu, suka nufi store d’in da ya zama kamar d’akinsu, karo suka ci da Aneesa dake ‘ko’karin fitowa daga d’akin cikin wata doguwar Riga , mamaki ne ya kama su Abla dan basu ta’ba ganin ta da irin wannan kayan ba “ Anee?” Cewar Abla , itama Aneesa murmushi ta sakar musu , cike da murna ta furta “ tun d’azu nake tanbayar inda kuke akace ba’a san inda kuke ba , Aushe zan ganku dai kafun na fita “, kallan ban gane ba Abla ta bita dashi, fahimtar hakan Yasa Aneesa bud’e wata swag Jakarta itama da Alama sabuwa ce ta Fito da ma’kudan kudi tana nuna musu “ A ina kika samo wannan kudin? Karkisa na fara zargin ko sata kika fara ?” Dariya Aneesa ta saki” haba Abla ki dunga mun kyakkyawan zato man, inda naje ne nasa mu wannan kudin kyauta , kinga tun jiya kaza da lemo nake sha sai abunda yayi mun yanxu na dena kwanan yunwa , zan dunga samun kudi” atare suka had’a baki wajan furta kamar ya”, bata damu ba itama ta soma musu bayani” kawai fa hotel zakuje, Wanda aka had’a ku dashi ya d’an shash shafaku,shikenan fa”, da mamaki Abla ta furta “ kina nufin karuwanci?” Girgiza mata kai Aneesa tayi “ ni ba karuwanci nayi ba , nace miki shash shafa ni yayi yana mun wasa da breast d’ina , ni kuma yace na sha masa…”, bata ‘karasa ba Abla tayi Saurin daka mata tsawa “ ya isa haka Aneesa bana bukatar jin zancenki , Allah ya shiryeki, banga anfanin mu’a mala da me irin halinki ba “, daga bayan ta taji an furta “ sai me idan bazaki yi mu’amala da ita ba ? Ko kina ba’kin cikin kudin da ta fara samu bakamar ke da kike a wahale ba? Gabaki d’aya maida kansu sukai wajan wacce tayi maganar , Husna ce tsaye sai faman harararsu Abla take , babu Wanda ya tanka mata tsakanin ilham da Abla, Hakan sai ya ‘kara ba’kanta mata musamman ydda Abla ta sakar mata murmushi tayi wucewarta, itama ilham wucewarta tayi batare da tace musu komai ba , tsaki husna taja dan ba haka taso ba “ Alhaji sammani yace na fad’a miki yana waje yana jiran ki, karki saurari maganar su? Ba’kin ciki suke miki dan sun fara ganin kin fara samun kudi, da suke cewa karuwanci, me kikayi a ciki dan kawai an shafa ki? Ki rabu dasu nima ke nazo kira daman Zinariyya tace mun akwai wani Alhaji da yake jira na, zo mu tafi “ ta kama hannun Aneesa sukabar wajan gudun kar Abla ta fito ta hana ta zuwa.

Suna shiga d’aki Shuru Abla tayi kamar me tunani, dafata da ilham tayi ne yasata sakin ajiyar zuciya “ na fad’a miki kidena sa damuwa aranki,ki duba kiga abunda husna take miki, gaskiya bana jin dad’i” Abla bata tanka mata ba sai ma murmushi da ta sakar mata,Inda suka bo’ye ledarsu ilham ta nufa Amma wayam babu ita babu alamar ta da sauri ta kalli Abla “,Abla banga ledar da na ajje anan ba , ko kin sauya Mata waje ?” Kai Abla ta girgiza mata alamar ah’ah suka shiga bincikar d’akin ga baki d’aya ko zasu ganshi amma wayam babu ,kamar zatayi kuka ta furta “ yanxu Abla ya zamuyi kenan Haka zamu zauna kenan?Ni ina tunanin ko su husna ne ma Suka d’auka “, zato zunubi koda ya kasance gaskiya , ki kyautata musu zato, sannan idan kika yarda da ‘kaddara sai kiga Allah ya baki sama da hakan Kinji “ cewar abla “ naji Abla Amma kinsan su Zinariyya bazasu taba bamu abinci ba ,” idan kikai Imani da Allah sai kiga ya baki mafita , kinji? Komai ki dunga saka Allah a ciki sai kiga komai ya daidaita “, cewar abla , canza akalar maganar tayi ta hanyar furta “ ya kamata muyi sallah tun kafin su Zinariyya Susan da zuwanmu “, da hakan ko wannansu yayi alwala suka kabbara sallah bayan ‘boye kararan da tayi a inda baza a yi saurin ganin saba , suna idar da sallah Zinariyya da ‘yar shila suka shigo cikin d’akin, wata shegiyar ashar Zinariyya ta saki, a tsorace ilham ta kalleta Abla kuwa ko a jikin ta, “ kun gama yawan karuwancin naku? Kun mayar da kowa yan iska ko? Yau kam sai munyi maganin ku”, cikin daka tsawa yar shila ta kalli ilham “ dan ubanki ki tashi kije uwar karuwai na d’akinta tana jiran ki , kafun mu had’a dake muci ubanku “, da Sauri cike da tsoro ilham ta bar dakin, ita kuma Zinariyya ta kulle kofar daga ciki, zuciyar abla ce ta buga amma duk da hakan bata nuna musu komai a fuska ba , rigar data ga sun fara cirewa ne yasa ta mi’kewa a tsorace jikinta har ya fara rawa , ganin yadda suke ‘ko’karin cire kayansune Yasa Abla saurin kawar da idanuwanta , tunanin yadda zata ku’buta daga sharrinsu ta soma , karara d’in data ajje ne ya fad’o mata , a wayance ta d’aukoshi batare da ko wannansu ya ankara ba , daga baki d’ayansu kayan jikinsu suka cire Allah ya temaketa ma da short wando da singlet a jikinsu, yadda suka fara nufotane yasa ta fara ja da baya da baya, suma suna bunta suna dariya “ kwanda ki hakura muji dadin juna zai fi miki amma yau babu abunda zai hana ban d’and’anakiba “ cewar yar tsila , ita dai Alba babu abunda tace musu sai ma mayar da hannunta da tayi baya tana kwance karara d’in ta cikin Leda, Zinariyya ta saka hannu zata kamota kawai Abla ta fesa musu kararar nan a jiki, tare da kaucewa, dariyar mugunta suka saki har da tafawa , “kin d’auka ‘yar ‘kasar nan da kika samana zai mana abu? Yau ko me zakiyi sai mun ciki”, itadai Abla babu abunda tace musu sai ma addua da take yi cikin zuciyar ta, zasu ‘kara kama tane kamar daga sama yar shila taji kamar abu ya tsireta tayi saurin dakatawa tana ta’bawan, bata Ankara ba wani ‘bari wuyanta shima taji kamar abu ya tsireta, kallan ta Zinariyya tayi tana ‘kokarin tanbayarta menene taji itama kamar abu ya tsireta, da sauri ta saka hannu tana sosa wa , a maimakon ya dena sai kuma ya ‘Karu, da sauri da Sauri kamar had’in baki kuma suka soma Susar jikinsu hankali a tashe , duk inda suka sosa a maimakon wajan yayi sau’ki sai ma ‘karuwa da yayi, a haukace Zinariyya ta manne jikin bango tana susar jikinta, yar shila kuwa burgima ta somayi a kasa tana kururuwar jikinta , ga baki d’ayansu sun fita hayyacinsu babu abunda suke sai susar jikinsu, Abla kam dariya da tausayin sune ya kamata lokaci d’aya musamman katakwan data ga ‘yar shila ta d’auka zatai Susa dashi, Zinariyya kuwa kamar wata ‘kadan garuwa sai bun bango take , ilham ce ta fad’o mata arai shiyasa tayi saurin bud’e kofar da Zinariyya ta kulle cikin da bara gabanta na fad’uwa da sauri ta nufi haryar da zata kai ta d’akin uwar karuwai haryanxu hannunta da ledar karara.

A bangaran ilham kuwa tana shiga d’akin uwar karuwai ta tarar da ita daga ita sai wani ‘karamun towel , tana ganin ilham ta saki murmushi dukda abunda sukayi d’azu ita da Abla, muryar ilham har rawa yake wajan furta “ Gani Ance kina.. kirana”, amaimakon ta amsa mata sai ma jikinta da ta soma bi da kallo, “daukomun ruwancan “ cewar uwar karuwai, ruwan ilham ta d’auko mata jikinta na rawa musamman yadda uwar karuwai take bunta da wani irin kallo, “ ga wayata can a kan gado d’au komun “, nufar gadon ilham tayi itama uwar karuwai ta mi’ke , ilham bata Ankara ba sai bom-bom d’inta dataji ta shafa da mugun tsorace ta juyo sai taga tayi mata runfa kasan tuwar ta ‘katotuwace daman uwar karuwan,kamar zatayi kuka ta furta “ ga wayan”, a maimaikon ta amsa wayar sai kwantawa da tayi towel din jikintadaga sama sama ana ganin na shanunta kamar kan jinjirai guda biyu, “yimun tausa”, cewar uwar karuwai , kamar ta kwalla ‘kara Haka takeji sai duba ‘kofa take tana so taga ta inda Ablan zata temaka mata, cike da tsawa tace “ ba dake nake va?” Arud’e ilham ta kama yar lukutar ‘kafarta me shegen tauri tana matsawa, duk inda ta matsa sai uwar karuwai ta furta “Ashhhhh da dadi”, sosai hakan ya fara bawa ilham tsoro,amma ba damar musu Sabida yadda zubun uwar karuwai yake tsoratata, d’an zame towel d’inta uwar karuwai tayi yanxu kam sosai na shanunta ya fito ba’ka’ke wuluk dasu waje sai mai’ko suke, cikin rawar jiki ilham ta soma ja baya , fuska a had’e uwar karuwai tace mata ta matso, Amma tsoro ya hanata hakan , tsawar data daka mata ne yasa ta matso kusa da ita, mummunar fuskarta ta d’aure ba wasa ta furta “ cire kayanki na du baki “, hakuri ilham ta soma bata amma ta d’auketa da gigitaccen marin da yasa ta cire hijabinta , tana kuka ta soma ‘ko’karin cire rigarta, banko ‘kofar d’akin da Abla tayine yasata sakin ajiyar zuciya , itama Abla ajiyar zuciya ta sauke ganin ta zo adaidai, wani bakin cikine ya tokare wuyan uwar karuwai, ga samu ga rashi duk alokaci gudu, ranta a ‘bace tana mamakin ina su yar shila da ta saka su rufe mata Abla , Abla kam fuskarta ‘kam a kanta ko tsoron abunda zata sa ayi mata bataji, “me ya kawo ki d’akin nan ? Ki tattara ki fice mun daga d’aki kafun ranki yayi mummunan ‘baci,”toh abla ta furta kafun ta ruko hannun ilham zasu fita
End Ads