x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 65 - IBTISSAM BOOK 1

  • 192001 words
  • 195000 words
  • Out of 200864 words

Category: Romance Story +18

Views 300

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
Baby ta furta wayyo Allah na , adduar da Abla ta koya mata take ‘ko’karin yi amma kamar wacce ake sha’kewa ma’koshi , gabaki d’aya sai ta kasa magana, a razane ta mi’ke ta saka gudu zata koma wajansu Abla , tun kafin tayi nisa taga wani irin ba’kin abu na tunkaro ta ,da sauri Baby ta soma ja baya gashi gabaki d’aya bakinta ya kasa bud’uwa balantana ta iya addua, yadda abun yake nufota gadan gadan ne yasaka Baby yanke jiki ta fad’i a wajan su mammiya . Kamar jira abun da tagani yake , yana gani ta sume a wajan ya rikid’e ya koma gizo gizo, a hankali ya zoma zagayeta yana bud’e bakinsa, da ya kai daidai kanta sai ya kasa ta’ba , ya kai sau uku yana ‘ko’karin saka bakinsa a kanta, a karo na hud’u da d’aya daga cikin’kafafun sa suka ta’bata ya saki wani irin gurnani mara dad’in ji , cikin sauri ya soma ja baya , ko second biyar be ‘kara a wajan ba , wasu ba’ka’ken gizo gizo suka ‘kara fitowa kamar wasu aljanu, duk wanda yayi ‘ko’karin ta’bata sai ya kasa , sun dad’e suna abu d’aya kafin su zagayeta gabaki d’ayansu suna binta da ba’ka’ken idanuwansu.

***** Tunda teacher d’in maths yashigo su Abla suke kallan ‘kofa suna jiran shigowar Baby , amma har teacher d’in maths ya gama teaching d’insa Baby bata dawo ba shiyasa gabaki d’aya babu abunda suka fahimta a maths d’in, suna ‘ko’karin mi’kewa teacher d’in geography ya shigo , nan ma gabaki d’aya kasa samun nutsuwa sukai gashi 2 class ne dashi a jere , kusan Allah Allah suke kawai ya fita , time nayi babu wanda ya tsaya jiran books d’insa a cikin su , haka suka nufi wajan flowers d’in da Baby ta ce musu . Adaidai lokacin da su Abla suke tunkaro wajan adaidai lokaci suma gabaki d’aya gizo gizon suka ‘bace , sai Baby dake kwance a wajan a ‘kasa kamar matacciya.

Eshaal ce ta soma hango ta, hannunta har rawa yake lokacin da take kallan Baby , suma gabaki d’aya inda suka ga Eshaal ta kalla suka kalla, cikin sauri suka kwala kiran sunanta tare da nufar Inda take a gwance , Abla kam kasa ta’bata tayi sai binta kawai da take da kallo, Eshaal da Fanan kuwa sai faman jijjigata suke , lokaci d’aya kuma suna kiran suna ta , ganin ta’ki motsa yasaka Fanan barin Wajan a guje, amma ko mintu biyu batayi ba ta dawo d’auke da wani bottle wata, cikin sauri ta bud’e ruwan tare da yayyafawa Baby, wani irin jannufashi Baby tayi sai a lokacin Abla ta iya matsowa wajan ta , a firgice Baby ta bud’e idanuwanta tana bin ko ina da kallo , suma kallan wajan suka soma kama ganin babu komai , a hankali Baby ta saki ajiyar zuciya “ Menene ya faru Baby ?” Cewar Abla , Baby ta bud’e baki zatayi musu bayani kamar almara ta manta duk abunda ya faru, hannu kawai ta bud’e tare da furta “ Nima bansan me ya faru ba ! Sai yanzu da naganku a Wajan “baki suka saki gabaki d’aya suna kallanta “ kudena kallo na ! Ku taso mu tafi “ tana kai wa nan ta juya , suka suka bi bayanta suna mamakinta .

Har lokacin tashi yayi basu dena mamakin Baby ba , gashi gabaki d’aya ta ‘kiyi musu bayanin abunda ya faru da itama , musamman Abla da take lura da ita, lokaci zuwa lokaci tana d’an firgita. Ana tashi su Eshaal suka koma hanyar gida , itama Madam sarah time d’in tashi nayi tazo d’aukar Abla suka tafi gida .

*****Abla tana shiga cikin gidan ta tarar da babu kowa a falourn, a tunaninta su Little suna d’aki shiyasa itama bata zauna a falour ba ta wuce cikin d’akinta tayi wanka ta shirya cikin maroon d’in doguwar riga . Tana sakko wa ‘kasa still bata tarar dasu Little a ciki ba , batayi tunanin komai ba ta wuce dinning zatayi serving kanta , kamar Ance mata ta jiyo taga su Little sunfito daga wata ‘kofa , prince na gaba little na binshi a baya ga hannayensa biyu da ya ‘boye duka a bayansa . Murmushi Abla ta sakar musu “ Na dawo gida nan gankuba , na d’auka bakwanan ai “ , murmushi a face d’insu suka furta “ No Lil mun tsaya wani abune “ kallan bayan prince Abla tayi ganin yadda Little yake kakkarewa , cikin ‘yar dariya Abla ta furta “ yaya little me kake ‘boyewa a bayanka ?” Kanshi ya girgiza mata ga face d’insa da har yanzu akwai murmushi akanta “ No ! No! Babu komai “ zatayi magana prince yayi saurin furta “ No please karki yi magana “ shiru Abla tayi tana Kallansa , da Sauri ya zagayo ta bayanta ya kulle mata ido da wani bakin abu, ita Abla gabaki d’aya dariya suka bata ma yadda suka kulle mata fuskarta , “ karki magana “ cewar prince , batayın ba kuwa har prince ya kama hannunta suka zaunar da ita kan kujera , tana zauna prince yayi dialing number din uncle da shima ko mintuna 5 beyi ba ya fito face d’insa fal murmushi. Da ido Little ya nunawa prince ya bud’e wa Abla idanuwanta , yana cire kyallan prince da little suka had’a baki wajan furta “ Happy Birthday princess “, at the same time kuwa ya fito da wani medium cake da ya ‘boye a bayansa . Lokaci d’aya gabaki d’aya murmushin fuskar Abla ya ‘bace sai ja da fuskarta ya soma yi , da Sauri ta sunkuyar da kanta ‘kasa tana taunar le’ben ’kasan bakinta ,” Lil ?” Tun bai ce sister d’in ba Abla ta kulle idanuwanta tare da fashewa da kuka , cikin Sauri little ya ajje cake d’in tare da zama a side d’in ta , “ Lil me akai miki? Waya ta’ba ki ? Ni ne ? Yaya prince ne ? Me akai miki?” Shine tanbayoyin da Little ya soma yi wa Abla ganin yadda take kuka sosai , uncle kuwa waje ya samu ya zauna yana kallan Abla ganin yadda take kukan ta da gasken gasken, Little zai sake magana Uncle yayi saurin dakatar Dashi “ it’s okay Little “ da Sauri little da prince Suka kallesa , da kai kawai ya amsa masa yana ‘kara Kallan yadda Abla take kuka . Suma shirun sukai suna ‘kara binta da idanuwa , musamman little da shima yake ji kamar yayi kukan.ta d’auka kusan 5 minutes tana kuka ganin kukan nata bame ‘karewa bane yasa uncle dakatar da ita “ it’s okay Daughter, kukan ya isa haka , tunda birthday d’in ne bakyaso bazasu sake miki ba , kinji ?” Sai kuma ya ‘karasa yana kallan su Little “ karku ‘karayı mata tunda bata kunji ?” Cikin Sauri Abla ta girgiza masa kai , muryarta kamar me kuka ta furta “ Ah.. ah ni basuyi mun komai ba uncle , abune ya shiga cikin ido na , babu abunda ya sameni “ , shiru sukai mata suna kallanta ,kafun prince ya furta “ kuka kikai magana , bamusan hakan zai ‘bata miki ba , we’re all sorry “ wani kukan Abla yaji yana san sake zuwar ta , murmushi me ciwo ta saki sosai kafin ta furta “ Dagaske nake yaya prince ni bakuyi mun komai ba , ku dena bani hakuri “ then me yasaka ki kuka ?” Cewar little yana tsareta da ido, shiru Abla tayi masa tana bin cake d’in gabanta da kallo , shima prince murmushi ya d’an saki kad’ai kafun ya furta “we’re not family ? Da bazaki fad’amun abunda yake damun ki ba ? I thought we’re family ! We can share our issues ! Amma it’s okay tunda bakya san kowa ya sani “ ya ‘karasa yana ‘ko’karin mi’kewa , da Sauri Abla ta ri’ko hannunsa “ No please ka zauna “zaunawar yayi kuwa yana kallanta , wani murmushin Abla ta ‘kara saki “ ba yau ne birthday d’ina ba , bansan Yaushe bane , bansan ranar ba Nima “ cikin Sauri prince ya furta “ Sister “ kanta ta jinjina masa “ yes ! Yaya prince bani da family, bani da kowa , bansan su wanene suka haifeni ba ,bansan mamana ba , bansan babana ba , sun mutu ko suna raye duka bansani ba “, hawayen da suka zubo mata Abla ta share tana sakar musu murmushi ganin yadda reaction d’in face d’insu ya canza gabaki d’aya , a jiyar zuciya ta dauke ahankali kafun ta cigaba “ cikakken sunana shine Ibtissam amma cikin wad’an da na rayu dasu suna kira da Abla, kullum cikin godewa Allah nake da irin rayuwar da na tashi , kuma bazan daina gode masa ba , kamar yadda na fad’a muku bansan su wanene suka haifeni ba , nasan kawai na taso cikin ‘kunci da ba’kin cikin rayuwane,da farko na taso cikin gidan haka , matar da ta d’auke ni ta shaidamun batasan su wanene suka haifeni ba , ta tsinceni ne cikin wata ‘kauye a daji cikin cijayawa duk Jini a jiki na , ga ruwa anayi lokacin wannan ne babban dalilin da yasa ta tausaya mun ta d’auke ni, nayi rayuwa da Ita cikin bautawa , kamar baiwar ta haka ta mayar dani dukda nafijin dadin sosai akan inda na rayu , ko ba komai tayi mun hallaci,ita ta sakani makaranta, take boyamın kudin makaranta , abinci na , komai ita take yi mun shi , hatta sunan da na mahaifinta nake anfani a makaranta Sabida bansan wanene nawa uban ba.” Sai da ta saki a jiyar zuciya kad’an kafun ta cigaba , “ rayuwata ta soma gur’bacewane tun bayan rasuwar ta , Sabida tsangwama da mutane suke nuna muna , suna Kirana da yar karuwa , bani da yadda zanyi , babu Wanda zai tai maki rayuwa ta , da farko na soma kwana a cikin kwango amma Sabida yadda mutane ke ‘ko’karin lalatamin rayuwa tsoran hakan ya kamani, Tuna’nı na kullum ya zanyi na tsira , kwatsam wata hajiya ta so temaka mun duk na so na ‘ki amince mata amma sabida ba yadda zanyi dole na amince mata , haushe ‘ko’karin fad’awa rami nake, a ranar farko da naje gidan ta , ta kula dani sosai kamar yar data haifa har na soma sha’kuwa da ita Sabida Itama ta fad’a mun ita kadai take rayuwa bata da yan uwa, shiyasa Nima na sake sosai da ita , a cikin kwana na biyar da nayi a cikin gidan ta wasu mutane suka d’auke ni daga wajan ta, Aushe siyar dani tayi , ta siyar dani ga macen da ta fi kowa san lalata dani , karuwa, mara tsoran Allah , mara ‘kaunar addinin Allah, nasha wahala sosai , bana bacci sai cikin dare sai ayyukan da nake yi , ga kiran da ake saka wa cikin dare , hakan baya hana ‘karfe 3 na dare a tashe ni daga bacci ni da ‘yan matan da aka siyar dasu , ka zame mun tamkar yan uwana na Jini , Arwa, ilham, Aneesa, muna shan wahala sosai , basa bamu abinci, kullum burin su , su sami Wanda zaiyi lalata damu ,” gabaki d’aya sai da Abla ta zaiyane musu irin rayuwar Da tayi cikin gidan uwar karuwai da ‘kalubalen data fuskanta har kashe mata Arwa da sukai da yadda suka siyar da ita har zuwa lokacin da su Bobo suka tsinceta, tana kaiwa nan ta fashe da kuka tana kulle fuskarta, cikin Sauri Little ya goge hawayen fuskarsa “ waya ce miki baki da family ? Ku kuma fa ? We’re all family! Na miki al’kawari I will always be by your side , kin manta ni yayan kine ?” Kanta Abla ta jin jina masa tana murmushi kad’an , shima prince hannunta ya ri’ke “ we’re family ki dena cewa baki da family , duk Wanda ya ta’baki just karki manta Prince and Little will always be there for you , kinji?” Yanzu ma kanta Abla ta jinjina masa gabaki d’aya sai sukayi hugging d’in juna . Uncle kuwa tun da ta soma basu labarin ta be motsaba sabida zurfin Tuna’nın da ya fad’a , ganin yadda mood d’insu ya canzane suma Abla ta furta “ Nifa yunwa nake ji ! Let’s eat the cake “ kasa magana sukai gabaki d’ayansu, da kanta Abla ta yanka cake d’in , ta basu, zasu magana Abla tayi saurin furta “ let’s enjoyed our life komai da sanin Allah ! Okay ?” Kansa little ya jinjina mata, gefe d’aya kuma yana jin badad’i ko kad’an, zuciyarsa yaji ta soma zafi shiyasa ya kawar da komai amma duk da hakan yana ‘ko’karin dannewa sabida bayasan tayar musu da hankali .A ‘bangaran Abla ma dannewa kawai take sabıda kar suga rauninta, shiyasa Ta kawar da duk wata damuwar ta Sabida tana san ganin farin cikinsu , suna zaune a falourn har lokacin kuma babu abunda uncle yace sai binta da kallo da yake. Lokacin sallah nayi suka wuce masallaci itama kuma Abla ta wuce d’akın ta . Cikin Sauri ta kulle ‘kofa tare da tsugunnawa a Wajan , kukan da take ‘boyewa yana ‘kwace mata .

******NYC****
********* wajan ‘karfe 3:20 helicopters d’insu Big Boss suka sauka cikin wani gida da kallo d’aya idan mutum yayi masa zai ga sojoji tako ina suna shawagi a cikinsa , ga bindigu dake hannun ko wannansu , suna sakkowa gabaki d’aya sojojin suka zagaye wajan suna jiran fitowar su Big boss, a hankali ya fito daga cikin helicopter din shida Bobo, yanxu babu face masks a fuskarsa sai face d’insa da take d’aure babu ko d’igon fara’a , suna ganin fitowarsu suka sara musu cikin tsantsan girmamawa , babu Wanda Big Boss ya kalla a cikinsu ya nufi cikin gidan , cikin Sauri su Victor suka bi bayansa , Bobo kuwa helicopter d’in da aka d’auko prisoners d’in ya kalla Daidai lokacin da Suke fitowa , abun mamaki gabaki d’aya sun canza kayan jikinsu zuwa wani kayan da ban , ga ‘kafar d’aya daga cikin su da aka harba da bandage alamar anyi masa treatment , sojojin nan suka ganin fitowar su suka saramusu lokaci d’aya , suna prisoners din sara musu sukai kafun su kalli Bobo da ke tsaye a gefen su , fuskar ko wanne da murmushi aciki sukai hugging d’in juna. “ Good job “ cewar Bobo , kallan hannun Bobo da aka harba d’ay daga cikin su yayi “ Sorry Dude ! Dole yasa nayi maka haka , but am sorry “ bugu Bobo ya kai masa mutumin yayi sauri kauce wa , a haka suka nufi cikin gidan da Big boss ya shiga ،a tsaye suka tarar dashi ya zuba hannayensa cikin aljihun wandansa , lokaci d’aya suna ‘kame tare da sara masa kafun biyu daga cikin su, su nufesa tare da hugging d’insa “ Long time ! Big Boss “ banzan kallo Big Boss ya jefa masa , dan ‘karamun dariya Bobo yayi kafin ya furta “ snoopy kwanda ka rabu dashi kafin kasamı Kasan naushin ka now “ Wanda aka kira da snoopy yayi dariya kafun ya furta “ Bobo it’s now 4 month fa muna prison just a work , kaga yanzu dole na takalosa tunda shi ya saka mu wannan aiki, and if to say shi na harva d’azu I think muna shigowa nan zai saka a tsireni “, gabaki d’aya shiru sukai tare da zama kan chairs din wajan. Almost 5 minutes suna zaune a haka kafin Big Boss ya furta “ Welcome Back Alpha team”da Sauri wani farin bature ya furta “ yeah the team is back ! Now lokacin operation ne “ kansa Big Boss yayi knodding kafun ya samu waje ya zauna , d’ayar guy din da tunda Suka shigo beyi magana bane ya ciro kwalbar da mutum d’azu ya saka masa a prison , cikin tsokana ya furta “ Mun Samu kwalbar! Yanxu aikin mu zai tashi zuwa wani stage din! Work time ! Black operation 111 “….., daga haka suka cigaba da tattauna maganar da suke sanyi cikin sirri batare da kowa ya jisu ba.

Har bacci ya kwashe Abla bata sanı ba sai farkawa da tayi taga shida ta kusa , cikin sauri ta wanke face d’inta tayi wanka tare da yin alwala sabida kiran sallah da ake yi , Sabida baccin la’asar d’in da taji sai taji gabaki d’aya ranta a’bace yake har tayi sallah kuwa , har zata zauna a d’akin sai ta fasa kuma ta sakko falourn , Daidai lokacin da prince xai wuce , yana ganin Abla yayi saurin dakatawa “ Yawwa Lil ! Please come and help me kinji , shaff namanta su yaya Big Boss zasu dawo and namanta bamu gyara part d’insa ba , please ko zaki temaka ki gyara , irin gyaran sa kikai masa kafun mu dawo ?” Kanta Abla ta jinjina masa dan ko magana bata sanyi, “ Thank you dear” cewar Prince , ynxu ma kanta Abla ta jinjina masa, sabida süne akwai zata gyara masa d’akin amma idan ta Ita ne har abada ta dena shiga part d’insa shiyasa bata ‘bata lokaci ba ta nufi part d’insa gudun karsu had’u , mayafinta kawai ta zame da doguwar rigar jikinta tabar guntun wandan ta da ya wuce cinyarta kad’an sai white shirt d’inda ta saka matsatsiya, kanta kuma ta d’aura wani white cap , cikin ‘kan’kanın lokaci ta soma gyaran falourn sa , komai sai data gyara cikin falourn , kafun ta koma second falourn nasa shima tana gyarawa , batasan ya akai ba lokaci ya ja sosia , har wajan ‘karfe 8 tana aikin gyara masa part
End Ads