x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 17 - IBTISSAM BOOK 1

  • 48001 words
  • 51000 words
  • Out of 200864 words

Category: Romance Story +18

Views 274

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
nan, nagaji da abubuwan da suke , mahaifiyata ta rasu, mahaifina da nake tunanin xai Sharan hawayena ko rabarsa bayaso nayi, wacce zan kalla kamar uwata ta tsaneni, bayan ke babu me sona Amma , Wana irin lefi nayi musu haka da na cancanci irin wannan hukunci?” , kowa da irin tasa jarabawar Eshaal , Allah yana jarabtar bayinsa ta ko wace hanya bawai dan baya san suba , ah ah Sabida ya kwada imaninsu ne , ki dena saka komai a ranki duk lokacin da kikaji ranki ya ‘baci ki kunna karatun alkurani zai debe miki kewa “, kanta Eshaal ta jinjina “ nagode sosai AMMA , nagode Amma dan Allah Amma ki dunga hakuri da abubuwan da baby take miki acikin gidan nan “, karki damu babu komai wallahi, “ yanxu ma naga sun fita ne bansan me za’a dafa mata na dare bane shiyasa nace bari nazo na tanbayeki “, hawayenta Eshaal ta goge “ Karki damu Amma yau baza muyi girkin dare ba , na Riga na dafa yana dinning , nasan yanxu kingaji ya kamata Kema ki dunga hutawa kinji Amma “, Allah yayi miki albarka “ cewar Amma , itama cike da farincikin adduar Amma ta furta Ameen, Amma na barin d’akin ita kuma tashiga wanka , shaf shaf ta Fito kaya kawai ta saka sai turare kad’an , batasan lokacin da su baby zata dawo ba tasan kuwa intace bazata gyarawa baby d’akin ba wani karin drama ne zai faru da zata kwana tana kukan bakin ciki. Shiyasa bata zauna a d’akinta ba ta nufi na Baby dan ta gyara mata tunkafun momcy ta dawo itama .

🍃🍃🍃🍃
GERMANY
FRANKFURT

“Sauban meyasa kake sawa ranka abunda ya faru tsawan shekaru?shekara 22 ba wasa bane , tsawan lokaci kasawa ranka abunda yake neman illataka , Na ro’keka ka cire wannan damuwar dake ranka karka sawa kanka wata cutar”, cikin yaran German wata kyakkyawar mata da ashekaru bazata wuce 50 ba , jikinta sanye da irin kayan Germany masu shegen kyau, d’ago da idanuwansa guy d’in yayi, kyakkyawane shi na ajikin ‘karshe da za’a iya kira d kyakkyawa amma ba fari bane chocolate colour ne shi amma kalar fatansa me kyau ce sosai kanshi cike yake da suma amma ba’a kwance take ba irin gashinn Americans haka gashinsa yake sai faman ‘kyalli da take d’auka ba’ka’kirin da ita “ kiyi hakuri Mameey! But I can’t , bazan iya manta suba , gani nake duk lefina ne , if not my best friend nasan da yana tare dani, mamey lefina ne da natafi na barsu”, kusa dashi ta samu ta zauna tare da fuskantarsa , cike da tausayi ta kallesa “ Sauban ba lefin ka bane , it have been years now , ya kamata ka cire wannan abun aranka , karka manta munbincika amma har yanxu babu labarinsu , for how long zaka sawa kanka damuwa haka ? Kanasan sawa kanka ciwan zuciya ? Ka tashi hankalin ka sannan ka tashi hankalin mu, bana tunanin ma suna raye yanxu…”, No please mamy, ki bari banajin dad’i duk lokacin da kike maganar basa raye , we lost dad and now kina fad’amun suna sun mutu?please , Insha Allah sunanan da ransu and zan bin ciko duk Inda suke , ina so naji ya yafemun, inaso mu dawo yanda muke Ada “, kallansa kawai mamey tayi ta rasa Wana irin soyayya yake wa best friend dinnan nasa , bata sake ce masa komai ba ta mike ta nufi hanyar fita “ kiyi hakuri mamy “, shine kadai abunda sauban yace mata harta fita , wani diamond bracelet d’insa ya kalla shi kad’ai yana tuna memories din abun hannun da baze taba gushe masa a rai ba .
Babban Frame d’in sa dake cikin ‘kayataccen d’akin ya kalla, kai tsaye wajan frame din ya kalla, bakomai bane a ciki sai wani drawing da ya d’an fara tsufa cikin sa zanen bracelet din hannunsa ne a ciki kamar Wanda ya d’auko ya manna Sabida yadda zanan ya fiko kamar a zahiri.

“Assalamu Alaikum,”wata daddad’ar murya siririya tayi sallama, amsa mata yayi yana juyo wa shima , wata fine girl ce kyakkyawar gaske , skin d’inta sak irin na Sauban ne , ga baiwar kyau da Allah ya bata, sosai kamanninta ya fito irin na sa , banbancin su kawai ita macece amma kyakkyawar budurwace da a shekaru bazata wuce 17-18 ba, jikin ta sanye cikin wata farar shirt d’in Riga irin me design, sai ba’kin falazo da ta saka ba’ki , kansa kuma wani d’an madaidaicin mayafine shima black colour data nad’e uban tulun gashin kanta , Cikin daddad’ar murya tace “ can I ?” Kansa ya gyad‘a mata yana sakar mata murmushi , itama martanin murmushi ta sakar masa lokacin da take shigowa d’akin , “ Yaya BiiBii ga abincinka nan mameey tace na kawo maka “, kan wasu kujeru biyu masu had’e da center Sauban ya nuna mata “ Thank you SISI FANAN”, murmushi ta sakar masa “ you’re always welcome Yaya Bibi sauban , kaci abinci please amma idan ka gama zan dawo hira nasan nan da 2 days zaka tafi , lokacin da zaka dawo may be ankoma school ina U.S sea dea ka kawo mun ziyara “ , toh mamey “ cewar Sauban yana hararan ta , itama fanan dariya tayi tare da nufar kofar fita ,tunda taji yace mata mamey bazai zo mata ziyaraba kenan daman bazuwa yake ba. Harta fita ta kuma dawowa “ and last yaya biibii plx ka rage damuwar wannan besty din naka da har yau bantaba ganin saba sai a labari”, pillow dinsa ya jefo mata da Sauri ta fice tana dariya .

🍃🍃🍃🍃
🍂🍂🍂🍂🍂🍂

ABUJA
ABLA

yau gabaki d’aya tun da ta tashi take jinta wani iri alamar kwana kin period d’inta na daf da zuwa , dama hakance ke faruwa da ita a duk lokacin da period d’inta ya kusa zuwa , gabaki d’aya yau sukuku ta tashi , Sabida tunanin zuwan period d’inta dan ba’karamun wahala take shaba a duk lokacin da take yinsa , ga tunanin yadda zata biya uwar karuwai kudin da tace mata zata biyata duk ya tsaya mata a zuciya , d’ari uku da hamsin d’in da yayi mata ragowa kawai ta kalla tun bayan Awarar hamsin d’in da taci da safe bata kuma cin wani abuba duk da yunwar da yake ji yanxu , yau gabaki d’aya haka kawai taji bata san futa shiyasa tayi zaman ta a d’aki tun bayan lokacin da su Arwa Suka bar d’akin. Tun tana waje take jin hayaniya na tashi kad’an kad’an har hayaniyar ta so tayi yawa shiyasa ta tashi ta rufe ‘kofa.
A falo kuwa sai faman gyare gyare ake yi tun safe , ga wasu set din kujerun roba da ake faman jerawa kamar masu shirin yin wata liyafar, ga sabbun beers(giya) da shisha da ake shigo dasu , kowana table ansaka amsa giya da shisha, ga kayan lemo da ake jejjerawa , gabaki d’aya tsarin wajan kasan na tantiran ‘yan duniya ne da baki bazai musalta ba. Duk wannan abunda suke Abla tana d’aki bata san wainar da suke toyawaba sabida ydda cikinta ya fara yimata ciwo ciwo alamar ako wana lokaci period d’inta zai iya zuwa , gashi in tana period batasan kowa kusa da ita musamman yadda take fita hayyacinta, tun tana sa abun a rai har bacci ya d’auketa.

6:30 pm wani irin kid’a aka saka daya firgitar da Abla daga baccin daya d’ebata, kid’a ne kawai yake tashi ga ‘kara da shewa da take jiyowa , Sabida yadda kid’an ke tashi ko kiran sallah bata jiyowa, gashi bata san fita balantana su ganta ko wani ya dakatar da ita har lokacin salla ya wuce ta , ba yadda ta iya haka ta hakura tayi sallarta ga uban kid’a da yake tashi sai kace gidan arna duk lokacin sallar magrib. Ban kad’o ‘kofar d’akin da akai ne ysa ta d’ago da lumsassun idanuwanta, wasu kaya debeka ta jefa mata , “ kisa ka kayan nan ki fito kafun nan da mintuna biyar idan ba haka ba mazan da kike i’kirari ba kyaso su ta’baki sune zasu d’aukoki “, ta karasa tana sakar wa Abla harara, ko motsa Abla batayi ba balantana tayi tunanin saka kayan dan yadda na gansu daga nesa tasan ba kayan arziki bane kwata kwata , har tsawan minti 4 tana zaune a wajan , taso tayi taurin kai amma tasan Itace a ruwa Sabida kamar yadda debeka ta fad’a hakan ce zata kasance dan tsaf zasusa maza su d’akko ta . Jiki a sanyaye ta gyara hijab din jikinta, lokacin da taji wani irin sowa ya tashi yasa tafito daga cikin d’akin, a cikin falo kuwa dandazan maza da Mata ne yan duniya cike a falon ga kid’a da aka saka musu sai faman rawa suke cud’e da zunansu, yadda hayakin shisha da warin giya da ya cika falon yasa Abla tayi saurin toshe hancinta , lokaci d’aya wani kid’an ya ‘kara tashi da ya saka Abla toshe kunnuwanta, a take a Wajan kid’a da rawar da ake ya tsaya, daga inda take hana iya jiyo takun na kalli na shigowa ga wani irin kas kas kas din cingum da ake taunawa , yan falon gabaki d’aya bin hajiyar matar da tashigo suke da kallo, a kallon karfo da mutum xai mata yasan zatayi 45 to 47 years a shekaru Amma d’in kin jikinta ya ‘kwararrun tantirai tayi musamman da tayi d’inki zamani Kawai wata budurwa , ga breast d’inta da ake hangowa Sabida d’inkin da tayi, ko mayafi babu a jikinta shiysa kayansuka ‘kara d’ameta, tabar dake hannunta ta ‘kara zu’ka cike da kwarewa kuma ta fesar da ita ta hanci da ta baki, cikin ya tsina fuska ta soma bin kowa na cikin falon da kallo, yaranta na take mata baya , cike da ga daya ta furta “ Ni sunana BINTA SHALAGA, ni nake shagalta yara maza da mata , zawarawa da duk Wanda yake san jin dad’i, kowa ya ji dad’insa ya huta , maza su za’bi matan da suke so, mata ma su za’bi mazan da suke so , mata idan mace takeso ta d’auka namiji idan namiji yake so ya d’auka , kowa yasha shagalinsa , yadda ko lahira akaje kun d’ana “, lokaci d’aya falon ya d’auka sowa da ihun kiran sunan BINTA SHAGALA, hannu ta d’aga musu lokaci d’aya suka shiru gabaki d’ayansu “ kafun nan ina bukatar yarinyar da zan huta ku kuma kusha sha’aninku , idan na sake fitowa ko wacece sa’a yazo kanta tana da babbar kyauta Dan haka zan za’ba , UWAR KARUWAI da ta saka kowa su bubbud’e sabida aminiyarta ta za’ba yarinyar da take bu’kata , wani wawan tsaki Abla taja , wani haushin kanta ta somaji da tafito falon har kunnuwanta suka ji mata wad’annan munanan kalaman, ta juya da niyar barin Wajan taji saukar sha’kar’kiyar muryar BINTA SHAGALA ta furta “ gatanan “, lokaci d’aya haske ya kai kan Abla da BINTA SHAGALA ta nuna .


MASU BU’KATAR A TALLATA MUSU HAJARSU SUYI MUN MAGANA TA NUMBER NA 07041879581.

LEESHARH DATA HUB 2
MTN
1gb-240
2gb-480
3gb-720
4gb-960
5gb-1200

AIRTEL
1gb-300
2gb-600
3gb-900
4gb-1200
5gb-1500

Validity 30 days

Account number : 2681892316 Aisha umar zenith bank .

Phone number : 07041879581.


https://chat.whatsapp.com/DBN2FLDRV5XKMpvHpltmLt

IBTISSAM
( A heart touching story of love and destiny)

Story & written
By
Mss Lee ✨


Littafin IBTISSAM is now 300 , me bu’katar ya karanta littafin har ‘karshe zai iya biyan kud’insa ta wannan bank d’in 2681892316, zenith bank , Aisha umar, sai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581.

Littafin ibtissam ‘kir’kirarran labari ne , ban yadda wani ko wata ya juyamun book ta ko wana sigaba. Duk Wanda littafina yazo d’aya daga cikin wani sashe na rayuwar sa, to a rashi sani ne .

💞ALL PRAISES ARE FOR ALLAH IN ALL CONDITIONS 💞.

___💕 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM 💕___

BOOK 1
Season__13.
A rud’e Abla ta juyo tana bin dandazan mutanan falon da kallo kamar yadda suke binta dashi, lokaci d’aya wani irin shewa ya karad’e ko ina , musamman wanda suke jin haushinta da Wanda suka tsaneta, gani sukayi ko su basu same taba tunda za’a lalata ta hakan ma ya biyasu, wani irin shewa aka ‘kara d’auka “ sai kinyi BINTA SHALAGA” shine abunda yan iskan samari maza da mata suke cewa , uwar karuwai kuwa bataji dadin nuna Abla da tayi ba Sabida itama tana san cin ma burinta akan Abla , amma babu yadda zatayi idan tace bazata bawa binta shagala abla ba zata iyayin rashin makudan kudaden da zata kar’ba a wajanta, shi yasa ta sakar mata ya’ke “ Amma Aminiyas ki duba kiga ratsats tsun yan mata masu Jini a jiki, komai gashinan ya fito wara wara, idan breast ne gasunan luba luba , idan bom-bom dinne ma gashinan Washa washa , me zakiyi da Wannan kazamar kullum cikin hijabi, bakya tunanin ko nuna kayan ta basuyi bama “, wata yar iskar dariya Binta shagala ta saki “ kawata baki da dama , ni nafi san d’an yan kaya ai , banasan nunannu,nafisan na nuna kayana da kaina sannan nasa suyi tsuro, ina santa, sannan ta mun yadda nake so duk da banga jikintaba Amma zan d’an d’anata “, cike da mugunta wayanda suka fi jin haushin Abla suka dunga ihu cikin su kuwa harda husna da ta sha wankan ‘kananan kaya.
Da wani irin banzan kallo Abla ta bi binta shagala dashi, tsanarta na darsan mata cikin zuciya, duk da tsoro da bugawa dake ziyartar ta ga fargaba da yasaka zuciyarta bugawa da Sauri Sauri , ko a fuska bata nuna ba sai a cikin zuciyar ta da take faman kai kawo, bata shiga tashin hankali ba sai da binta shagala ta saka ‘yan iskan yaranta mata da duk cikin su babu me shigar Arziki ta nuna musu Abla akan sukai mata ita d’akinta , sannan ta bawa kowa kyautar yasha duk abunda yakeso , sannan yayi duk abunda yake so zata d’au nauyi dan tace partyn till down za’ayi, cikin ihu da sowa cike da jin dadi , dan da zan barikin suka soma had’ewa da junansu , Abla ma tayi ‘ko’karin guduwa Amma gabaki d’aya babu hanyar da zata ku buta, sosai Tasha Danbe da yan mata ukun da Suka ‘ko’karin kamata , ba ita da take danban kwacan kanta dasu ba , hatta suma matan saida suka jigata sabida yadda Abla ta jigatasu, da bala’i da masifa haka suka kinkimi Abla zuwa d’akin Binta shagala da har ta cire kayanta sai wani d’an iskan underwear skirt data janyo saba , sha’ba sha’ban na shanunta da suka kwanta har wajan cikin ta ana hangosu ga ta ‘baka Kirin da ita, da Sauri Abla ta kawar da kanta tana neman tsari daga sharrinta, yadda binta shagala take binta da kallo zaka san ba ‘karamar cikakkiyar ‘yar bariki bace , cikin wani irin tafiya , cinyoyinta na had’ewa kamar wata saniya ta soma tunkaro Abla , da Sauri Abla taja baya ta nufi ‘kofar fita Amma a kulle alamar ta waje aka kallesu,wani dan iskan dariya binta shagala tasaki “ baby na da kin kwantar da hankalinki, bazamu dade ba ,2 hours ne kawai, zamuji dad’in mu, Kema kiji dad’inki sannan kuma ki samu babbar kyauta daga gareni “, duk da yadda Abla take cikin tashin hankali hakan be hana ta Dallawa Binta shagala harara ba , amma ko a jikinta sai ma ‘kara nufo Abla da tayi , itama Abla bakinta d’auke da addua ta fara ja baya, still binta shagala na binta har tazo wajan gaban mudubi, Daidai binta shagala ta d’aga hannunta zata ta’ba Abla , turaran da Abla ta gani tayi saurin d’auka irin spray dinnan, batasan lokacin da ta feshe fuskar binta shagala Dashi ba , wani irin ihun azaba ta saki da yasaka yaranta shigowa cikin d’akin daman suna waje suna gadinta kar Abla ta fito, yadda suka ga ta rike idanuwansa tana ihu yasa sukayi kanta , gashi an ware kid’a babu damar aji ihunta, d’aya daga cikinsu ce ta nufi abla , itama Abla ta bata kyakkyawan marin da yasa ta kusa faduwa cikin sauri kuma Abla ta hankad’ata ta fice a guje , idanuwan binta har jaja yake sabida azabar zafin turaran da yashigar mata ido, matan zasu bi Abla ta dakatar dasu “ ku rabu da ita , kar kuyi mata komai sannan ko aminiyata karku nuna mata komai , Indai nice Binta shagala kuma naci sunana sai na d’and’anata sannan sai ta zama baiwata a harkar duk lokacin da naga damar anfani da ita sai nayi kamar yadda engine baya gajiya haka zan dawo da ita , sai na mayar da ita karuwar Binta shagala “ ta karasa tana sakin wani shegen shu’umin murmushi.
Baiwar Allah , Abla kuwa a ‘boye ta fito daga d’akin binta shagala batare da ta bari wani ya lura da ita ba , duk ta rud’e gashi bazata iya fita ba sabida tana tsoran fita kamar lokacin data ta’ba tunanin kwana a waje wasu yan iskan mashaya suka so keta mata haddi da ‘kyar tasha , shiyasa jikinta har rawa yake ta nufi store din bayan gidan daya ta’ba kulleta, ga yunwa da kishirwa tana ji, haka tashiga cikin store d’in , sau’kinta d’aya ma akwia haske , zuciyarta fal tunanin rashin sallar isha’in da batayi ba , still da ta shiga cikin store din can cikin kayan shirgi ta ‘buya ga tsoro fal a ranta shiyasa ta runtse idanuwanta tana faman karanto adduar da yazo duk bakinta, ga wasu siraran hawaye da suke zubo mata a kuncinta.

*********
*************
WASHINGTON D.C
White House

Zaune ALICE take kan wasu irin ratsats tsun kujera , tayi crossing legs d’inta , ga wayarta da take dannawa cike da yanga , daga gefe gefenta wasu
End Ads