kuwa , “ don’t mind him ok? “, kafun ya d’auko wani siririn abu da aka rufe ya mi’kawa Charles , “ happy birthday once again !” Cikin farinciki charles ya furta “ thank you so much “, kara kallan little Charles yai amma bai ce masa komai ba, ganin prince na ‘ko’karin juyawa ne yasa charles yayi saurin dakatar dashi “ dude ina zakaje ? Ba’a dad’e da farawa ba , and your place is there “,ya karasa yana nuna masa wani ‘kayataccen wajen na musamman, “ yaya prince it’s time “, cewar little , kallan Charles prince yayi “ sorry ! Am going ,” ya karasa yana kallan little shima “ let’s go” ynxu ma da Sauri Charles ya ri’ko hannnun prince “ plx dude kar muyi haka , bai kamata kamar kai kazo waje na bakasha koda lemo ba , plx ko bazaka zauna ba atleast I will be happy idan yasha wani abun , “ bai jira jin me prince zai fad’a ba yayi dialing wata number “ ku kawo mun drink dinnan now “, Shima kallansa prince yayi “ don’t mind am going “, daga nan be kuma cewa komai ba ya kama hannun little suka fita , duk yadda wasu daga cikin friend din Charles Yaso su zauna amma daga prince har little babu Wanda ya zauna , musamman little da babu Wanda ya kalla a cikin su. Suna shiga cikin mota securities suka bar wajan, sai yanxu fargabar lefin da sukai ya soma yiwa prince yawo cikin zuciya, ro’kon Allah kawai yake Allah yasa yaya bobo be dawo ba .
NORTHWESTERN
WASHINGTON D.C
NUMBER ONE OBSERVATORY CIRCLE
cikin wani ‘kayataccen waje da ya hadu sosai da duk Wanda ya gansa zai gane mamallakin wajan ba ‘karamun mutum bane, wasu manyan mutane ne su uku cikin babban office d’in, daga gefe zaka ga flaq d’in U. S me girman gaske , zaune suke gabaki d’ayansu kan chairs d’in wajan , gabaki d’ayansu fararan turawane zaune a wajan kowa ka kalli fuskarsa zaka ga tsantsan tashin hankali, musamman yadda suke farare sai fuskokinsu ta ‘karayin ja na tashin hankali , d’aya daga cikin su sai faman duba wayarsa yake kamar me jiran wani abu, hasken da wayarsa ta soma ne yasa ya d’auki kiran da Sauri yana furta “ Charles how far?” Bansan me aka ce masa ba , sai kallan ragowar mutane biyun da yayi, yana kashe wayar, “ me ya faru?”, shiru be amsa masa ba “am asking you amma kayi mun shiru ansamu nasara ?”, gabaki d’aya wannan tanbayoyin da yake masa cikin turanci yake masa su “ sun bar Wajan , Charles ya fad’a mun basu zauna ba , and basusha drinks d’in da aka zubawa pills d’in ba “, da ‘karfi Wanda yake gabansu ya buga table d’in gabansa “ why? Why ?” Ya fad’a da ‘karfi , gabaki d’aya mutane biyun had’a baki sukai wajan furta “ sorry your excellency”, a zuciye ya kallesu “ wanene mutumin da ya d’aukar mun d’a? Ko wanene sai na sa yayi na dama , sannan aikin da yake ta’kama dashi zan sa a ciresa “ gabaki d’ayan su firgicine tattare akan fuskarsu Sabida zan tukan vice president da Suka ji , da ‘kyar mayor ya furta “ your excellency sir , wannan maganar ba me sau’ki bace , Sabida mun saka manyansu akan wannan case d’in , abune me matukar wahala “ , wahala? Cewar mutumin yana dakatar dashi “ karka manta ko wanene ni , har yanxu nine Vice presidents , ina da mu’kamun da ko ku zan iya cirewa balantana wani soja ? Wanene shi da zan zauna ina ‘bata lokaci ?ina bukatar ganin Nicholas nan da kwana biyu kawai “, governor ne ya kalli mayor , shima mayor d’in kallansa yayi , tunanin ta yadda zasu fad’awa vice president ko wanene ya saka a kama ‘ya ‘yan su suke , abun ba me sau’ki bane kamar yadda yake tunani duk da kasancewar sa vice president, governor ne yayi ‘karfin halin furta “ BIG BOSS”, wayar da his excellency ya d’auko ce ta su’buce ta fad’i, shima mai mai kalmar sunan “ Big boss “yayi jiyayi kamar wani abu ya tokare masa makoshi da yasa cikin sauri ya d’auki ruwa ko bi ta kan cups din wajan bebi ba ya soma sha, saida ya kusa shanye ruwan kafin ya ajje bottle d’in “ big boss ? Nicholas yana hannun big boss ? “ sai kuma ya mi’ke tsaye “ i can’t wait , ina bu’katar tattaunawa da his excellency , you can all go “ Mikewa sukai gabaki d’ayansu cike da girmamawa har sunyi nisa ya ‘kara dakatar dasu “ karku manta wannan zaman sirrine mu kayi daku sabida ‘ya’yan mu, kar ku kuskura wannan maganar tattaunawar ta fita har his excellency yaji “, yanxu ma cike da girmamawa suka amsa masa , suna fita cike da tashin hankali ya soma dialing wani number gabaki d’aya kalmar “big boss da aka fad’a ce ta fi komai tsaya masa , dan shi karan kansa yasan wanene big boss “.
🍃🍃🍃🍃🍃🍃
🍂🍂🍂🍂
ABUJA , NIGERIA__!
Tunda aka d’auke wuta nunfashinta yake sizing, sosai ta takure kanta a waje d’aya tana nan nunfashinta da yake barazanar fita daga ‘kirjinta, aduniya idan akwai abunda tafi tsoro shine duhu sai kuma soja , duk lokacin da waje yayi duhu hankalinta ba ‘karamun tashi Yake ba , hatta nunfashinta ya dinga barazanar d’aukewa sabida yadda ‘kirjinta yake d’agowa sosai ,yana d’aya daga cikin dalilin da yasa take tsoran soja musamman lokacin da take ‘yar ‘karama Umma asabe kullum cikin ‘ko’karin kai ta wajan soja take a cewarta su harbeta su yanka namanta subawa karnukansu, tun tana ‘yar ‘karama tsoran soja ya shiga zuciyarta, har zuwa yanxu tsoransu be fita a cikin ranta ba. Daga ‘kasa ta tsugunna ta kame jikinta waje d’aya ita kad’ai jikinta sai faman rawa yake , gashi ta kulle idanuwanta sosai ko saud’aya batayi gigin bud’e suba , babu abunda take cikin zuciyarsa sai addua , ita kanta batasan me take karantawa ba . Haka ta cigaba da zama cikin Wajan duhu na ‘kara mamaye Wajan alamar dare yafarayi sosai ,tun tana san ran ganin wani yazo wajan har ta fara cirewa, dataji d’an motsi kuma zata firgita ta sake rud’ewa, ga matsananciyar ‘Kishin ruwan da ta soma ji.
****A cikin gidan kuwa tun wajan ‘karfe 9 Arwa da ilham suke neman Abla amma basu gantaba, hankalinsu ba ‘karamin tashi yayi ba musamman da Suka san Abla bata ta’ba zama a waje , sai dai kome za’ai mata ai mata amma da Zarar Anfara kirar sallah Magarib take nufo gida , hatta uwar karuwai sai datayi mamakin rashin dawowar Abla , ga su zeenariya dasuke zugata akan cewa ‘karya kawai take musu idan ta fita da Alama wajan barikinta take zuwa tunda ga alama nan har wajan 12 bata dawo ba . Debeka ma rai a’bace so take kawai taga dawowar Abla daman ita ‘kiris take jira akanta , sabida mugun tsanar da tayi mata , bakomai ne ya ja hakan ba sai kyau Abla ga idanuwanta masu shegen kyau da ko ya ta ware maka su sai kaso ka ‘kara kallansu, ga diri da Allah yayi mata duk da bata da jiki amma Allah ya bata albarkatun kirji da hips , sai kuma ta samu ‘karin karamar ‘kugu da yawanci mutane suke wa la’kabi da shape d’in coca-cola , Allah ya rufa mata asiri ma Sabida hijabin da take sawa sabida hari da ake kawa mata, shiyasa ta kwammace zama cikin gidan karuwan tunda Allah yana tsareta. Rai a’bace uwar karuwai tasa a kulle mata gida sannan ta bawa debeka dama , da zarar Abla ta shigo gidan tayi mata mummunan hukunci sannan ko ruwa kar abata, lokacin da Arwa taji batun uwar karuwai hankalinta ba ‘karamin tashi yayi ba , duk wannan abunda ke faruwa husna da Aneesa basa cikin gida , da Alama ba anan zasu kwana ba Sabida kulle gida da debeka tayi sannan ta kora su Arwa ma kwancinsu, har zasu shiga sai ta tsayar da ilham , “ ke banan zaki kwana ba ki kwana a d’aya d’akin shirgin” cewar debeka sai kuma ta daka wa Arwa tsawa Alamar ta wuce , d’an guntun murmushin ciwo Arwa ta saki ta shige cikin d’akin shirgin da suke kira d’Ali , ita kad’ai ta takure kanta sabida rashin ganin Abla da batayi ba .
Debeka kuwa cike da mugunta ta ‘ki shigewa cikin d’aki , jira take taga ta inda Abla zata fito , tun tana zaman tsammanin jiranta har bacci ya d’auketa kan farar kujerar robar da take zaune . Ga baki d’aya har wajan ‘karfe 1 idan Arwa biyu lokaci ta tabbata kowa yayi bacci acikin gidan , haka kawai ta kasa runtsawa zuciyarta na raya mata ta ‘kara duba stores d’in shirgin gidan. A hankali ta fito daga cikin d’akinsu cikin san d’a hatta takalmin ‘kafarta da ya gama shan duniya saida ta cire sa , Sabida duhun da ke cikin falon da baya da baya Arwa take tafiya batayi auneba taji ta taka ‘katuwar ‘kafar debeka, da Sauri ta toshe bakinta tare da ‘buya bayan kujera , d’an motsi kad’ai debeka tayi , sai alokacin Arwa ta sauke ajiyar zuciya ganin bata farka ba , store d’in falon ta fara bud’ewa , a hankali kamar me rad’a take furta “ Abla ? Abla kina jina ?”shiru ba’a amsa mata ba , “ Abla kina jina ?” Nan ma still ba’a amsa mata ba ,sau biyu ta maimaita Abla kina jina , ganin ba’a amsa mata bane yasa ta rufo ‘kofar a hankali, store din gefen falon Arwa ta nufa , nan ma abunda ta fad’a a store d’in farko ta ‘kara maimaita wa , nan ma shiru babu Alamar da mutum a ciki, wani store Arwa ta ‘kara nufa , ko da taje a kulle yake ma Alamar ba’a shiga ba , sai a lokacin hankalin Arwa ya ‘kara tashi ganin da gaske Ablan bata nan , har ta juya wani tsohon store d’in gidan ya fad’o mata , duk da d’an tsoran da ya fara kamata haka ta nufeshi ta bayan kitchen ko tsoran wani abu ya faru da ita bataji, tana zuwa wajan taga ansa abu an kulle ta waje , a yanxu kam hope d’inta ya cire ganin store d’in a kulle , har ta juya ta kuma tsaya wa , haka kawai taga bazata iya barin Wajan ba sai ta duba dukda bata tunanin Abla tana ciki, a hankali shima ta bud’e wajan, bud’ewarta kuma tayi Daidai da ware idanuwanta da Abla tayi cike da tsoro amma ta kasa motsawa “ Abla ? Abla kina jina ?”, cewar Arwa , shiru ba’a amsa mata ba , “kara maimaita mata tayi nan ma shiru bata amsaba , juyawa tayi daniyar fita daga sama taji muryar Abla a dushe ta furta “ Arwa “, itama da Sauri arwa ta juyo cike da farin ciki take furta “ Abla ! Abla kina jina ? Ke ce ? Daman nasan bazaki ta’ba kwana a waje ba , kasa magana Abla tayi a hankali kuma ta fara mi’kowa Arwa hannunta , itama arwan cikin d’an hasken da rafito kamar na wata tafara baza hannunta har ta kama hannun Abla , sai da ta temaka mata sannan suka fito daga cikin store d’in , suna ri’ke da juna suka shigo cikin falourn ta inda arwa ta Fito zuwa d’akinsu , a hankali Abla ta furta “ ruwa “ , da sauri Arwa ta fita bata Jima ba kuma ta dawo d’auke da pure water a hannunta guda biyu, tana bawa Abla saida ta shanye guda d’aya , d’ayan ma sai da ta ‘bulashi Tasha rabinsa Sabida ‘kishirwar da ya kamata , sai alokacin ta fara dawowa daidai, hasken fitilar da ya kamane yasa Abla sakin murmushi harda ajiyar zuciya, kallan d’akin Abla tayi taga babu kowa sai su a hankali ta furta “ ina sauran?”, sai da arwa ta kwanta akan takwalinta ko tunanin hawa kan katifar d’azu bata yi ,” husna da Aneesa basa gidan nan , ilham kuma debeka ta canza mata d’aki”, jinjina kai abla tayi “, Abla ?”cewar arwa “ na’am “ ki kulle ‘kofar da kyau kizo muyi bacci sabida dare yayi sosai kar ciwan idanki ya tashi , Hakan kuwa Ablan tayi saida ta kulle ‘kofar sosai duk da d’akin ba fanka sai fitila haka sukayi baccin su fitila a kunne , su arwa har sun saba ma sabida tsoron duhu da Abla take shiyasa ko cikin dare ne basa kashe fitula saida su barta a kunne.
***
****** karfe 3:30am na safe wata irin azaba Abla taji a ‘kafarta cikin bacci da ya sata sakin razananniyar ‘kara tana bud’e idanuwanta , debeka ce tsaye a gabanta, yadda ta ganta tsaye ‘ki’kam sai data d’an razana ta , zafin da ta ‘Karaji a ‘kafarne ya ‘kasa ta sakin wani ‘karan har tana bada sautin “Auch”, ita kuwa debeka cike da zallan muganci take taka ‘kafar Ablan ,bayan takalmin ‘kafarta da tasaka med’an rud’u, har cije baki take wajan take ‘kafar, yadda taga Arwa na baccine itama cike da mugunta ta daddage ta d’akawa Arwa dukan dayasa ta farka a firgice, a yatsine debeka ta nuna mata kofa , cike da firgici ta mike tsaye tanayi tana tafiya tana waiwayo bayanta dan har cikin ranta bata ‘Kaunar abunda Akewa Ablanta, rashin gatan da basu dashine yasa ake kaskantar dasu kamar wasu bayi , duk da a wasu lokutan uwar karuwai tana danganta su da kaskantattu ko kuma jari. Kallan kallo Abla suke ita da Debeka , ita Abla har mamaki take tsanar da debeka tayi mata .ruwan hannunta me shegen sanyi ta watsa wa Abla tana shirin damko hijab d’inta , Abla ta d’angoce mata .’kara yun ‘kurawa debeka tayi zata bigi Abla, a wannan karan ma Abla ta ‘kara kauce mata dan ta gaji da abunda debeka suke mata. “ Dan uwarki har kin isa ki kauce mun ?”, kallar uwarki da debeka ta anbata wa Abla shine yayi mugun ‘bata mata rai , duk da har yau bata san ko suwanene iyayanta ba , bata sani ba suna da rai ko sun mutu, suna tunawa da ita ko sun mance da ita ? , amma duk da hakan ta’ki Jinin a ta’ba mata iyaye , zata iyayin hakuri da komai amma kar mutum ya kuskura yace zai zagar mata iyaye anan ne zai ga ‘bacin ranta . Yanxu ma a zuciye take kallan Debeka fararan idanuwanta kamar madara sun fara kad’auka , cikin sexy eyes da Allah ya halicceta dasu ta zubawa debeka kallo, kallo irin natsana,sai da ta d’auki kusan 30 seconds tana kallanta kafun ta janye idanuwanta gabaki d’aya tana mi’kewa tsaye , ko kallan inda debeka take a tsaye bata ‘karayi ba sai toilet d’insu da take niyar shiga , bata Ankaraba taji debeka ta janyo ta baya ta bugata da garu, duk da hakan Abla batayi mata komai ba ta ‘kara ra’bawa zata wuce yanxu ma cike da mugunta debeka ta janyo “ Dan uwarki…” ta’bata ‘karasa zagin da take so tayi ba taji saukar mari akumatunta, bata Ankara ba ta ‘karajin sautin wani marin , cike da mamaki ta d’ago dan ganin ko wanene ne ‘karar kwanan da yayi mata haka , mamakin ganin Abla tayi a tsaye rai a ‘bace “ Ni kika mara ? Yau zaki ci uban ki kuwa “, wani saban mari Abla ta ‘kara d’auke debeka da shi dama haka take da wuya mutum ya ‘Kure ta amma duk ranar da mutum ya kaita bango bata raga masa , rai a ‘bace Abla ta kalleta “ kin dade kina cutar dani , me nayi miki? Me na tsare ki ? Me yasa kika fi nuna tsanarki a kai na? Duk wannan be shafeni ba amma daga rana irin ta yau , ba debeka ba ko sumammiya ce ke kika ‘kara kuskuran anbatan iyayena sai na nuna miki Nima bani da mutumci , na so na dunga shange duk abunda kike mun , nayi hakuri da halayen ki, kin Musguna mun, kin hantare ni duka hakan be ishe kiba sai kin ‘kara da iyayena? Naso na baki girman ki na wacce ta girmeni amma naga Alama bakya bu’katar haka , daga rana irin ta yau , ni IBTISSAM bazan kara jurar ko wana iskanci ba , tunda so kuke na nuna muku asalin halin muzu ha mugani shege ka fasa ,” ta ‘karasa a zafafe dan sosai ranta ya ‘baci yau , debeka ta kaita bango iya tsawan shekara biyun da tayi a cikin gidan nan sun mata abubuwa da yawa amma ban da yanxu kuma , bazata ‘kara d’auka ba , bata kuma bi takan debeka ba ta shige ban d’aki,debeka da mamakin Abla ya gama cika ta kasa motsi tayi dan tun da Abla ta shigo cikin gidan uwar karuwai bata ta’ba d’aga mata murya ba sai yau , har wani d’an shakkar Abla ne ya shiga ranta lokaci d’aya , amma da yake ‘yar duniya ce kasa cewa komai tayi azuciye ta yi ‘kwafa ta bar d’akin har cikin zuciyar ta kuma tana mamakin Abla .
Itama Abla ko da ta fito daga toilet d’in alwala tayi Sabida abunda ya faru da ita jiya sai ynxu zata samu tayi sallahr isha’i, tana idar da sallar d’akin nasu ta fara gyarawa dukda ba wani datti yayiba amma duk da haka sai da ta gyara kafun ta fito falon. Kamar kullum bakowa a falon yau har debeka bata ciki, cikin sauri sauri Abla ta fara gyara falon Sabida tanaso taje gidan ruwa , tana gama gyarawa d’akunan sama da ‘kasa ta gyara gabaki d’aya har da band’akin da kullum baya gama gajiya da ‘kazanta musamman condum da take yawan kwasowa ko wana d’aki, kome takeye cikin Sauri take yinsa har lokacin kuma bata ga kowa na cikin gidan ba .lokacin