a wjan , ba ‘karamin billions ya kashe akan wayar ba sabida da kansa ya bada idea din yadda za’ayi masa ita, sosai Kenta ya wuce musali, ‘karin ban sha’awa bayan ninkata uku da akeyi har Çan za tsarinta ake ta yadda kome yake cikin wayar zai iya ganin sa gaba da baya komai na cikin wayar ana gani, ko kuma aka rage mata tsahonta, iya had’uwa wayar ta had’u, yadda yake kallan wayar hakan ya bawa green eyes din idanuwansa fitowa sosai ga red lips dinsa da ya d’an ciza a hankali ,sosai lokaci zuwa lokaci yake shafa girarsa guda d’aya da alama habit dinsa ne wannan.
Sai daf da kiran sallahr asuba ya ajje wayar tare da nufar ‘kofar d’azu, bai jima sosai ba kamar d’azu , kamshin turaransa har ya kama ko ina sabida bala’in dad’insa, ba shigar d’azuce a jikin saba yanxu sanye yake cikin white d’in riga da ta d’ame damtsen hannunsa kamar zasu fasashi su fito waje , sai farin dogon Wanda sa shima fari kirar kamfanin Armani, sosai farin fatarsa ta fito , hannunsa d’aya ya saka Wajan girarsa ya d’an sosa kafun ya sauke hannunsa, fuskarnan kamar hadari babu fara’a Sam a tattare dashi ko kad’an , Daidai wjn shan iska d’akin ya tsaya har yanxu sojojin suma suna nan a tsaye suna gadon gıdan, har aka fara kiraye kirayen kiran sallah .
**** yau hakanan prince shine ya fara tashi tun kafun yaya bobo ya tashesu, saida ya tabbata yayi wanka sannan ya Tashi little shima , yau be ‘bata lokaci ba ya mike shima ya shiga Wanda duk iskancinsu basa so jam’i ya wuce su, shiyasa yau da wuri suka shirya , Sabida sanyin asuba kaya me kauri sosai little ya saka sabida sanyin da yake ji, su fito daniyar tashin bobo da uncle suka tarar da bobo suma sun fito shida uncle , with a suprise bobo ya furta “ addua akai muku kuka tashi yau dawuri “, dariya little ya saki yana nuna masa ya prince “ yaya bobo , shine fa ya fara tashi yau dawuri “, da mamaki uncle da bobo suka kalli prince , shi kuma hararan little ya ke yi “ addua kayi ka Tashi da wuri?” Cewar bobo , kamar zaiyi kuka ya furta “ please yaya bobo ka bari” yanxu ma dariya little ya kara saki yana sakar masa gwalo “ lokacina tafiya fa” cewar uncle , jinjina masa kai bobo yayi “ yes uncle ! But ku ‘kara 5 minutes tukunna “, lokacin sallar za’a karawa lokaci?” Cewar uncle yana kallansa da mamaki, bobo murmushi kawai ya saki ba tare da ya ce komai ba , elevator din da aka bude ne gabaki d’aya uncle , prince , little Suka mayar da kansu waje cike da shakkar abunda zasu gani, banda bobo da ko juyowa beyi ba sabida sanin ko wanene, cikin ta kunsa ya fito daga elevator fuskarsa kwata kwata ba annuri, prince be san lokacin da bakinsa ya fara furta “ Innalillahi wa’inna ilaihi rajiun” , Sabida yadda zuciyar sa ta buga bummmm yasan tabbas yanxu dole ya shiga taitayinsa ,kafun big boss ya canza masa kamanni da Sauri ya toshe bakinsa , yana zare ido , uncle ma da shock da mamakin lokacin da ya dawo ya hana sa motsawa, sosai jikin little ya fara rawa yana ‘ko’karin magana amma ya kasa sabida tsananin murna da yake ciki, da’kyar bakinsa ya iya furta “ yaya big boss dina ?” Sai kuma ya kalli yaya bobo, ganin ya jinjina masa kai yasa da Sauri ya ‘karasa wajan big boss da yake tunkaro inda suke ,be tsaya ‘bata lokaci ba yayi hugging d’insa ,cikin kuka little ya furta “ nayi missing dinka sosai, plx kadunga tafiya dani”,sai kuma ya soma kuka kamar wani ‘karamin yaro.
********
ABUJA NIGERIA
A hankali Abla take shash’she’kar kuka gudun kar Binta shagala ta fad’awa uwar karuwai abunda tayi mata , ita kuma ta saka su zinariyya su no mota shiysa tayi zamanta a wajan , ba tsoron binta shagala ko uwar karuwai ne yasa ta kuka ba , zafi da zuciyarta take matane yaşa take kuka , ji kanta take kamar acikin wata ‘kuntacciyar rayuwa , batasan
iyayenta ba , bata danginsu ba , bata san a ina suke rayuwa ba , suna mace ko a raye ?, suna tunawa da ita ko sun mata da ita ? So? Bata san shi ba , batasan ya yake ba, abu d’aya ta sani, tun ta sowarta har zuwa yanxu batasan wani abu wai shi gata ba ko farin ciki , abu d’aya ta sani , ta taso cikin kuncin rayuwar, rayuwar da tunda tayi wayo ake mata gori ita da wacce ta tausayawa rayuwar ta lokacin da take jinjira , matar da ta sadaukar da farinciikinta tana kula da ita duk da kasancewarta karuwa. A wannan duniyar barıkin ta koyi abubuwa da yawa aciki,abu d’aya ta sani , in dai kana bukatar abu to tabbas zaka mayar da saka mako,a duniya idan akwai abunda Abla ta tsana to tabbas karuwanci ne na farko, tun tana tunani har baccin wahala ya d’auketa a yadda take a cunkushen nan.
A cikin gida kuwa sabida bariki irin na binta shagala ko a fuska bazaka ga alamar ‘bacin rai tattare da itaba duk da abunda Abla tayi mata ya mugun ‘bata mata rai, amma da yake ta san ta kan duniyanci fuskarta cike take da Anna shuwa a ciki, a maimakon Abla da Husna ta tafi d’aki ganin yadda take binta da kallo tun d’azu , har dare ya fara ratsa wa babu Abla babu alamarta , Allah sarki Arwa tun da taga dare yayi sosai bata ga Abla ba ta kasa zama sai faman jiran tsammanin dawowarta take, shiru har wajan shad’aya sosai hankalinta ya Tashi ta kara komawa d’akı ko zata tarar da ita amma shiru babu ita babu alamarta , sai ma Anee dake zaune kankatifarsu sun bud’e ‘kartuwar gashshiyar kaza sai ci suke ga manya manyan kwalin exotic d’insu , da kallo suka bi ta Dashi ganin kamar akwai da Muwa a tattare da ita , ta’be baki ilham tayi kafun ta furta “ ke kuma lapiya kamar wacce akai wa mutuwa zaki shigo mana a furgai furgai haka ?” , bansa Arwa mata , sai kum ta mayar da kallanta kan Anee “ Anee bakiga Abla ba ?, tun d’azu nake jiran ganin ta amma haryanxu babu ita babu alamarta..”, bata ‘karasa ba sabida dariyar da ilham ta kwashe da ita “ Sabida wannan abun ne wai kika burkice haka ?, nasan tana can tana kuka tunda abunda take kurin’boyewa Anta’ba zanso naganta nima ba “, kallan me kike nufi Arwa ta bita dashi, yanxu ma wat dariyar ta ‘kara kwashewa da ita “ bani nakar zomanba fa , rataya aka bani,rayuwar kuce dole sai kun gur’bata kamar sauran , dan dole ki zabi d’aya ko ki fara shaye shaye ko ki fara karuwanci , kin ga Anee yanxu shaye shaye ya bi jikinta, husna ta za fara shiga hanyar karuwanci, waccen banzar da ita kuma kinga sai ta zama karuwar gida kawai…”, bata ‘karasa ba sabida yadda Arwa ta daddage ta buge bakın ilham da harsaida tayi ‘karamin kara Sabida taji zafin dukan , zata mike aneee tayi saurin ri’ko “ ki manta kawai , kiyi hakuri mana “, fusge hannunta ilham tayi tana nuna Arwa da yatsa “ tabbas bakisan wacece ni va shiyasa kika tafka wannan kuskuren , ada inashare duk wani haukanku Sabida na samu biyan bu’kata ta amma banda yanxu , Wallhi dukannan da kikai zaki gane shayi ruwane , Indai nice ilham “, tsaki Arwa ta ja duk da yadda take da tsoro yau saida ta tankawa musu “ Menene kuma bamusani ba na halin naki? Kina tunanin bansan cewa labarin da kika babu nacewa iyayenki sun mutu duk karya ne ? Ko kuma siyarda mutumci na da na Abla da kuke shirin yi? Ko muna furta Anee da har kikai sanadiyar sata ta fara shaye shaye , duk da husna kwad’ayi da san zuciyar ta ne ya ja mata wannan ba’kar rayuwar amma kefa? Komai ma rayuwarki ‘karya ce “ batare da damuwa da maganganun Arwa ba ilham ta ta’be baki , Aneesa kam sai faman lumshe ido take sabida maganin da ta sha yanxu da alama batajin me suke cewa ma “ bakiyi ‘karya ba , duk abunda kika fada hakane sabida banasan naganku cikin farinciki, inaso naga rayuwarku ta gur’bata, inaso naga rayuwarku ta gur’bata kamar yadda tawa take a gur’bace, sau da dama na so kawar dake Sabida idanu da kika samun har kike ‘ki’karin fad’awa abla abunda kikaji muna tattaunawa da uwar karuwai, amma shegiyar Ablar nan kullum cikin bayyana take , maganar da kikaji Hakane,eh Hakane , ni ba nazo nan gidan sabida gata ba , nazone Sabida na lalata rayuwar yan mata masu irin shekaruna kamar yadda kwartan Dije yar kwal wato mahaifiyata yake tan haddi na , yasa na koyi bariki , sanin cewa uwar bariki aminiyar Dije ce yasa nazo gidan nan , kuma nayi sa’a na samekun duk da gabaki d’aya kudin gidadawane marasa tunani kun kasa fahimta , duk da ibtissam taso fahimtar wani abu amma na wuce tunaninta “, ta fad’a tana Kallan Arwa da ta gama shiga shock din maganganun Iham “ kınsan Menene abun burgewar, tun ina 12 years na san d’a namiji sannan yanxu a rayuwa ta bani da wani babban buri kamar naga lallace war Abla, wallahi na tsaneta, Sabida duk cikin gidan nan tafi kowa kyau , tafi kowa gashi, tana da jiki me kyau , sosai hakan yake ‘bata mun rai Sabida banaso taji dad’in rayuwa , na fiso taita wahala a haka karta samu farinciki”, idanuwanta akan Arwa ko tsoran wani ya shigo batayi ta cigaba da maganar “ bawai na fada miki maganan nan dan naji tsoroba, na fad’a miki abunda ya kamata ki sani sannan kema ki shirya , Indai ni Jinin Dije Yar kwalce “, ta karasa tana bin Arwaa da kallan kaikai ce tai ficewarta daga d’akin tana barin Arwa da Tashin hankali , hannu ta d’ora a sama tana fad’in “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un da ma duk wannan plan din ilham ne ? Shiysa duk lokacin da Suka kwanta suna tashi zasu ga bata nan” tunani Arwa ta somayi , ta fad’awa Abla ko karta fad’a mata , tasan Abla bazata ji dadi ba musamman yanxu da batasan halin da take ciki ba shiysa tayi wa kanta al’kawarin bazata fad’a mata va . A d’akın ta zauna tana jiran tsammanin ganin Ablaa , tun tana saka ran ganinta har bacci ya fara fuskarta, lokaci d’aya kuma wani wahalallan bacci ya d’auketa.
Kiran sallah asuba ne ya farkar da Abla daga baccin da ya d’auketa, bakinta d’auke da adduar tashi daga bacci da bud’e idanuwanta , idanuwanta har sun ri’ke , sosai taji zafin wuyanta sabida yadda tayi bacci, tasan yanxu su zinariya suna ta nemanta ganin bata nan , a hankali ta fito daga cikin store din, duk da ydda zuciyar ta take bugawa hakan be hana ta tunkari gidan ba , tana shiga babu kowa. Falon , kai tsaye d’akinsu ta nufa nan ma Arwa da Aneesa kawai ta tarar cikin d’aki, kai tsaye toilet ta nufa ta tsarkaka jikinta , sai datayi sallar isha’i da asuba tana kaiwa Allah kukan ta kafun ta tafi Arwa da Aneesa akan su tashi suyi sallah , gabaki d’ayansu da farin ciki Suke kallanta har da had’a baki wajan furta “ kindawo?” Kai Kawai Abla ta d’aga musu dan ko kanta bata san d’aga wa , suna shaf shaf suka tashi sukayi sallah dan Abla ce kawai me tunatar dasu sallah arayuwarsu.
Har ‘karfe tara babu Wanda ya shigo d’akin , itama abla bata fito waje ba Sabida zafin da wuyanta yake mata, amma abun mamaki yau gabaki d’aya yaran binta shagala ne suka gyara ko ina na cikin gidan harda kawo musu abunci dukda abunda tayi wa binta shagala, haka kurin bata yadda da abincin ba shiyasa bataci ba ta barshi, tana fitowa falo suka ci Karo da binta shagala taji uban ado, yadda abla take kallanta itama ita take kallo fuskarta cike da murmushin bari ırin nata “ baby ba gaisuwa ?” Cewar binta shagala , banza alba tayi mata tayi ficewarta daga gidan , girgixa kai Binta shagala tayi tana bin hanyar da Abla ta fita da kallo, kai tsaye d’akin uwar karuwai ta nufa, ko sallama batayi ba ta banka kofar d’akin ta shiga , lokacin da uwar karuwai take cin chips da Kwai abunta , tana ganin binta ta Soma washe mata baki “ kina rayuwa cikin yara ‘kanana bakyaşamın kud’i ta dalilinsu? To Menene anfanin barikin naki? Hajiya duniya ta bun’kasa yanzu da yara zaki samu ma’kudan kudin da har zakiyi ta juya su san ransu, ya kika ganni? Kinsan ba ‘karamin kud’ine ya zauna munba, ta ‘karasa tana juya Orobo (lukuti)d’in jikinta , samun waje uwar karuwai tayi tana jinjina maganar binta shagala kafun ta saki a jiyar zuciya “ban’ki ta taki ba binta amma taya kike tunanin za a fitar da yaran batare da mutane sun Ankara ba ?, dan tabbas inaso na dunga fancanawa cikin daula “, anzo inda take so shiyasa ta saki wani shu’umin murmushi tana kallan kawar ta “ wannan ba matsala bane, zan temaka miki amma mutum d’aya zan fara fitar miki da ita , kina zaune zaki samu 20million”, zaro ido uwar karuwai tayi tana furta “ 20 million fa kika ce ? “, kanta binta ta jinjina mata alamar hakane , da Sauri uwar karuwai ta furta “ na Amince amma wa za a fara fitar wa ?” Yarinyar da na d’auka jiya “, cewar binta , katseta uwar karuwai tayi ta hanyar furta “ kardaki kice Abla kike magana ? Kinsan taurin kan yarinyar nan kuwa ? Cikin ‘kan’kanın lokaci zata ‘bata mana shiri me zai hana ki d’auki wata a cikin su ga Arwa ga Aneesa dan bazan iya saka ilham ba Sabida yar Dije kwalce kinsan kuma bala’inta itama cikakkiyar yar barikice kema kinsani”,murmushin gefen baki binta ta saki tana d’age ka fad’a” tun da baki Shirya ba ai shikenan “, zata tafi uwar karuwai tayi saurin dakatar da ita ganin ga samu ga rashi cikin saku wa ta furta “ na amince amma taya za a fitar da ita ?yarinyar ba ‘karamin brain ne da ita ba “, ynxu kam binta kyal’kyale wa tayi da dariya kafun ta ciro wani farar powder a Leda tana nunawa uwar karuwai “ duk kwakwalwarta da ilimin ta ai bata Kai wannan aiki ba ko?” Ta ‘kara tana d’aga coccaine din hannunta . Gabaki d’aya dariya sukai saki “ shegiya binta baki da dama duk wani shu’umancina kin dameni, shiyasa nake san harika da irin ku “, cikin yanga binta take d’ad’d’age fuska da hura gajeren hanci ita a dole ana kod’ata .
**********
************
KANO
1:30pm kid’ane yake tashi a falon sosai sabida volume din murya da Baby ta ware sosai sai kace gidan shed’anu ga wani irin ‘kara da ya karad’e ko ina , baby ko ajikinta ko d’an kwali babu akanta sai gashin kanta da ta tufke jikinta sanye da ‘kananan kaya Riga da wando ga head phone d’inta da ta saka a kunne amma duk da haka sabida neman rigima da Eshaal ta ‘kara waye volume , ko mintuna 5 bata ‘kara ba tana rawa Eshaal ta shigo falourn rai a ‘bace , magana take wa baby amma kamar ma bata san tanayi ba shiyasa taji haushi ta kashe kid’an , azuciye baby ta tsaya daga rawar da take tana bin Eshaal da shigo falourn sanye da hijab da alama sallah zatayi ko take shirin yi “ uban wa yace ki kashe mun kid’a ? Ke wace irin ballagazace wai ? Nace ki dena shiga rayuwa ta amma sabida maita sai kinshiga, karkiga mun had’a dad dake ki fita idona “, cewar baby, guntun tsaki Eshaal ta saki “ ke kullum baby wai sai kin nemo abun rigima? Karki manta sallah fa akeyi , be kamata ai kisaka kid’a lokacin sallah ba , ko ke bana Tuna’nın kinyi sallahr, sannan idan dole sai kinji wa’kar sai ki kunnashi a d’akin ki mana ?”, a kufule baby ta kalleta “ idan kece kika kar’barmun sallar karki karba , da nayi sallar da banyi ba ai ba kabarin mu d’aya ba , stupid kawai, wareey daga nan wajan “, ta karasa tana d’aukar remote , fusge remote din Eshaal tayi “ wallahi bazaki kunna ba , kinsamu ana bin ki ta laluma amma ke sam bakısan annabi ya kafuva”, itama hannu baby ta saka zata karbi remote din Eshaal ta hanata, lokaci d’aya suka soma kokawa ran baby ba ‘karamun ‘baci yayi ba , shiyasa ta daddage ta gantsarawa Eshaal cizo a wuya da yasata sakin gigitaccen kara dan mugun cizo baby ta kai mata , karar da yasa momcy da ke waya a d’aki sai da taji amma ko motsawa batayi ba balantana ta fito ta duba abunda ke faruwa ,AMMA kuwa lokacin da Eshaal tasaki ‘karar tana cikin band’aki tana wanka, itama azuciye Eshaal ta cijeta da yafi wannan baby tayi mata , itama ‘karar ta saki dan sosai taji zafin cizan, a wannan karan karar baby da momcy ta jine yasa ta kashe wayar tare da barin dakinta Daidai lokacin da baby ta d’auki wani abun decoration ta kwalawa Eshaal , lokaci d’aya goshinta ya soma zubar da Jini , zata Shako baby momy ta shigo falon , cikin kukan shagwaba baby ta nuna mata cizan