x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 57 - IBTISSAM BOOK 1

  • 168001 words
  • 171000 words
  • Out of 200864 words

Category: Romance Story +18

Views 272

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
furtawa Abla “ Get lost “ da Sauri Abla ta mi’ke ko kallan inda yake batayi ba tayi wucewarta, sai da ta shige d’aki sannan kukan da take so ya zo mata, wato in mutuwa zatayi ma taje ta mutu ?” Wannan maganar tasa sosai ta ba’kanta mata rai shiyasa bata ‘kara Tuna’nın sakkowa ba tayi zamanta a d’aki .
Sai da Bobo yaga ‘bacewar ta ya kalli Big Boss da ya mi’ke tsaye “ Haba please? It can hurt her more ! Why please ?” Dakatar Dashi Big Boss yayi ta hanyar furta “ Am out “ yana kai ‘Karshen maganar sa ya bar falour shima . Gashin kansa Bobo ya ta’ba , a hankali ya furta “ why please ?” ‘Dan karamun murmushi Uncle ya saki “ it’s okay Bobo , yasan yanzu kai ma akwai wajan da kake san zuwa , inasan kumar maganar for now ! Okay ?” Kansa Bobo ya jinjina masa shima kafun ya bar falourn, kallansa Little da prince sukai “ uncle yanzu shikenan guy d’in can ya ci bulus?”d’an harararsu uncle yayi lokacin da yake mi’kewa , “ Me isa baku tanbaye su ba har suka fita ?” Haba mana uncle “ cewar prince “ nace abar maganar nan “ daga haka ya bar falour , jijjiga kai prince yayi “ you know what Little ? Inda yaya zai bani Victor da Anthony ko hmm” a hankali Little ya furta “ Sabida duk a jikin sojojin gidan right side d’in Yaya Big Boss sun fi kowa iya hoto ki ?” Kansa Prince ya jinjina masa .
Yau gabaki d’aya basuyi hira ba sabida basa cikin good mood d’insu, kowa d’aki ya koma abunsa, har dare Abla tana d’aki sai da little da prince suka lalla’bata sannan ta iya cin abincin da ko spoon 10 be kai ba, still tana ‘ko’karin komawa su little suka hanata sabida yadda gabaki d’aya ta sauya musu ko magana batayi sai dai ta amsa musu da eh ko ah’ah,ko 9 batayiba Abla ta koma d’akin dan ko san kallan Big Boss yau bata sanyi.
Har wajan karfe 12 idan Abla biyu abunda jabcon yayi mata yayi mugun tsaya mata arai , ba shi kad’ai ba , hatta LG ta gane ta , wani irin tsanar tane ya dar sar mata a zuciya na ‘ka zafin karuwanci da sukai mata , duk lokacin da ta kulle eyes d’inta hango yadda mutane suke kallan hotan da aka sa fuskarta a jiki take. Murmushi Abla ta saki me ciwo tare da d’aga hannunta sama “ Allah kafi kowa sanin Daidai da kuskure, Allah kana ganin halin da baiwar ka take ciki , Allah na ro’ke ka , ka saka mun ta hanyar da basu ta’ba zato ko tsammani ba , Allah na ro’ke ka duk Wanda yake da hannu akan sharrin da akai mun Allah ka saka mun “ tanayi tana kuka , har wajan ‘karfe d’aya idan ta biyu , cikin ‘kan’kanin lokaci zazzafan zazza’bi ya rufe ta , da ‘kar bacci ‘barawo ya d’auke ta.

Washe gari ma da zazzafan zazza’bi Abla ta tashi amma tana iya bakin ‘ko’karin ta wajan ‘boye hakan, komai cikin sanyi take yinsa, ji take kamar kar taje makarantar Sabida bata san wani irin fassara za’a yi mata ba , cikin Sauri take yin komai har ta gama shiryawa cikin uniform d’inta , amma duk Wanda ya kalli face d’in ta zai ga rashin walwalar dake tattare da ita.

Tana sakkowa down stairs ta tarar da Little da Prince har sun shirya mata break fast d’inta , cikin d’an ya’ke Abla ta furta “ Yaya prince ina kwana ? Yaya little ina kwana ?” Yadda Little yaga tana magana cikin cool voice ya furta “ Bazaki fasa zuwa makarantar nan ba kuwa ? Are you okay ?” Murmushi Abla ta sakar masa kad’an “ I can manage , muna da speech yau ne “ kansa ya Jin kina mata kamar yace ta hakura sai kuma yayi shiru , dan dole suka sa ta ci abinci duk da yadda tace musu a ‘koshe take , da zasu tafi makaranta ma bata had’u da su Bobo ba , har suka kama hanyar idanuwan ta a rufe suke bata san lokacin da aka ‘karaso ba saida Little ya d’an ta’ba ta , “ please nace ki dena damuwar nan kinji ?” Kanta ta jinjina masa yanzu ma , wani black face mask ya mi’ko mata “ zaki iya sawa a face din ki in kina so “ d’an ‘karamun ajiyar zuciya Abla ta saki ka d’an ko ba komai face mask d’in zai kare mata face d’inta . Kamar kullum waving sukai wa juna suka tayar da motar suka tafi ita kuma ta nufi class d’insu . Tunda ta shigo ake binta da kallo ga wani ‘kus’kus da suke yi suna nunata , wasu zafafan hawaye taji suna ‘ko’karin sakko mata tayi saurin mayar dasu , harta ‘karasa seat d’inta babu Wanda ta kalla , tana zama Eshaal ta ri’ke mata hannunta “ kiyi hakuri nasan sharri akai miki amma Allah zai saka miki kinji ?just be you , okay ?” Kanta Abla ta jinjina mata ko bakomai ta samu wadda ta yadda da ita “ Nagode “ cewar Abla , itama fanan seat dinta tazo , ita da Eshaal suna so ta sake kamar da , amma zazzafan zazza’bin da take ji ya hana tayi magana sai dai ta jinjina musu kai ko kuma ta furta “eh ko ah ah “ shine kad’an abunda bakinta yake iya furtawa , gashi ko karatun abunda zatayi a speech bata karanta ba Sabida abunda ya faru da ita jiya. Ba’a d’au 2 minutes ba Baby ta shigo cikin class d’in, Daidai seat din da su Abla suke ta nufa , da Sauri Eshaal ta had’e hannayen ta alamar ro’ko, hararar ta Baby tayi tana kallan Abla, a bazata ta fusge mask d’in Abla cikin Sauri Abla ta sunkuyar da kanta ‘kasa , karo na farko da Baby taji babu dad’i dan anyiwa mutum abu, “ ‘boye fuskar ki da kike bashi zai hana mutum ya yadda da abunda aka gani ba , ko ma su wanene sukai miki Haka raunin ki suke so kamar yadda kike ‘ko’karin nuna wa yanzu, bance sai kin yadda da maganganu na ba , kwanda ki fito ki nuna wa ko wana d’an iska daidai kike dashi , ta hakan ne zaki iya kwatar kanki a hannun kowa “ tana kai ‘karshen maganarta ta juya , d’an ’karamin murmushi ne ya fitowa Abla ,” Na gode “ shine abunda ta iya furtawa Baby , kanta Baby ta jinjina mata kafin ta harari su Eshaal da suka saki baki suna kallanta , sosai suke kallanta da tsantsan mamaki , karo na farko da Baby ta fad’i maganar arziki, shiyasa cikin Sauri fanan ta koma Seat d’inta . Har lokacin kuma ba’a dena gulmar Abla ba , ga zazza’bin da yake ‘ko’karin cin ‘karfin ta , duk yadda Eshaal da fanan sukayi da ita akan suje clinic ta ‘ki yadda. Har 9am suna class babu teacher din da ya shigo sabida speech din da za’ayi na seniors, wani irin fargaba Abla take ji a ‘kasan zuciyar ta ,babu abunda take sai adduar da ta zo bakinta. 9:40am aka bu’kaci duka students suje babban filin hall din da za’ayi program din , duk yadda Eshaal tayi da ita suje Abla ta kasa zuwa , zuciyarta ba dad’i da kyar ta hakura ganin time na tafiya suka nufi hall din , duk Wanda ya ganta sai su fara magana kasa kasa ko su dunga nuna ta , Daidai zasu shiga hall din suka tarar da Mr jabcon a tsaye sai faman murmushi yake wa Abla, a bakin ‘kofar ya tsaya ta yadda dole sai sun ra’bashi tukunna , kallan da yake bun Abla da shine ya ‘kara tunzurata, Daidai zata shiga cikin hall d’in yayi ‘ko’karin rike mata kwankwaso, bata damu da d’aliban da suke wuce ba wa , ta d’aga hannunta da iya karfinta , ta tsinka masa mari, tare da tofa masa miyau tayi wucewar ta . Wannan abunda tayi masa ne ya ‘kara tun zura jabcon, shi kad’ai sai jijjiga kansa yake yana ‘kwafa , wayar sa da ta d’anyi ringing ya d’auka, banyi me aka ce masa ba sai wata shegiyar dariya da ya saki lokacin da yake komawa gefe , “ kamar yadda aka shirya plan , komai yana kan shiri nan da ‘yan mintuna kad’an aikin ki zai kammalu kamar yadda kike bu’kata” yanxu ma banji me aka ce masa ba sai wata shegiyar dariya da ya ‘kara saki kafun ya furta “ zan turo miki da account din yanzu “ sai d’iff ya kashe wayar yana shiga cikin hall d’in.

Tunda Suka shiga cikin hall d’in yan set d’in su Abla suke kallanta , gabaki d’aya ta tsargu da irin kallan da suke bunta dashi, har suka zauna a Inda aka tana dar wa yan set d’insu waje , daga bayan ta Abla taji d’aya daga cikin yan Ss2 tana nuna Abla , cikin ‘kasa ‘kasa da murya ta furta “ she’s a prostitute” da mamaki d’ayar ta gefenta ta furta “ no wonder kullum take Simi Simi Aushe karuwa ce at her ages” da Sauri Abla ta damtse idanuwanta dan gabaki d’aya taji maganganun su , itama Eshaal Sauri ri’ke hannun Abla tayi ganin tana ‘ko’karin tashi “ Na fad’a miki ki dena saka irin wannan abun a ranki , koma wanene yake da hannu akan abunda sukai miki Allah bazai barki ba , idan kinji sauyi cikin zuciyar ki toh kiyi addua kinji ?” Kanta Abla ta jinjina mata Batare da tace komai ba , tunda Suka zauna jabcon ya zuba musu ido shikad’ai sai murmushi yake yi abunda duk da marin da Abla tayi masa lokaci kawai yake jira . Ba’a d’au dogon lokaci ba aka fara gabatar da program din da za’a yi , Abla gabaki d’aya hankalin ta da gangan jikinta basa tare da ita shiyasa bata san speech d’insu yayi ba . Sunan Eshaal da aka fara kira ne ya fad’ar mata da zuciya dan tasan daga Eshaal sai ita a speech d’in. Cikin nutsuwa da kwarewa Eshaal ta fara gabatar da speech din ta gwanin burgewa lokaci lokaci ana ta fa mata har ta kammala , wata malama ce ta furta “ the second person is Ibtissam Mohammed Al-Taufeeq “ daram Abla taji zuciyarta ta buga da ‘karfi ,’kafarta tayi mata sanyin da nazata iya me’kewa ba , sai da aka kusan kirata sau uku sannan ta iya mi’kewa bakinta d’auke da addua . Mr jabcon na ganin Abla na nufar Inda zata gabatar da speech shima yayi Sauri nufar wajan , Abla na ‘ko’karin fara speech d’in ta Mr jabcon yayi saurin taran nunfashinta , cikin d’aga murya ya furta “ am so sorry da na katse muku speech din nan da ake yi , amma akwai babban abunda ya kamata kusani yanzu amma sai d’alibar nan ta gama speech d’inta , please ku tafa mata” gabaki d’aya kuwa aka hau tafa mata musamman Wanda suke san hotunan jiya zai rabawa Malam suma , Eshaal da Fanan ne kawai basu tafa ba sai Baby itama da bataji dad’in abunda akwai Abla ba dukda itama tana mamakin me yasa ta damu akai ma . Abla duk da tasan wula’kanta ta yake so yayi hakan be hana lokaci d’aya ta dake ba ta fara gabatar da speech d’inta yadda ya kamata cikin tsan tsan turancin da ya burge kowa , tana gamawa gabaki d’aya hall d’in ya d’au tafi. Zata koma Mr Jabcon yayi saurin dakatar da ita , yana kallan gabaki d’aya mutanan cikin hall d’in, Daidai lokacin da yake furta gabaki d’aya kowa da kowa ya kalli Abla wasu irin manya manyan motoci ba’ka’ke suka danno kai cikin makarantar da mugun gudun gaske , Abla dake cikin hall da gudu ta fito sabida bazata iya kallan cin mutum cin da yake ‘ko’karin yi mata ba, Eshaal da fanan ma cikin Sauri suka biyo bayanta suna ‘ko’karin dakatar da ita , Daidai lokacin da take gugu a dai dai lokacin wasu manya manyan combo cars suka danno kai cikin makarantar, su Abla suna Barin wajan ratsatstun Ba’ka’ken jerin motocin nan sukai parking Wajan babban harabar hall d’in, babu abunda ake ji sai diran motoci , yadda combo cars din suka shigo ajere sai ya burge mutum , lokaci d’aya motocin da akalla zasu kai 15 suka yi slow down sukayi parking, cikin Sauri motocin farko suka fito da Sauri sanye da kayan sojoji ga wasu irin makamai a jikinsu , dayawa daga student d’in da suka fito kallan motocin suke daga gefe kowa yana so yaga wanene a cikin motar , cikin Sauri gabaki d’aya sojojin cikin combo cars d’in nan suka fito gwanin burgewa ko wannan su sanye da kakin sojoji da bindugu a jikinsu, kafun kace me gabaki d’aya motocin sun zagaye farar Bugatti La Voiture Noire d’in da ke tsakiyar su, cikin zafin nama Victor da Anthony suka fito daga gaban mota, da Sauri sojoji suka yi layi , abun sai gwanin burgewa , cike da tsantsan girmamawa Victor ya bud’e door d’in bayan farar Bugattin, kusan tsawan mintuna 3 kafun mamallakin motar ya fito da farar ‘kafar sa me sanye da ba’kin Gucci loafer , ga farin wandansa d’aya fito me shegen laushi, be d’auki ko cikkaken mintuna ba gabaki d’aya ya Fito daga cikin motar cikin fararan suit da sukayi mugum amsar sa , fuskar sa sanye cikin wani black sunglasses da yayi matukar ‘kawata face d’insa , hatta gyaran gashin kansa na dabanne yau , yadda fuskarsa take a had’e cikin ba’kin glass din idanuwansa sai ya matu’kar girgiza mutum ba kowa bane face Big Boss da fuskarsa babu ko d’ugon fara’a akai, cikin Sauri sojojin suka soma tafiya sai yazama kamar Big Boss aka saka a tsakiya , ga Victor da Anthony da suke taka masa baya , tun da ya fito maza da matan makarantar suke san ganin fuskar sa amma abun ya ci tura Sabida sojoji suka karesa ta ko ina , kai tsaye cikin hall d’in suka nuna Daidai lokacin da Jabcon ya d’auko wani and envelope zai bud’e bayan ya gama surutun da yake san yi, kamar daga sama yaji saukar abu a bakinsa , a razane ya fasa ihu lokaci d’aya sabida Jinin da bakinsa ya fara yi masa , manya manyan sojojin da Suka fara shigowa ne ya matukar tayar musu da hankali , cike da tsoro teachers da student suka mimmi’ke sabida bindugun dake hannun sojojin gasu da uban yawa, lokaci d’aya hall d’in ya nemi ya rikice amma kallan da sojoji sukai musune yasa sukayi saurin yin shiru , ta ko ina sojojin Big Boss ne da bin dugu a cikin su . A hankali ya shigo yake da kowa cikin hall d’in, Daidai wata lafiyayyiyar kujera da d’aya daga cikin sojojin ya shigo da ita Big Boss ya zauna kamar kullum yayi crossing legs d’insa waje d’aya ,
Cikin Sauri Victor da Anthony suka ‘karasa wajan jabcon da yake du’ke a ‘kasa jikinsa sai rawa yake ga Jinin da yake fita daga bakinsa , hannu Victor ya d’aga ya kaiwa bakin Jabcon duka , wani Jinin ne ya ‘kara fitowa abakin jabcon sai ihun yake yi Sabida azabar da yaji, hanya d’aya daga cikin sojojin sukai wa student cikin Sauri suka fara fitowa banda yan set d’insu Abla da aka dakatar dasu sai kuma teachers , duk da sauran student d’in ma sunso tsayawa , wata waya aka jefowa Anthony yayi saurin jafewa,Big Boss na zaune Anthony ya d’aga hannu ya tsitstsinka wa Jabcon mari da har saida gefen fuskarsa ya kunbura , tsabar azaba ko ihun ya kasayı sai kukan sa da yake fitowa kad’an kad’an, wani kujera d’aga daga cikin sojojin ya janyo Victor ya hankad’a Jancon ciki tare da saka masa d’aya daga cikin wayoyin wutan cikin wando , cikin wani socet aka saka wayar , cikin tsananin tashin hankali jabcon ya saki fitsarin da kamasa, ana kunna socet d’in wutar Jabcon ya fara jijjiga , ga fitsarin da yayi ya ji’ka wando , a karo na biyu suka ‘kara kunna socet d’in yanzu ma ihu kawai jabcon yake yi cikin a zaba , sai a lokacin sojojin suka bud’e yan class d’in Abla hanya da sukayi mugun tsorata Sabida tashin hankalin da suka shiga , ko wannan su cike da tsoro suka har hall d’in har teachers d’in da kowa jikinsa ya d’au ruwa , wani medium Box aka d’akko , da yake d’auke da cutters kala Kala a ciki, da ya bud’e baki zaiyi ihu zai ji saukar mari a bakin ta , tun yana fahimtar abu har ya dena ga hakwaransa guda biyu da suka fito waje Sabida azabar shan mari da yayi. Tsabar mugunta toshe masa baki d’aya daga cikin sojojin yayi ga hannunsa da aka rike, Daidai babban finger din kafarsa Anthony ya saka ya datse dan yatsan, cike da azabar da yaji ya dunga girgiza kai yana so ya basu hakuri amma sun toshe masa baki , d’ayan finger d’insa Anthony ya ‘kara Yankewa da har saida jabcon ya suma , Victor na ganin ya suma ya saka hannunsa guda biyu ya bawa fuskar jabcon tass , ba shiri ya farfad’o daga suman da yayi fuskarsa gabaki d’aya ta kumbura , wani babban cutter Victor ya d’auko sojojin suka tu’be masa kaya suka barsa sa singlet , Allah ya temakesa a kwai dogon wando har wajan gwiwarsa , hannu d’aya Victor ya saka zai zame wandan Jabcon da yayi mugun galabaita ya dunga girgiza musu kai da iya ragowar ‘karfinsa ga d’an yatsansa da yake Jini, Big Boss na zaune kamar be san abunda ke faruwa a Wajan ba sai phone d’insa da yake dannawa hankali
End Ads