x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 66 - IBTISSAM BOOK 1

  • 195001 words
  • 198000 words
  • Out of 200864 words

Category: Romance Story +18

Views 297

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
d’insa , tana gamawa da falourn ta koma cikin bedroom d’insa , lokaci d’aya ta tuno yadda ya ji’kata da ruwa da yanke mata gashi da yayi , ‘karamun tsaki Abla taja lokacin da ta soma gyara d’akin , har yanxu ranta a’bace yake Sabida tuno tarihinta da bata ‘Kaunar tunoshi, tana cikin gyara d’akin ta janyo wani white envelope bata sani ba , ya Garin d’akko su wasu hotuna suka fad’a daga ciki, da Sauri ta tsugunna ta soma tattara su batare da ta kalli ko d’ayansu , Adaidai lokacin da shi kuma ya shigo cikin d’akin ga black shirt dinsa da ya soma cire ma’ballinta har ana ganin singlet din jikinsa . Ido cikin ido Suka kalli juna Daidai lokacin da idanuwansa suka kai , kan envelope d’in hannun ta , yana zuwa be tsaya ba ya tsinka mata mari, kasa d’ago da face d’inta Abla tayi Sabida marin da yayi mata , a zuciye ya daka mata tsawa cikin kausashshiyar murya ya furta “ how dare you ? Ke wace irin mutum ce ? Baki da hankali ne ? “ shiru Abla tayi masa ga hawayen da suke sauka kan face d’inta , a zuciye ya sha’kota idanuwansa har sun soma ja sabida ‘bacin rai “ How dare you ina magana ki mun shiru , ko duk cikin rashin tarbiyar da iyayenki suka koya miki?” A hankali kuma ya furta “ I won’t be surprised tunda iyayenki a gidan karuwai suka ….. “batasan ya akai ba , batasan dalili ba , jikinta har rawa yake , tun kafin ya ‘karasa maganar sa Abla ta d’auke kyakkyawar face d’insa da mari…



PLX MASU NEMANA BASA SAMU NA A WHATSAPP ZAKU IYA MUN MAGANA TA TELEGRAM KO KU KIRANI ! Na d’an samu matsla da WhatsApp dina.

https://chat.whatsapp.com/CsKAjdD6LxZ8ue0YL5gPxQ

IBTISSAM
( A heart touching story of love and destiny)

Story & written
By
Mss Lee ✨


🦅 MIKIYA WRITER’S ASSOCIATION 🦅
🦅🦅M.W.A🦅🦅


AREWABOOKS: msslee
WATTPAD : Msslee__


✨MSS LEE BUSINESS WORLD ✨

💃💃💃💃 Ahayye Yar uwa kina business Amma bakida tambarin kasuwanci wato(logo& flyer) Maza ki garzayo ki kara mutuncin business dinki da customers ta hanyar logo da flyer Zaki jawo hankalin customers
Akwai Abubuwa da yawa dayakamata ace kinadasu a matsayinki na me business 👇🏻
🌹Logo
🌹Flyer
🌹Account sticker
🌹Business card
🌹Menus

🌷 payment received with thanks sticker Se asamiki Sunan business dinki wannan Yana matukar daukar hankalin customers
SANNAN INAYIN WASU ABUBUWAN KAMAR HAKA 👇🏻 🌹🌹 👇🏻
🌹Invitation Card
🌹Save the date
🌹calendar
🌹Book Cover
🌹Political poster
🌹Certificate
🌹Brochures
🌹Kar ku manta akwai Data cikin Sau’ki da arha tare da farashi me sau’kin gaske💃🏻💃🏻💃🏻.
Da sauransu duk a farashi me sauqi kardai na cikaku da surutu😄
Dan samun cikakken bayani zaku iya garxayo wa wajan MSS LEE BUSINESS WORLD , sannan zaku iya mata magana kai tsaye ta number wayarta kamar haka *07041879581*
Muna maraba da kowa da kowa 😍.

___💕 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM 💕___

BOOK 1
*PAID BOOK*
300 into 2681892316 Aisha umar, zenith bank . Sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581.

NOT EDITED

S____40💞
( Last free page)

Cikin wani irin shock Abla ta ja baya ganin abunda tayi, jikinta har rawa yake , gashi sai faman girgiza kanta take hawaye na sakko mata a kan face d’inta , a hankali Big Boss ya d’ago da eyes d’in sa yana binta da wani irin kallon da shi kad’ai yasan ma’anar sa ,yadda yaga ta tsoratan ne yasa shi d’aga girar fuskarsa kad’an tare da matsowa inda take, itama Abla cikin sauri ta soma ja baya hawaye duk ya ‘bata mata face d’in ta , ko kusa ta ‘ki d’ago da idanuwanta balantana ta kallesa , haryanzu kuma be mata komai ba sai matsowa inda take da yayi, yadda taga yana matso ta sosai yasa bata san ina take zuwa ba har ta cigaba da ja baya itama, bata ankara ba taji ta a bango zata matsa yayi saurin saka hannun sa guda biyu a both side d’inta.
Abla kamar zatayi kuka ta kawar da face d’inta tare da kulle idanuwanta gam tana jiran jin irin hukunci da zai mata.
Murmushin gefen baki ya saki kad’an duk da be fito sosai ba , face d’insa ya matso da ita Daidai fuskarta kafun ya furta “ open your eyes “kamar ya ‘kara zugata kuwa ta ‘kara kulle idanuwanta gagam, lumshe eyes dinsa Big Boss yayi tare da ‘kara bud’esu yana bin face d’in Abla da kallo, Babu mahalu’kin da ya ta’ba Marin sa ko da namiji ne sai ita , Wanda shi kad’ai yasan punishment d’in da zaiyi mata , a hankali ya ‘kara furta “ open your eyes “ yanzu ma kulle idanuwanta Abla ta ‘karayi a hankali ya sakko da hannunsa kan cikinta yana zagaye mata shi da öne finger d’insa , a razane Abla ta ware idanuwanta a kansa wasu hawayen suna ‘kara sakko mata, duk da yadda ta bud’e idanuwan nata be dena zagaye cikin ta da 1 finger d’in saba, cikin Sauri Abla tabuge masa hannun nasa , duk da ‘karfin hali ne take yi , cikin d’an masifa masifa ta furta “ Ni karka ‘kara ta’bani…” bata kai ga ‘karasa maganar taba ya had’e lips d’insu waje d’aya , a razane Abla ta ware idanuwanta kamar zasu fito waje , lokaci d’aya jikinta ya soma karkarwa , ‘kafafunta sun mata sanyi, ‘ko’karin zamewa take ya saka hannunsa guda d’aya ya talla’bota , har yanzu kuma be saki lips d’inta ba duk da yadda taso kwace wa , ji tayi gabaki d’aya nunfashinta yana ‘ko’karin d’aukewa ga wani irin abu da yake ratsa mata tun daga d’an yatsar ‘kafarta har zuwa kwakwalwarta, duk yadda taso kwace lips d’inta Big Boss ya ‘ki bata wannan damar,a hankali wani irin hawayen takaici suka soma sakko mata daga cikin idanuwanta ,Ji take kamar lips d’inta zasu tsinke sabida tsabar rad’ad’in da suke mata, cikin ‘karfin hali da ragowar ‘karfin da yayi mata saura ta cije a lips d’in sa itama. A hankali ya soma bud’e eyes d’insa da suka soma canza kala zuwa launin ja , yadda yaga ta kawar da kanta gefe tana ‘ko’karin kwace jikinta yasa ya motsa lips d’insa kad’an kamar Wanda yake shirin murmusasu, cikin cool voice kamar bashi ba ya furta “ Marin da akai mun kuma da me zan rama ? “ banza Abla tayi masa sai ma faman kwace hannunta da take ‘ko’karin yi , a hankali ya furta “ it’s Okay “ cikin ‘kasan ma’koshi kamun ya soma bud’e bottom d’in rigarsa cikin Sauri Abla ta ja baya , wasu hawayen suna ‘kara sakko mata, gabaki d’aya ta tsorata da yanayınsa , ita kad’ai sai faman Kallan ‘kofa take , a hankali ta furta “ kayi hakuri”, tsayawa yayi da ‘balle button d’in da yake kafun ya matso da face d’insa Daidai saitin kunnanta , a hankali ya furta“ we’re so sweet Mrs Omar Farooq”, da wani irin ‘karfi Abla ta bangajesa ta arta na kuje cikin sauri ta janyo doguwar rigar ta , tunda ta turesa be motsa ba har ta ‘karasa wajan ‘kofa, da manyan idanuwan ta da suka cika da kwalla sakar masa harara cikin ‘kasa ‘kasa da murya ta “ Allah sai ya saka mun d’an iska kawai “ , sarai yaji abunda tace , shiyasa yayi kamar zai mi’ke , cikin tsoro Abla ta bud’e ‘kofar ta arta a guje, wani irin lallausan murmushine ya su’buce masa akan lips d’insa , har hakwaransa suna fitowa waje kad’an, yadda yayi murmushin ba’karamun kyau yayi ba kamar fuskarsa ta tsaya a hakan , ga dimples d’insa da suka lotsa sosai , a hankali ya fesar da iskar bakinsa , cikin ‘kasa ‘kasa da murya ya furta “ Batajin magana”.

Hotunan da suke zu’be a ‘kasa ya kalla, lokaci d’aya mood d’insa ya soma canzawa , d’aya daga cikin hotunan ya d’auka me d’auke da hotan jariri a ciki, gabaki d’aya jikin yaron jinine da alama kuka yake aka d’auki hotan , a hankali Big boss ya lumshe idanuwansa ,tun bayan tsawan shekara 22 hotunan suke ajje, Sabida ko kusa bayasan tuno da abubuwan da suka faru,lips d’in sa na ‘kasa ya d’an ciza Kafun ya mayar da pics d’in cikin envelope . Gucci watches din hannun sa ya kalla , a hankali ya furta “ Oh God “ sai kuma ya mi’ke cikin nutsuwar sa ya nufi dressing room d’in sa .

Abla tana barin part d’insa cikin sauri sauri ta saka doguwar rigar ta , ga hawayen face d’inta da suka ‘ki tsayawa , har ta wuce uncle a falourn bata sani ba , gabaki d’aya bata cikin nutsuwar ta , kai tsaye d’akin ta ta wuce tare da saka wa ‘kofar key , cikin masifa masifa Abla ta furta “ ‘Dan iska , mugu kawai , Allah sai ya saka mun , idan ka tashi hukuntani karka barni da raina kayanka ni gunduwa gunduwa “, tana surutun tana cire kayan jikinta , bata tsaya a bedroom d’in ba ta wuce toilet tayi a wanka . Ta d’au kusan mintuna 15 a cikin toilet d’in kafin ta fito , kallan fuskarta tayi a mudu bi, lips d’in ta har ya d’anyi ja sabida muguntar da yayi mata , lokaci d’aya kuma ta saka kuka me ta’ba zuciya “ akan me kake ‘ko’karin zagar mun iyayen da bansani ba suna raye ko sun mutu, bana san ka , bana ‘kaunar ka , Nima na tsaneka kamar yadda ka tsaneni , mugu kawai “ ita kad’ai sai sanbatu take yi, lokaci zuwa lokaci kuma tana mitar abunda yayi mata. Doguwar Riga kawai ta saka ajikinta , tunda ta kwanta akan gado take juyo , gabaki d’aya ta rasa meke mata dad’i, da ta kulle idanuwanta abunda ya faru a tsakanin su yake sake dawo mata , cikin ‘kan’kanin lokaci Abla ta rud’e jikin ta yasoma rawa kamar me zazza’bi, duk yadda taso bacci ya d’auke ta abun ya ci tura , sai fuskar Big Boss da ke faman yi mata gizo a duk lokacin da ta kulle idanuwanta , har wajan ‘karfe 2 idanuwanta biyu , sai juyi take akan gado da ‘kyar wani irin wahalallan bacci ya d’auke ta .
***** 3:10am
Cikin wani irin d’aki me duhun gaske ta tsinci kanta , ga wasu irin abubuwan tsafi dake cikin d’akin ta ko ina , a tsorace Abla ta soma bin cikin d’akin da kallo hankali a tashe , “ Abla ! Abla ! Abla “ sunan dake faman kira Kenan , cike da tsoro Abla ta d’aga kanta sama Sabida muryoyin wad’an da taji , a gigice ta ‘kwalla kara kafun ta soma kiran “ Eshaal , Baby ,Fanan ku matsa zasu kashe ku, ku matsa ,” cikin kuka Fanan ta girgiza mata kai “ Abla mutuwa zamuyi, suna bin mu duk Inda muke , ke kad’ai ce zaki iya cecen rayukan mu,” cikin Sauri Abla ta soma ‘ko’karin kwance kanta , amma igiyar kamar merai da tayi ‘ko’karin kwance wa zata ji igiyar ta ‘kara matse mata jiki . Da ‘karfi su Fanan suka furta “ Abla…” suna furta sunan ta gabaki d’aya Jini ya fara fito musu ta baki da ta hancin su , ihu Abla ta saki tana ‘kokwarin kwace kanta , da tayi ‘ko’karin Yin addua zataji an matse mata ma ‘koshi , gasu Baby da suma sai fitar da Jini suke ta baki , cikin azaba Abla ta furta “Ya Al…Al…Allah”, cikin ‘kan’kanin lokaci igiyar data d’aure ta , ta ‘bace batt babu ita , tana kai dubanta idan su Fanan suke taga nan ma wayam babu su babu a lamarsu, wani irin jiwane ya soma kamata , gani take kamar ba’kin dakin yana juya mata , da’karfi ta toshe kunna wa tare da kurma ihu *****
Bakinta cike da addua Abla ta farka daga baccin da ya d’auketa , gabaki d’aya jikin sai faman d’aukar rawa yake ga wani irin zufa da ta had’a ta ko ina , wayar ta tayi saurin janyowa tare da kunna karatun alqurani, kusan mintuna 5 tana zaune tana sauraran al_qurani me girma, kafun ta soma a jiyar zuciya a hankali Sabida nutsuwar da ta soma samu cikin ranta .

***WASHE GARI***

Washe Gari da wurwuri ta farka daga baccin da ta koma , wanka kawai tayi ta Shirya cikin uniform d’inta , yau ko jiran su Little batayi ba , tunda taga basa falourn , hatta breakfast d’inta bata tsaya tayi ba sai Youghurt da ta d’au ka , Burin ta kawai taje taga su Eshaal . Tana fitowa ta tarar da su Madam Sarah, cikin Sauri ta nufi motar, madam sarah ta bud’e mata suka nufi makaranta . Ko kallan su sarah batayi ba , motocin su na tsayawa ta wuce class d’insu. A zaune ta tarar dasu ko wannansu da book d’insa a hannu tana ganin su tasaki wani irin ajiyar zuciya , “ meyafaru haka kike ajiyar zuciya ?” Cewar Baby , kanta Abla ta girgiza mata “ No babu komai kawai na d’auka bakwanan ne “ kin tabbata?” Cewar Fanan, yanzu kanta Abla ta d’aga mata , “ yes da gaske nake babu komai, just I wanna check on you gurls “ ta ‘karasa tana sakar musu ‘karamun murmushin da ko cikin zuciyar ta be kai ba , bakin ta Eshaal ta nuna tana kallan Abla” me ya samu lips d’inki? Ya fashe ?” Ta’ba lips d’inta Abla tayi kad’an , cikin sauri ta furta “ Bugewa na d’anyi amma yanzu it’s okay ya dena mun zafi ma “, Eyya sorry dear “ cewar Fanan , wani murmushin Abla ta saki tana ajje school bag d’inta , gabaki d’aya sai suka zuba mata idanuwa kuma , cikin tsarguwa ta furta “ Menene kuke bina da kallo haka ?”cike da tsokana Baby ta furta “ kin tsargune ?” ‘Dan harararta Abla tayi “ yadda kuke bina da idanuwa haka ba dole na tsarguba”, da haka suka canza topic d’in hirar su zuwa wani daban kafun teacher ya shigo class d’insu.

Da aka fito break ma , gabaki d’aya hankalin Abla baya jikinta, mafarkin da tayi jiya gabaki d’aya ya tsaya mata arai, dafatan da Baby tayi ne yasa ta d’an firgita “ Abla meke damun kine ? Ko akwai abunda kike ‘boye mana ne ? “, cikin Sauri Abla “ No Baby seriously Babu komai trust me , Kawai ciwan kai nake ji sama , but don’t worry nasan stress ne ina komawa gida na huta zai dena” hugging d’in ta Baby tayi “ it’s okay zai daina kinji? “ kanta Abla ta d’aga mata , da haka suka soma cin abincin da sukayi order , time nayi kuma suka koma class a binsu.
Lokacin Tashi nayi kamar kullum suka fito abunsu su uku, har zasu bar building d’in Abla ta daka sorry gurls ku bani 2 minutes na bar littafina a class , zan same ku a inda muke tsaya wa , “ Toh “ kawai suka ce mata suka wuce ita kuma Abla ta nufi class d’insu. A Daidai inda suke suke tsayawa d’in suka zauna zaman kiran fitowar ta , almost 10 minutes sai ga motocin su Little sun shigo , Yana fitowa shida prince inda su Eshaal suke ya nufa dan ya ganesu, murmushi akan face d’insu suka furta “ yaya little barka da zuwa “ shima face d’insa cike da murmushi ya furta “ Gurly d’in Lil ! Ya kuke “ a had’e Suka furta Alhamdullhi kafun su juya wajan prince shima su gaidasa, da kai ya amsa musu kafin ya furta “ ina Lil take ?” Cikin d’an damuwa Fanan ta furta “ ita muke jira tace zata d’auko book d’inta but almost 10minutes Kenan bata dawo ba.”

Cikin d’an mamaki little ya furta “ and shine kuka tsaya anan ? Me ya hana ku dubata ? Kuzo muje ku nuna mana class d’in” da toh suka amsa masa kafun su nufi hanyar class d’insu gabaki d’aya , abun mamaki suna shiga cikin class din basu tarar da kowa,” kuka ce ta zo class “ Baby ce ta furta “ Eh haka tace mana but may be munyi kuskuran hanya ko ita ta koma tana jiran mu , let’s go back “ har zasu juya Fanan tayi Saurin furta “ ku daka , wancan ba jakar Abla bane ?” Kallan direction d’in sukai gabaki d’ayansu, cikin sauri Little ya ‘karasa wajan school bag d’in” yeah jakar tane amma me yasa na ganta a ‘kasa ?”Cikin d’an shakku prince ya furta “ something is wrong, lets go back “ , cikin tashin hankali gabaki d’aya suka dawo inda Abla tace su tsaya ko zasu ganta amma babu ita babu alamar ta , zuciyar Little ne ta buga da ‘karfi shiyasa yayi saurin tafe ta “ yaya prince we have to check the school , ka kira su robert “ kansa Prince ya jinjina masa kafin yayi dialling number Robert , su fanan ma gabaki d’aya sun tsure , cikin su babu wanda be soma hawaye ba a cikinsu. Cikin mintunan da basu wuce 5 ba motocin su Robert suka shigo cikin makarantar, da sauri little ya furta “ Robert we have to check da school , bamu ga lil ba ,” shi kansa robert din sai da ya sha jinin jikinsa , cikin ‘kan’kanin lokaci sojojin su soka rabu kashi kashi , suna su little d’in basu
End Ads