craying!" ae kamar cewa yayi ma taƙara volume ɗin kukan nata, kansa dake matuƙar yi masa ciwo ya dafa, haɗe da cije laɓɓansa, wallahi bazai iya jurewa ba komai zai iya faruwa dashi, yakai ƙololuwar sha'awa matuƙa, amma kuma yazaiyi da kukan da Zahrah takeyi masa yanajin tausayinta sosai, yasan ahalin yanzu metake tunawa, wancan mummunar ranan take tunawa, amma kuma haƙƙinsa ne ya mantar da ita komai. (Khair anya ruwanki bazaiyi tafasan banza ba kuwa🤔 naga mutumiyar taki tana neman hana doctor walwala🙊) Sake matseta ajikinsa yayi haɗi da haɗe bakinsu waje ɗaya, sauya salon kiss ɗin nasa yayi, wanda hakan ya tilasta mata dole tayi shiru, sai dai haryanzu jikinta bai daina ɓari ba, idan tace gangar jiki da ruhinta basa karɓan saƙon Dr.Sadeeq tayi ƙarya, amma kuma matuƙar tsoro takeji, ƙwaƙwalwarta azabar da Zaid yajiyar da'ita take tariyo mata, gani take shikenan itakam tata ta ƙare dan kuwa bazata iya jure azaba biyu ba,, salon romance ɗin da Doctor keyi mata yawuce gaban kwatance burinsa shine ya mantar da'ita wannan tsoron, ita kanta ta yarda da cewa saƙonninsa sun ratsata domin kuwa tuni ta gama jiƙewa to amma abun tsoron na gaba,, bai ɗauke bakinsa acikin nata ba haryagama ratsa cikin jikinta, wani irin wawiyar ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da sakin wani irin ƴar ƙaraman ƙara dake nuna alaman cewa mutum yagama lulawa cikin duniyar da babu irinta,, baisan dayaushe yazare bakinsa acikin nata ba, wani irin ƙara ta sake haɗe da soma rusa kuka kamar wanda ake zarewa rai.....*** Bayajinta balle kuma ganinta saboda idanuwansa rufewa sukayi ruf, duk kuka da ihun da takeyi baisan tanayinsu ba, wallahi shikam tunda yake baitaɓa sanin menene daɗi ba aduniya sai awannan lokacin, bazai taɓa iya misalta abun dayaji ba abun yafi ƙarfin tunaninsa ya shammaci hankalinsa, harya manta da cewa ita ɗin ba budurwa bace, baitaɓa kusantar wata mace ba Zahrah itace ta farko, kuma amatuƙar kame yajita gam, sai dai kuma fa har'abada baza'a haɗa virgin da kuma wacce ba virgin ba dole akwai banbanci amma shidai baiji banbancin ba saboda dama baisan kowaba sai ita*** Doctor ya hole iya holewa yayi gurnanin yayi sambatun harsau ba'adadi yayinda ƴar mutane kuwa tayi kuka kamar ranta zaifita harsaida idanunta suka kumbura alokaci guda kanta kuwa ba'a magana wajen yi mata ciwo..
***
After 1 hour.
Shikansa jikinsa zafi zau ya ɗauka yayinda yaji gaba ɗaya duniyar tana juya masa, to inaga kuma wacce ya bawa kaya, da ƙyar ya'iya kwantawa agefenta haɗe da jawota cikin jikinsa, baisan da wani kalma zaifara yi mata magana ba, kyakkyawan sumbata ya bata akan goshinta haɗe da rumtse idanunsa, wanda suke zubar da hawayen tsananin tausayinta,,, kusan 12 minute yana rungume da'ita acikin ƙirjinsa "Me daɗi na!" yafaɗi haka acikin kunnenta da'alama dai sunan daya bata kenan,lol. Zahrah da'idanunta sukayi luhu suna ta tsiyayar da hawaye kasa cedashi komai tayi.. (Su Me daɗi ansha wuya😂🙊🙈)
"I'am so sorry, banyi haka don nacutar dake ba, nakasa control ɗin kainane, Inasonki Zahrah, a iya daren yau soyayyarki ta sake ninkuwa acikin zuciyata, kiyafemin kinji me daɗi na bazan ƙara ba, please for give me!" yaƙare maganar cikin kwantar da murya, da'alama dai har yanzu giyar daɗin baigama sake shiba... Me daɗi dai taƙi cewa komai haka ya sauƙo daga kan gadon rungume da'ita kamar wata ƴar baby, direct bathroom yanufa da'ita, dakansa ya haɗa mata ruwan ɗumi haɗe da zaunar da'ita aciki, duk da cewa ita ba virgin bace amma kuma wannan ɗin ma kusan daidai yake dayinta na farko, saboda ta matuƙar shan azaba sosai, hakan yafarune kuma saboda yanda Hajiya Shuwa ta dinga ɗurka mata magungunan matsi dakuma na ciko da mace, sosai taji zafi aƙasanta lokacin da yazaunar da'ita acikin ruwan amma kuma yazatayi yazama dole ta daure.. Dakansa yayi mata wanka haɗe da naɗota acikin towel like wata ƴar ƙaraman baby, shima wanka yayi kana yafito daga cikin bathroom ɗin, shidakansa ya sanya mata rigan bacci, shima ya jallabiya ya sanya ajikinsa, haryanzu Zahrah bata daina tsiyayar da hawayeba,, new blanket yasanya musu domin kuwa wancan ya ɓaci da sperm ɗin me.... au 🙊Zahrah,, jawota yayi jikinsa haɗe da rungumeta tsam tsam jiyake kamar wani zaizo ya ƙwace masa ita (wai inji nuru ba kama bane Zaid yananan tafe😂 niko nace yayi ƙarya)
Hawayen da suketa ambaliyan sauƙa akan fuskarta yashiga share mata, haɗe da ɓare wani sweet yajefa acikin bakinsa, kwantar da'ita yayi akan ƙirjinsa haɗe da ɗago fuskarta ya tura mata sweet ɗin acikin bakinta, harshensa yasanya yana meyi mata wasa da sweet ɗin acikin bakinta, lumshe idanunta tayi tana me sauƙe ajiyar zuciya, yayinda yake shafa mata bayanta ahankali,,har wani irin nannauyan bacci yazo ya ɗauketa..... Kafeta yayi da idanunsa aransa yana me godia ga Allah daya basa wannan mata me ɗauke da tarin ni'imomi na fili dana baɗini, kai yasha sweet fa yau harwani jin kansa yake a sama.Lol,,, batare da yayi aune ba shima bacci ya ɗaukesa bayan yayi musu addu'a yashafa mata... Good night angon me daɗi...
Tun da ta tashi tayi sallan asuba take ta ruskar kuka tamkar wacce aka cewa wani nata ya mutu, ita kanta batasan kukan me takeyi ba, amma dai hakanan takeji zuciyarta babu daɗi, gashi gaba ɗaya jikinta ciwo yake, "Gaskiya Doctor mugune." tafaɗi haka acikin zuciyarta, gaba ɗaya ya gajiyar da ita, daga ƙasan zuciyarta kuwa wani abune yayi mata tsaye wanda kuma shine sanadiyar kukan nata, wannan wace irin rayuwa ce? wace irin ƙaddara ce wannan? rabonta da tayi farinci me tsayi tun kafun Zaid yashigo cikin rayuwarta, ada tana ganin rayuwar da takeyi acikin gidansu rayuwar ƙunci ce, ashe bata sani ba wannan rayuwar salama ce a gareta, SO baiyi mata adalci ba, so bai kyautawa rayuwarta ba...
Yajima tsaye akanta yana me ƙare mata kallo, mamakin yanda take kuka tsakaninta da Allah yake, a iya saninsa banda abun daya wakana atsakaninsu daren jiya baiyi mata komai ba, amma kuma sai gashi yanzu tana ruskar kuka, har a ƙasan zuciyarsa bayason kukanta, idan yaji kukanta jiyake gaba ɗaya nutsuwarsa ya ƙaura daga jikinsa,, ahankali yashiga takawa harzuwa inda take duƙe akusa da gado tana kuka, sam batamasan da shigowarsa ba kukanta kawai takeyi.... Hanunsa yasanya ya dafa kafaɗanta, da sauri ta juyo aɗan razane don bataji shigowarsa ba,, idanunsa ya ƙanƙance haɗe da waresu alokaci guda, zama yayi akan gado haɗe da ɗagota zuwa jikinsa...
"Me yasa Zahrah? me nayi miki? meyasa kike ƙuntatawa rayuwarki akan wani dalili naki? ban aureki don nazuba miki ido kita cutar da kanki ba, please ki daure zuciyarki kidaina wannan kukan banaso!" ya faɗi maganar cikin lallashi... Saurin ɗauke hanunsa dake kan wuyanta yayi, kansa yaɗan ɗafe haɗe da zaunar da ita akan gado, direct wani ɗan madaidaicin drawer yanufa, maganin da yasan zai sauƙar mata da zazzaɓi acikin mintuna ƙalilan ya ɗauko tare da ruwan gora ya dawo zuwa gareta. Maganin ya ɓalla ahanunsa tare da jawota jikinsa, bakinta ya buɗe ya jefa maganin aciki haɗe da bata ruwa, babu musu ta haɗiye maganin bayan ta rumtse idanunta, sai kace wacce aka bawa guba... Aje goran ruwan yayi haɗe da sake jawota jikinsa, kwantar da kanta yayi akan ƙirjinsa, yayinda yake shafa bayanta a hankali. Ajiyar zuciya haɗi da sheshsheƙan kuka kawai take sauƙewa. Shikuwa Dr.Sadeeq wani tunani na daban yakeyi acikin zuciyarsa, hakanan Allah ya halittamasa tsananin tausayin Zahrah acikin zuciyarsa, yana sonta sosai, bayason yaga tana cikin damuwa, bayajin akwai wani abu aduniyar nan da Zahrah zata nema agaresa matuƙar yana dashi tarasa, zai iya mallaka mata komai nasa, matuƙar zataji daɗi, za kuma tayi farinciki, bakinsa ya kawo daf da kunnenta cikin murya me sanyi yace
"Zahrah!"
Tanajinsa amma kuma saitayi sauri ta lumshe idanunta, tanaso ya ɗauka cewa bacci take.
Jin tayi shirune yasanya yashiga goga mata lallausan sajensa akan fatar wuyanta, yayinda yake yawo da hanunsa akan bayanta a hankali..
Luf tasakeyi acikin ƙirjinsa, tana jin saƙonsa yana tsarga mata hartafin ƙafarta, yayinda daddaɗan ƙamshin turarensa ke ƙara sanyaya mata jiki, batajin bacci ko kaɗan, amma kuma yazama dole ta ƙwaƙulowa kanta baccin dole, kodan ta samawa zuciyarta salama. "Ina laifin Dr.Sadeeq? mene bayi dashi wanda mace takeso tasamu ajikin ɗa namiji? miye laifin masoyin daya nuna maka haƙiƙanin so? ashe wani lokacin zuciya batasan menene halacci ba? me yasa SOYAYYA tazamo guguwa me hargitsa zuciyar ɗan adam tayi fatali da komai nasa?" itakam ko da a yanzu soyayya ta barta haka ta gama iya cutarta, cuta me muni ma kuwa.. Yajima yana shafa bayanta, harsai da ya ji sauƙar numfashin dake nuna cewa da gaske bacci ya ɗauketa. Kwantar da'ita yayi akan gado, haɗe da jawo blanket ya rufe mata duka jikinta, yasani sarai batason sanyi, don haka ya rage gudun A.C, kashe mata fitilan ɗakin yayi, kana ya jawo mata ƙofar ya rufe mata bayan yafita zuwa falo.. Laptop ɗinsa ya ɗauka haɗe da buɗewa, aikinsa ya shigayi cikin nutsuwa, ɗan kwana biyun nan da bai shiga office ba haryatara ayyuka masu yawa, gashi ansanar masa patients suna buƙatar taimakon sa, duk da ya ɗau hutu ma ashe bai tsira ba, ayyuka na nan akansa wanda yazamana dole sai shi zaiyisu...
***
*GERMANY*
Shikaɗai yake rayuwarsa acikin ɗakin, yau kwanansa ɗaya kenan baisanya komai na abinci acikin saba, yayi matuƙar ramewa alokaci guda, yayinda gashi dakuma sajen dake kwance akan fuskarsa suka ƙara yawa fiye da na da, duk da dama cewa shi mutum ne me yalwan suma, kallo ɗaya zakayi mai kasan cewa yana ɗauke da damuwa me tarin yawa acikin zuciyarsa, Zaid ɗin da dana yanzu sun banbanta, wan can Zaid ɗin zuciyarsa cike take da isa, ɗagawa, girmankai, rashin sanin darajan ɗan adam, Zaid ɗin da mashayine, mazinaci, wanda bai ɗauki zina abakin komai ba, haka kuma Zaid ɗin da, baisan menene damuwa ba, baisan menene rashi ba, samu kawai ya sani, sannan kuma baisan menene ƙunci da ɗaci ba, baikuma san menene wani abu waishi soyayya ba. Zaid ɗin daya kasance yanzu kuwa, wani mutum ne dayake cikin ƙunci, zuciyarsa tana cike da tarin damuwa, Zaid ɗin yanzu yarasa duk wani farincikinsa, yarasa jin daɗi, yarasa nutsuwar zuciya data ƙwaƙwalwa. "ko wannan baici yasa Zahrah ta tausaya masa ba? shin wai shi kaɗaine yataɓa aikata abun da baidace ba?" yatambayi kansa, abu biyune suke damunsa, zazzafar soyayya dakuma rashin nutsuwa da salama dake damunsa, yanzu shikaɗai yasan halin dayake ciki, baya iya bacci, baya iya cin abinci, bayajin daɗin komai nasa, gaba ɗaya duhu ya mamaye rayuwarsa, yanzu yafara zargin cewa zunubansa ma sunyi masa yawa, yasani ƙwarai, yasan abu me kyau da kuma marar kyau, amma saboda ruɗin duniya gaba ɗaya ya shagala. (Yawancin mutane yanzu rayuwarsu sukeyi saka ka, zasu aikata zina, zasu sha giya, zasu aikata duk wasu aiki dake jawo musu manya manyan zunubai, amma kuma yawancinsu sunfi gudun kunyar duniya data lahira, suna tsoron wani yakamasu suna aikata zina, amma basa tsoron kallonsu da Allah yakeyi, wasu sun maida zina manshafawarsu, suna ganin kamar hakan wayewace, bayan kuma suna sane dacewa aikata ta babban halaka ne, Ya ALLAH kaci gaba da karemu, kakuma tsaremu da sharrin zina, ka rabamu da zama da mazinata, Ameen Ya ALLAH!)
Yariga daya gama yanke hukunci cewa ko da su Dad ɗinsa basaso saiya koma Nigeria, bazai iya zama anan ba, zafi yakeji acikin zuciyarsa marar misaltuwa idan haryatuna da cewa Zahrah'nsa tana can gidan wani, sai yaji gaba ɗaya nutsuwarsa ta gushe, wataƙila ma wannan banzan Doctor ɗin ya kusanci Zahrah'nsa, ae kuwa baisan sanda ya ƙwalla wata irin ƙara ba, azuciye ya ɗauki wani flower dake gefen gadon, yayi jifa dashi, take kwalbar flower'n ya tarwatse a tsakiyar ɗakin, duk da haka hakan baiyi masa ba, saida yataka ya ƙarasa gaban mirror, da hanunsa ya daki mirror ɗin, take mirror'n ya tarwatse har saida ya yanka masa hanu, amma saboda tsananin kishi'n dake cinsa, ko zafin ciwon baiji ba.
"Hakane ma, yakusanceta" wata zuciyartasa ta faɗa masa..
"No!!! it will never happen, i Know Zahrah will not do it, bazata taɓa iya bawa wani kanta ba bayan ni, because she know we love each other" yafaɗi haka da ƙarfi cikin wata irin murya, me ɗauke da tsananin ɓacin rai, durƙushewa yayi a ƙasa haɗe da sanya hanu ya dafe saitin zuciyarsa wacce take bugawa da sauri, da dukkan alamu dai ya tsokalowa kansa. Haki yasomayi tamkar wani wanda yayi gudu, tarine ya sarƙesa, take jini yasoma fitowa ta bakinsa, shi kaɗai yayi tarinsa harya ƙare, ya galabaita sosai da sosai, da ƙyar ya'iya jan jikinsa ya shiga toilet, wanke bakinsa yayi kana yafito daga cikin toilet ɗin, numfashi kawai yake maidawa cike da wahala,, wani ɗan abu yadanna, bayan kamar minti 1 saiga wata cleaner tashigo cikin ɗakin, nuni yayi mata da inda jininsa ya ɓaɓɓatata, babu ɓata lokaci ta sanya kayan aiki ta gyara wajen, tana kammala gyaran kuwa wasu likitoti su biyu suka shigo cikin ɗakin.. Duba lafiyar jikinsa suka sake yi haɗe da basa wasu magunguna, wata allura sukayi masa da take matuƙar sa bacci, domin kuwa gwaje gwajen da sukayi masa yasa sungano cewa baya samun wadataccen bacci.
Suna fita ya lumshe idanunsa, wanda tuni suka zama jan gauta, saboda tsabar tsananin kishi dake cinsa, jiyake ma kamar idan ya ƙara kwana ɗaya ba acikin Nigeria ba ya cutu, gwamma yaje ya ƙwace Zahrah tunkan wanda ya ɗauka bakomai ba ya ɗanɗana masa zumarta. (Hahhh guy ae ka makaro,yasin doctor yajima da ɗanɗanawa🙈) **** Mintuna kaɗan dayi masa alluran, bacci me nauyi yayi gaba dashi...
Dad ne ya nutsu haɗe da dawo da kallonsa ga Mummy. "Inaga abu ɗaya zamuyi masa yamanta da wannan yarinyar, kawai na yanke shawara aure zanyi masa."
Shaye da mamaki Mummy take kallon Dad. "Aure fa kace Alhaji? wakake tunanin zata iya zama da Zaid, da irin wannan halinnasa? hmmm bana majin cewa Zaid zaiso wata mace bayan wannan Zahrah'n, ni nama fara tunanin cewa asirce masa zuciya tayi, amma inbanda haka taya lafiyayyen ɗa namiji kamar Zaid zai maƙalewa mace ɗaya kamar maye"
Murmushi Dad yayi haɗe da girgiza kansa, "itadai Safara'u haka take, idan ana magana me hankali saikuma tana sako wasu abubuwa kamar na wasa." dad yafaɗi haka acikin zuciyarsa, afili kuwa gyara zamansa yayi haɗe da sake fuskantarta...
"A wannan karon dagaske aure zanyi masa, saboda aure ne kaɗai zaisanya Zaid dawowa cikin nutsuwarsa, bandamu da ko yanason matar ko baya sonta ba, nasan watarana ahankali zai sota ya manta da waccar"
"To Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, amma gaskiya nima banjin daɗin ganinsa acikin wannan halin dayake ciki yanzu,ko abincin kirki wallahi bana iya ci" Mum tafaɗi haka cikin tausayawa ɗan nata..... (Team Zaid kunji fa wai aure za'ayi masa me zakuce? wayaga Zaid da auren dole)
****
NIGERIA
Tunda ta kwanta bacci ba'ita ta tashi ba sai 11:30 am, ko tsayawa nemansa yau batayi ba tafaɗa bathroom, wanka tayi kana ta fito daga cikin bathroom ɗin... Mai kawai ta shafa kamar kullum sai kuma powder, itakam batason cika meckup akan fuskarta.
Riga da sket na atamfa tasanya, wanda yayi mata caras ajikinta, ɗan kwalin kayan kawai ta yafa akanta zuwa kafaɗarta. Direct falo ta nufa sai tashin ƙamshi take, kamar yanda tayi zaton zata ganshi a falo, sai taga saɓanin haka, domin kuwa babu shi babu alamarsa,, kallonta ta mayar kan dinning area saidai taga kan table ɗin wayam babu food flask ko ɗaya,, hahhh take idanunta sukayi raurau dasu, ɗan ƙaramin bakinta ta tunzuro haɗe da shafa cikinta, "Yanzu kenan Doctor da yunwa ya barta?" ta tambayi kanta...
Motsi ta soma ji daga ɓangaren kitchine, tsoro ne yaɗan kamata dan tasan Dr.Sadeeq da kansa kam bazai shiga kitchine ba, "to kodai basu kaɗai bane acikin gidan?" tasake tambayar kanta. Cikin sanɗa take takawa harta isa ƙofar kitchine ɗin, motsinne yasake tsananta, don haka cikin sanɗa ta tura kanta cikin kitchine ɗin.
"Kamata!!!" taji anfaɗa da ƙarfi. Wani irin ƙara ta ƙwalla haɗe da rugawa a guje ta koma cikin falo.. Dariya yashiga yi mata bayan yafito daga kitchine ɗin hanunsa riƙe da plate wanda yake ɗauke da soyayyen chips..
Zamewa tayi aƙasa haɗe da dafe ƙirjinta, nunfashi take fitarwa da ƙyar, da'alama ta tsorata sosai.
Zama yayi akan kujera har yanzu dariya yakeyi mata, yasan zata tsorata amma baiyi tunanin tsoron nata zai kai har haka ba.. "Yadai karfa ki sume min" yafaɗi haka yana me ɗan tsagaita dariyarsa...
Ɗan ƙaramin bakinta ta tunzuro gaba haɗe da miƙe ƙafafunta akan sofa, "Nidai Allah ka tsoratar dani, please kada ka ƙara zan iya mutuwa fa!" taƙare maganar cikin tsantsar shagwaɓa.
"Kindai tsorata kanki, ni bani na tsorataki ba ƴan mata, da wayace ki shigo kitchine ɗin cikin sanɗa?"
"To ba motsi naji ba, na ɗauka ko aljanine!" still cikin shagwaɓa takumayin maganar..
Kallonta kawai yashigayi yana murmushi, a garin gudu harta yada ɗan kwalin dake kanta