x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 32 - SHU'UMIN NAMIJI

  • 93001 words
  • 96000 words
  • Out of 185824 words

Category: Romance Story +18

Views 254

10 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
abune me wahala ka yarda da abun dazan faɗa ma"


"Bazaka gane yanda nakeji agame da'ita ba ne Abid, dakasan yanda nakeji a zuciyata da ka tausaya kasanar dani maganin matsala ta, kodai shine so ɗin da kake cewa?" Zaid yatambayi Abid cike da damuwa...


"Ƙwarai kuwa Zaid wan nan shine SO, sai de naka SO'n ya banbanta da sauran soyayya'n, kai naka soyayya'r me tsanani kakeyi, wanda tariga da tajima acikin jikin ka batare da ka sani ba, ina da yaƙinin cewa tun farko Son Zahrah kake bawai sha'awarta ba kamar yanda ka ɗauka!" Abid yafaɗi haka da iyaka gaskiyarsa...


Nannauyar ajiyar zuciya Zaid ya sauƙe haɗe da sanya duka hannayensa ya dafe kansa wanda yake ɗan sara masa a hankali.. Tabbas yanzu kam ko yaso ko yaƙi dolensa ya yarda da maganan da Abid yafaɗa masa, domin kuwa idan har ba soyayya ba menene ke damunsa dayake sawa yakejin zafi a zuciyarsa? idan ba soyayya ba menene yake sanya tunaninsa hargitsewa da zaran yatuno Zahrah? idan ba soyayya ba menene yake sanya sa rasa sukuni da nutsuwarsa aduk sanda yatunanota kokuma yaganta? lallai kuwa soyayya baimasa adalci ba da bai sanar dashi kansa ba tun sanda yafarasa batare da yasani ba..


Idanunsa da sukayi jajur dasu ya ɗaga haɗe da maida kallonsa ga Abid "Inasonta Abid inasonta sosai!"


Waro idanu Abid yayi yana me kallon Zaid idan da ba Zaid ɗin ne da gaske a gabansa ba, to tabbas da sai yace badaga bakin Zaid wa ƴan nan kalaman suka fitoba, yau Zaid da kansa yake cewa yakamu da son wata? lallai kuwa rayuwa tana shirin juyawa abokin nasa baya.


Miƙewa Zaid yayi daga zaunen da yake haɗe da sanya hanu ya kwashe wayoyinsa dake kan ɗan ƙaramin table ɗin dake aje gabansu.


Kallonsa Abid yayi cike da mamakin ganin yanda lokaci ɗaya yanayin Zaid ɗin ya sauya.


"Inakuma zaka?" Abid yatambaya..


"Zanje gidansu Zahrah Abid, idanuna sun matsamin zuciyata har bugawa take Abid, ita kawai nakeson gani, idan har zata amince inaso ayau base gobeba koda ƙarfe ɗaya ne na dare a ɗaura mana aure da'ita" yanakai wa nan a zancensa yayi tafiyarsa.. Hangame baki Abid yayi yana kallonsa harya ɓacewa ganin idanunsa. Anyakuwa Zaid yana cikin hankalinsa? Kodai asiri yarinyar talakawan nan tayi masa ne? Abid yajerowa kansa waƴan nan tambayoyin, bayan yasan baida amsa bai kuma da me basa amasar...


Zahrah dake zaune tana gudanar da assigment ɗinta, wani yaro yashigo cikin gidan nasu haɗe da kwaɗa sallama.. Amsa masa Zahrah tayi batare da taɗago kanta takalli yaron ba..


"Wai ana ƙiran Zahrah a waje" yaron yafaɗa yana me kallon Zahrah domin kuwa yasan cewa itace wacce aka aikosa yayi ƙiranta..
Sai alokacin Zahrah taɗago kanta ta kalli yaron, haka nan taji gabanta yafaɗi, to waye kenan yake sallama da'ita? ta tambayi kanta, wayarta dake kusa da'ita ta ɗauka haɗe da dubawa, 1 missed call tagani na Dr.Sadeeq, dayake wayartata a silent tasanyata shi yasa bataji ƙiran nasa ba, kenan shine yazo yaƙira wayarta bata ɗauka ba shiasa yaturo yaro. "Jekace inazuwa" ta bawa yaron amsa a taƙaice..


Miƙewa tayi haɗe da tattara takardunta tayi ɗaki. Mayafi taɗauka ta yafa akan kayan dake jikinta...


Tsaye yake ajikin motarsa yayinda yakifa kansa asaman motar yana me kaɗa key ɗin motarsa dake riƙe a hanunsa..


Kanta a ƙasa tafito daga cikin gidan tana me duba wayar dake hanunta. Tsayawa tayi cak bayan ta haɗe wani miyau dayazo me ɗaci ya maƙale mata a maƙoshinta.


Murmushi yasakarmata haɗe da soma takowa zuwa gareta..
Lokaci ɗaya idanun Zahrah suka sauya kala daga fari zuwa ja, juyawa tayi a fusace tanufi hanyar shiga gida, da sauri Zaid yasha gabanta haɗe da marairaice fuska cike da tashin hankali yasoma cewa....


"Dan Allah Zahrah kitsaya ki saurareni, dan Allah kada kimin haka Zahrah, inaso ki saurare....." kasa ƙare maganar nasa yayi sakamakon kyakkyawan marin da Zahrah ta shimfiɗa masa akan kyakkyawar fuskarsa...
Cikin ƙuna da kuma zafin zuciya haɗi da raɗaɗi Zahrah ta haɗa yatsanta na tsakiya dakuma babbar yatsarta, ta kaɗa ade de fuskar Zaid duk da kuwa cewa yakerema tsayinta..


"Natsaneka tsana mafi muni, natsani jin kowani irin kalma ce da zata fito daga bakinka, wlh wlh nayi rantsuwa sau biyu, idan har ka sake naƙara ganin fuskar ka to zanyi maka abun da baka taɓa tunani ba!" cikin matsanancin ɓacin rai taƙare maganar tana me raɓan gefensa zata wuce, Zaid da zuciyarsa tariga da ta karye baiyi ƙasa a guiwa ba yasake shan gabanta.


"Kimin duk abun da kikeso Zahrah, zanfi jin daɗima idan akace kece zakiyi silan mutuwa ta, dan Allah ki saurareni mana Zahrah!!" yaƙare maganar cikin rawan murya...


Kuka ne ya ƙwacewa Zahrah me tsanani cikin muryan kukan tasoma cewa.....


"Miye laifina Zaid? Menene aibuna? shin wani abu na aikata maka da ka zaɓi cutar da rayuwata? ashe de ganganci ne don na ɗau soyayyata na baka? me yasa ka yaudareni Zaid? meyasa dole saini kazaɓi ka tozarta? Kacutar da rayuwata ka dasamin ƙunci a cikin zuciyata, wlh natsaneka Zaid, Idan har yaudara zata zamemaka abun ado mezaka amfana dashi acikin rayuwarka? Miye ribar aikata zina da fasiƙanci? Natsaneka Zaid! Natsaneka!! Bana fata Allah yaƙara haɗa fuskata da taka fuskar har gaban abada! Dan Allah kafita a rayuwata Zaid!!!" cikin matsanancin kuka taƙare maganar tana me durƙushewa ƙasa domin kuwa zuwa yanzu tsayuwa ya gagarewa ƙafafunta...


Idanun Zaid ne suka kaɗa suka zama jajur dasu tamkar wanda aka zuba musu jan barkono. gaba ɗaya jikinsane yasoma ɓari, shi ɗin ma durƙusawa yayi agabanta cikin murya me tsananin rauni yaƙira sunanta,, saurin ɗaga masa hanu Zahrah tayi alaman batason jin komai daga garesa..


"Banason nasake koda jin muryarkane Zaid, kafita a rayuwata, wai mekake nema dani ne? ko kana tunanin zan sake aminta da kai ne? hmmm kayi babban kuskure Zaid idan kuwa har haka kake tunani, zaifi maka kyau, kamanta dani kakuma manta da wacece ni, ni na barwa Allah cutarwan da kayi agareni, kuma insha Allah nasan zai ɗaukarmin fansa,, sai de inaso kasani cewa har abada bazan taɓa yafe maka ba, inaso kuma kada kamanta da cewar natsaneka !" a fusace ta faɗa cikin gida haɗe da banko ƙofar gidan nasu.


Tashi yayi daga durƙuson da yake haɗe da bin bayanta da kallo, gaba ɗaya zuciyarsa tagama karaya, wani irin abu yakeji ajikinsa yayinda kansa yayi masa wani irin masifaffen nauyi, zafi yakeji azuciyarsa irin sosai ɗin nan.


Zahrah kuwa zamewa tayi jikin ƙofar gidan nasu tasaki wani irin kuka me tsuma zuciya. Se yaushene zata warke daga raɗaɗi dakuma ciwon abun da Zaid yayi mata? ganinsa yasake tasomata da mikin daya ƙi warkewa tsawon lokaci acikin zuciyarta, maiyasa Zaid yazame mata bala'i acikin rayuwarta? kuka tashiga yi sosai da sosai...


Zaid kuwa daƙyar ya iya jan ƙafafunsa yanufi motarsa, kasa tuƙa motar tasa yayi, gaba ɗaya idanunsa duhu suke gane masa, tabbas bazai taɓa iya tuƙa mota yana a irin wan nan halin ba,, da ƙyar ya'iya laluɓa wayarsa yaƙira driver'nsa... Mintuna kaɗan drivern Zaid yazo ya wuce dashi....


Saida tayi kukanta son ranta har sai da taji kanta yasoma ciwo kafun ta tsagaita, haɗe da miƙewa daga jikin ƙofar tashige cikin gida, direct ɗakinta ta wuce ta kwanta numfarfashi kawai take sauƙewa, lokaci ɗaya zazzaɓi yarufeta, harsaida tajawo mayafi ta lulluɓi jikinta....


Sanda yashiga falonsa ko gani bayayi sosai, wani irin ciwo kansa ke masa me tsanani wanda yasanya idanunsa sukayi nauyi, da ƙyar ya'iya jan ƙafansa yashiga ɗaki, kalaman Zahrah ne sukeyi masa yawo acikin kansa,, yatsani jin kalmar tatsaneshi da take yawan faɗa ɗin nan, wlhy a gurinshi da ta faɗi wan nan kalman gwamma ta sharara masa maruka koda kuwa guda biyarne akan ƙuncinsa.. Ya yanke shawara da de yakasance a irin wan nan yanayin ya gwammace yafita daga cikin hayyacinsa idan yaso bayan wasu tsawon lokaci yadawo cikin hayyacin nasa,, wasu ƙwayoyin magani yaɗauko harkala biyu, wanda suke gusarwa mutum da hankalinsa, maganin suna da hatsari sosai hakan nema yasanya ba'a sai dasu a bayyane sai de a ɓoye, kuma suna mugun sa bacci sosai... Saida ya ɓalli guda uku uku daga jikin kowani sachet, kafun ya watsa maganin cikin bakinsa, wan nan karon ko ruwa baisha ba haka ya haɗiye magungunan, yanda kalaman Zahrah ke dawowa cikin kunnensa yafi komai ɗaga masa hankali, kwanciya yayi lamo akan gado yayinda yake ƙwato numfashinsa dake ƙoƙarin ƙwace masa da ƙyar. wani irin fusga numfashinsa yayi lokaci ɗaya kuma komai najikinsa ya sake...


Zahrah kuwa zazzaɓine ya dirarmata me zafin gaske, wanda yasanya lokaci ɗaya jikinta yasoma ɓari ta fara rawan ɗari, har zuwa yanzu hawayenta bai tsaya ba. Zaid ya cuceta itakam duk irin ƙuncin daya jefata a baya bai ishe saba saida yakuma da wowa gareta, sai yaushene hawayenta zasu tsaya? sai yaushene zata samu farinciki ingantacce wanda babu algus acikinsa? tunda ta haɗu da Zaid ƙuncin rayuwarta yasoma, wani irin annoba Zaid yazame mata ne?.....


*(Kuyi haƙuri kuyi manage da wan nan, headache ke damuna, nida Zaid duk cutarmu ɗaya😜 banyi posting da wuri ba wlh network ɗin sim ɗi nane gaba ɗaya ya ɗauke😥)*


*29/December/2019*


*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*SHU'UMIN NAMIJI !!*



*Written By*
*Phatymasardauna*


*Dedicated To My Brother KHABIER*


*🌈Kainuwa Writers Association*


_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_


*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*


*WATTPAD*
@fatymasardauna


*(💗Wannan page ɗin baki ɗayansa kyautane agareku my wattpadi'ans inagodiya sosai a gareku💗)*


*Editing is not allowed📵*



*CHAPTER 72 to 73*


Baki Labisat dake tsaye taturo gaba haɗe da ɓata fuskarta duk wai akan don Mom ɗinsu tace taƙira mata Zaid a ɓangarensa ne yasa take wan nan abun...


"Tsayuwan uban me kike bacewa nayi ki ƙiramin yayanki ba!" Mom tafaɗi haka cike da faɗa, ganin Labisat ɗin bata da niyar zuwa aiken datayi mata.


"Mom wlhy tsoro nakeji kada naje ya masifance ni!" Labisat tafaɗi haka cikin shagwaɓa.


Harara Mom tawurga mata bashiri Labisat takama hanyar fita daga cikin falon...
Aranta kuwa roƙon Allah take yasa idan taje kada ya masifanceta saboda shi abun faɗa baya masa kaɗan ko kaɗan, jiya jiya dawowanta daga boarding school amma Mom zata haɗata da masifan Yaya Zaid (Su yaya manya😂)


Kusan sau huɗu Labisat tana knocking ƙofar daze kaita cikin falonsa, amma shiru ba amsa, hakan yasanya tatura ƙofar tashiga,, bakowa acikin falon sai daddaɗan ƙamshinsa dake tashi.. Direct ƙofar bedroom ɗinsa tanufa haɗe da soma knocking ƙofar,, jin shiru ne yasanya tashiga ƙiran sunan sa...


"Brother! Brother!" ko gyaran murya bataji yayiba balle tasa ran zai amsa mata, batama tabbatar yana cikin ɗakin ko baya ciki ba..
Gajiya tayi da knocking ƙofar ta juya tayi tafiyarta...


"Mom inaga fa kamar Bro bayanan domin nayita knocking door ɗinsa amma bai amsa ba"


"Tabbas yana cikin gidan nan Labisat domin kuwa tunjiya daya shigo baifita ba, har me gadi na tambaya naji ko yaga fitarsa amma yacemin tunjiya daya shigo bai fita ba, miskilancin nasa ne ya motsa, banaje dakaina nasa mesa nikam ae be isa yanunamin halin ƙyaliya ba" Mom tafaɗi haka tana me miƙewa tsaye daga zaunen da take..


Itama ɗin de knocking tayi masa haɗe da ƙiran sunansa amma shiru bai amsata ba, hakan yasa ta murɗa handle ɗin ƙofar ta kutsa kanta ciki bakinta ɗauke da sallama..


Tsuka Mom taja sakamakon ganinsa da tayi kwance akan gado yayi ruf da ciki, lallai ma wato iskancine ya hanasa amsa mata, da fari hartayi zaton ko baya gidan ne..


"Zaid!" taƙira sunansa cikin kakkausar murya... Ko motsawa baiyi ba balle tasaran ze amsa mata..


Kafeshi da idanu tayi tana me nazartarsa, a iya saninta da Zaid baya bacci a irin wan nan lokacin, impact ma shiba mutum bane ma'abocin yawan bacci ba'a bisa ƙa'ida ba, idan kuwa harda gaske baccin yake to baya rasa ɗayan biyu kodai baida lafiya ko kuma yayi halin nasa nashan ƙwayoyi, "Sai yaushene Zaid ze san ya girma? sai yau shene zai dena nuna rashin damuwa da lafiyarsa?" tajeromawa kanta waƴan nan tambayoyin, "Haƙiƙa Zaid ɗanta ne amma ita kanta har yau batasan wani irin haline da shi ba, shi mutum ne me nuƙu nuƙu bakoda wani lokaci ne kake sanin gaba da bayansa ba, haka nan yake bakomai ne zaka masa ƙa burgesa ba yanada wani shegen shu'umin hali saide kawai Allah yashirya mata shi"...


A hankali tashiga takawa zuwa gaban gadon nasa..


Idanu Mom tasake warowa waje, tabbas idan de idanunta de de suka gane mata to kuwa Zaid baya numfashi, domin babu wata alamar da take nuna akwai nunfashi a tattare dashi saboda ko cikin sa baya motsawa, alama ta baya shaƙan numfashi kenan..
Hanunta takai setin hancinsa ko da zataji ɗumin numfashin sa.


Salati Mom tasa haɗe da dafe ƙirjinta, sakamakon wani irin bugawa da taji zuciyarta tayi.


"Zaid!Zaid!" Mom tashiga ƙiran sunansa cikin tashin hankali haɗe da soma jijjigasa.
Hawayene suka shiga bin ƙuncin Mom bashiri ta fita daga ɗakin, direct ɓangaren Alhaji Ma'aruf ta nufa saboda yana gida baikai ga fita office ba..


"Alhaji! Alhaji! katemaka wlhy Zaid baya numfashi zo muje ka gani, katemakeni kada na rasa ɗana mafi soyuwa a gareni!!" gaba ɗaya cikin tashin hankali Mom keyimawa Dad bayani..


Mamaki haɗi da al'ajabi ne yakama Alhaji Ma'aruf amma de yanzu balokacin tambaya bane gwamma yabita yaga meke faruwa da Zaid ɗin....


Shima sosai ya tsorita kuma hankalinsa yatashi daganin Zaid yashe a gado baya numfashi sai kace gawa...


Da ƙyar Abba ya'iya sungumarsa yasanyasa a mota, abunka da ƙaƙƙarfa kuma ma'abocin yin gym shiasa jikinsa yake ko ina a murɗe, san nan kuma me ƙaramin ƙarfi bazai iya ɗaga sa ba, Dad ɗin ma saida temakon Mom ya iya ɗagasa... Daga Mom har Labisat hankalinsu amatuƙar tashe yake haka suka shiga mota suka rankaya zuwa asibiti...


Direct Emergency aka kai Zaid cikin gaggawa likitoti suka shiga basa temakon gaggawa...


Jigum jigum haka Abba da Mom sukayi a wani ɗan corridor dake kusa da ɗakin da aka kai Zaid, iya ƙololuwar tashin hankali sun shigesa, kuka kawai Mom da Labisat keyi, kasa koda rarrashinsu Alhaji Ma'aruf yayi domin shima da akwai hali da kukan ze sanya ko da zaiji sassauci a cikin zuciyarsa...


Likitotin nan sunci baƙar wahala kafun da taimakon Allah suka samu suka daidai ta numfashin Zaid. Haka suka fito suna sharce gumi.... Kallon Alhaji Ma'aruf ɗaya daga cikin Doctors ɗin yayi haɗe da cewa "Ranka ya daɗe muje office" ƙoƙarin binsu Mom tasomayi Alhaji Ma'aruf yaɗaga mata hanu alamar tajirasu....


Handkerchief likitan nan yaɗauka ya ƙare share gumin dake tsatstsafawo akan goshin sa..
Ganin haka yasa Abba cike da tashin hankali yace "Yade Dr.Bilal meke faruwa ne, dan Allah kada kafaɗamin wani mummunan labari!"


Jinjina kai Dr.Bilal yayi haɗe da kallon Dad. "Kwakwantar da hankalinka Alhaji zuwa yanzu komai ya daidaita munshawo kan matsalan"


Nannauyar ajiyar zuciya Dad yasauƙe haɗe dayin hamdala acikin ransa...


Sake gyara zama Dr.Bilal yayi haɗi da cewa "Sai de kuma agaskia bazan ɓoye maka ba Alhaji ɗan ka yana cikin matsala wanda yake gab da rasa rayuwarsa matuƙar baikiyayewa kansa shan ƙwayoyi masu mugun haɗari ba, baya ga haka kuma idan har ya cigaba dashan giya nan da ƴan kwanaki tofa sai de kuma abun da Allah yayi!"


Yanzukam Dad ne yashare gumi ba Dr.Bilal ba, domin kuwa a iya tsawon rayuwarsa baitaɓa sanin Zaid nashan wasu ƙwayoyi masu bugarwa ba, yade san da ya nashan giya amma kuma atunaninsa yajima da dena shan giyan.


"Bangama fahimtarka ba likita, naji kace ƙwayoyi na bugarwa, kana nufin shiɗin ne yakeshan ƙwayoyin bugarwa?" Dad yatambayi Dr.Bilal cike da son sanin ƙarin haske akan batun..


"Wato a iya bincikenmu mungano cewa akwai wata ƙwaya me haɗarin gaske da yakesha lokaci zuwa lokaci, wanda kuma haɗarin ƙwayar yana da matuƙar yawa, bazanyi mamakin a ina yasamu ƙwayan ba, saboda nasan shiɗin isashshene, saboda ƙwayar ba ako ina ake samunta ba, a ƙa'ida ma anhana shigo da ƙwayar nan gida Nigeria, kawai de rayuwar yanzune da ta zama sai a hankali, zai iya yuwuwa kuma ba anan yake sayan ƙwayan ba daga can waje yake shigowa da abarsa, sai de kuma wan nan duk bashine damuwar ba, idan har ya cigaba da shan wan nan ƙwaya to ina me tabbatar maka da cewa zai iya rasa ransa ako da yaushe, duk da kuwa dama munsan mutuwa tana kan kowa yanzu ko anjima, amma tabbas kiyayewan shine yafi, san nan kuma giya tayi masa mummunan illa saboda tasamu mafaka acikin cikinsa, wataƙila yamai da ita ruwan shansa ne, amma kuma duk hakan ba wani babban matsala bane idan har ze kiyaye to da taimakon Allah komai zezo masa cikin sauƙi!"


Salati Alhaji Ma'aruf yayi a bayyane haɗe da sanya hanu yazame hular dake kansa, ashe bayan giya hadda wata tsinanniyar ƙwaya me haɗari Zaid yake sha? anya kuwa Zaid yanada cikakken hankali? shin wani irin haline haka da Zaid? amma babban abun tambayar shine laifin waye acikinsu, laifinsune su iyayensa kokuwa laifinsa ne shi kansa Zaid ɗin?


"Haƙiƙa dukansu suna da laifi, amatsayinsu na iyaye basu wani tsaya sunbawa Zaid kyakkyawar kulawa ba, kuɗi kawai suka sake masa haɗe da turasa makaranta har wata uwa duniya, amma duk da haka bekamata ace yakasance haka ba, idan su basa lura da al'amuransa shi ɗin mahaukaci ne da be san dede ba? tabbas yasan shiyake da alhakin kulawa da tarbiyan Zaid tunda shine yaɗaukosa daga wajen Mahaifiyarsa yadawo dashi America kusa dashi, tunda suke America bai taɓa tsayawa da kyau yakula da wani irin rayuwa Zaid ɗin keyi ba, shide kawai yabuɗe masa bakin aljihu yana ganin hakan shine gata, ƙwarai mafiyawancin iyaye ayanzu sunfi bada kulawarsune ga Ƴaƴa mata, yayinda ƴaƴansu maza kuwa ko oho, duk wata kyakkyawar tarbiya Ƴaƴa mata ake ƙoƙarin koyawa, yayinda Ƴaƴa maza kuwa suka
End Ads