x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 4 - SHU'UMIN NAMIJI

  • 9001 words
  • 12000 words
  • Out of 185824 words

Category: Romance Story +18

Views 202

10 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
jikinsa da shu'umin turarensa mai rikirkita ƴan mata,, haƙiƙa Zaid yana da kyau mai burgewa, Zaid haɗaɗɗen Namiji ne wanda kowacce mace idan tagansa saita ƙyasa, bazan iya misalta muku haɗuwar Zaid ba amma Zaid ya wuce duk inda kuke tunani,ga kuɗi ga kyau, shiyasa yake abun da yakeso,,, car key ɗinsa ya ɗauka haɗe da ficewa daga cikin ɗakin,, kaitsaye parking space ɗinsa ya nufa, haɗaɗɗiyar motarsa ƙirar Range Rover blue colour yashiga haɗe da bata wuta yafice daga cikin gidan,, yana tuƙi amma earpiece ne sanye a kunnensa yanashan ƙiɗa, kai tsaye Unguwar Suleja yanufa,,




Zahrah ce zaune a tsakar gida, tana wanke mawa inna kayanta, sanye take da wata atamfa irin mai sauƙin kuɗinnan amma, duk da haka atamfar tayi mata kyau ajiki, Inna kuwa nagefe akishingiɗe tana sana'artata cin goro,, wani yaro ne yashigo cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, Zahrah ce ta amsa masa Inna kuwa ko kallonsa batayi ba, domin a tunaninta baraka dake binta bashine ta aiko mata,, " Wai Zahrah tazo inji wani a waje " yaron yafaɗa, zuciyar Zahrah ce tayi wani irin tsalle tamkar zata fito waje, yayinda inna dake kishingiɗe tamiƙe zumbur haɗe da cewa " Zahrah kuma ? kai yaro anya kaji da kyau kuwa ?" kai yaron yagyaɗa haɗe da cewa "Eh wani ne yace inkirata, kuma Zahrah yacemin,,


"Wanin dame yazo? a tsaye kagansa ? koko amashin ? kokuma dai amota ? yaro faɗamin da maiyazo ? " Inna ta tambayi yaron,, "Awata irin ƙatuwar mota yazo mai kyau " yaron yafaɗa, domin shidai abun daya gani zai faɗa,,


"hehehhe ! jekace tana zuwa ɗan yaro " Inna tafaɗa tana mai tashi tsaye, "To" kawai yaron yace haɗe da juyawa yafice daga cikin gidan,,


"Tashi maza maza kije kada ki ɓarar mana,, banza kinaji ana ƙiranki amma kinwani shantakewa a waje ɗaya " Inna tafaɗa tana mai hararan Zahrah, da take ƙame a waje ɗaya, gaba ɗaya hankalinta baya jikinta.... hijabinta dake rataye kan igiya tasanya haɗe da nufar ƙofar fita daga gidan cikin sanyin jiki,,, tana fitowa daga cikin gidan yakafeta da mayun idanunsa, haɗe da sanya harshensa ya lashi laɓɓansa, Zahrah kuwa ganin bataga kowa awajen ba sai mota yasanya ta juyawa daniyar komawa gida, *"ZAHRAH"* taji ankirasunanta da wani irin murya wanda bazata taɓa manta ta ba duk da kuwa cewa sau ɗaya tak ta taɓa jin muryar a rayuwarta,, saurin juyowa tayi don taga daga ina muryar tafito, daidai lokacin ya sauƙe glass ɗin window'n motar, idanunta sukai mata tozali da kyakkyawar fuskarsa wanda bazata taɓa mantashi ba har abada kuwa,, wannan shu'umin murmushin nasa ya yi mata haɗe da cewa " shigo mana, kodai tsorona kikeji ne ? " a hankali ta sauƙe idanunta daga kansa haɗe da kaɗa kanta alamar a'a, amma still tana tsaye bata shiga motar tasa ba, wani murmushin yakuma aika mata haɗe da buɗe murfin motar tasa yafito, saida yazo gab da'ita kafun yatsaya haɗe da sanya hanunsa yaɗago haɓarta, wanda hakan yasanya ta jefa idanunta cikin nasa, " Haka kikafiso ko ? kowa yazo wucewa yaganmu tsaye ?" yaƙare maganar yana mai rage girman idanunsa,, wani irin zubawa tsikar jikin Zahrah ya shiga yi, saurin ja da baya tayi domin kusancin nasu yayi yawa,, batare daya sake ce da'ita komaiba yajuya yashige cikin motarsa, haɗe da buɗe mata ƙofar mai zaman banza, cikin sanyin jiki Zahrah tashiga cikin motar amma bata rufe ƙofar motar ba, saishi ne ya jawo ƙofar yarufe da kanshi, kallonta Zaid yashigayi harnatsawon minti biyu kafun yayi murmushi, haɗe da cewa "Baki iya gaisuwa ba ne ?" wani irin kunya ne yakama Zahrah kwata kwata ita tama manta da ana gaisuwa, gaba ɗaya ganinsa ya ruɗata,, "Inawuni " tafaɗa cikin sassanyar muryarta,, "bani amsawa saida ma na roƙa " yafaɗa yana ɗan hararanta, ɗan guntun murmushi kawai tayi haɗe da sake sunkuyar da kanta ƙasa, tanamai wasa da yatsun hanunta, "Zahrah!!" yasake ƙiran sunanta cikin kasalalliyar murya, kasa amsawa Zahrah tayi saima ɗago kanta da tayi taɗan saci kallonsa, haɗa idon da sukayi yasa tayi saurin maida kanta ƙasa,, "Bakiyi mamakin zuwa na ba ?" yajefo mata tambaya, alokacin da bata shirya ba, da ƙyar ta'iya cewa "nayi" satan kallonsa tayi ta gefen ido, "Idan namiki kyau ne kijuyo kikalleni da kyau, bawai ki tsaya kina satar kallo naba, yafaɗi maganar kaitsaye, wani irin kunyane yakama Zahrah sam batasan cewa yana ankare da'ita ba, da sauri ta cusa kanta tsakankanun cinyoyinta, haɗe da ɓoye fuskarta, gyara zama Zaid yayi haɗe da cewa " dama nazo na ganki ne, kuma naganki zaki iya tafiya tunda kunyana ma kikeji " yafaɗi maganar ataƙaice, ahankali tabuɗe murfin motar da sauri tafice bata ko waigo tasake kallon sa ba, tashige cikin gida,, yana ganin wucewarta cikin gida, yasauƙe ajiyar zuciya haɗe da sakin ɗan guntun murmushi, "da sannu zaki shigo hannu " yafaɗa acikin zuciyarsa, wani yaro dayake wucewa yaƙira haɗe da basa wata ƙatuwar leda yace yakai gidan su Zahrah'n, daganan yayi mawa motarsa key yabar cikin unguwar tasu,


Zahrah nashiga gida yaro yabiyota da ƙatuwar leda, "wai inji wani a waje" har Inna najin tuntuɓe wajen ƙwatan ledan ahanun yaron, "to, to,to kace angode ko yaro" Inna tafaɗa tana washe baki, yaron baice da'ita ƙalaba yafice da ga cikin gidan,, zama Inna tayi akan tabarma haɗe da zazzage ledan, kayane suka soma faɗuwa acikin ledan saikuma bandir ɗin kuɗi ƴan dubu dubu ɗauri ɗaya daya faɗo, waro idanu Inna tayi haɗe da dafe ƙirji, afili tace " Nashiga Uku ni Salma mainake gani haka, ke Zahrah ɗan fashi, ko ɗan yankan kai, kika jajiɓo mana? " Zahrah dake ɗaki jin abun da Inna kecewa yasa tayi saurin fitowa danganin meke faruwa,, turus itama tayi domin ganin abun dake zube agaban Inna, ɗaukan kuɗin Inna tayi tashiga juyawa, haɗe da washe baki, "Lallai ko ma waye ne wannan mutumin dayazo wajenki Zahrah baƙaramin mai kuɗi bane " Inna tayi maganar tana mai shunshina kuɗin hanunta, saurin cusa kuɗin tayi aƙasan ƙugunta, haɗe da soma juya kayan dake zube gabanta, dogin riguna ne ƴan ubansu kala uku sai lufayu, guda uku, dagani kai kasan masu tsadan gaske ne, kuɗin Inna taciro tasoma irgasu, dan tsabar naci saida Inna ta irge kuɗinnan tas dubu ɗari ne cus, dafe ƙirji Inna tayi cike da tsananin mamaki tace " Dubu ɗari awannan zamanin ? lallai ne inji masu faɗi sukace
arziki na'inda yake, aikuwa yau miyar zallan nama zamuci acikin gidannan, Allah yakashe ya bamu, ke Zahrah tsayuwan mekike ? maza ɗauko hijabinki kijemini bakin hanya nan kisayo mini ɗanyen nama da kuma danƙwaleliyar kaza ƴar gashi, yau bushasha zanyi " Inna taƙare maganar cike da farinciki, haɗe da wurgi da guntun goton dake hanunta,, cikin sanyin jiki Zahrah takoma ɗaki taɗauko hijabinta, kuɗi takarɓa a wajen Inna, kai tsaye tawuce aikan da Innan tayi mata, zuciyarta fal da tarin tambayoyi haɗe da tunani.....


Zaid kuwa daga wajen Zahrah guest house ɗinsa ya wuce, bayan yabiya yaɗauko sabuwar karuwarsa da yayi, maisuna Laylerh,,


Gaba ɗaya Zaid ya ruɗe ganin da yayi mawa Lylerh tsaye a gabansa tsirara haihuwar uwarta, saiwani banƙaro masa ƙirji takeyi, duk don ta ɗauke hankalinsa, duk dacewa ba irin macen da bai gani ba, amma Lylerh ta ɗan rikitasa, domin ta nada abun dayake so sosai ajikin mace wato breast, shi namiji ne mai son breast sosai, madaran holandia dake riƙe ahanunsa, yashiga zuba mata akan nonuwanta harzuwa ƙafanta,, bakinsa ya ɗaura akan nononta yashiga tsotson su haɗi da lashesu, yayinda yazura yatsansa ta ƙasanta, yana mai wasa da gabanta, a hankali, babu inda Zaid baibi yasuɗe ajikin Lylerh ba, cikin zafi zafi yake murza breast ɗinta, hanunsa kuwa yajima da nutsewa aƙasanta, duk kuwa yanda Lylerh taso su haɗa baki da Zaid yayi kissing ɗinta ƙiyawa yayi, sai dai yayi romance ɗinta yadda yaka mata, kwantar da'ita yayi flat akan gado, yayinda ya haye saman ruwan cikinta hannayensa yakuma ɗaurawa akan breast ɗinta yashiga murzawa, yayinda ya shiga goga bananarsa a dai dai wajen fitsarinta,, wani irin shishita Lylerh keyi domin ko ahaka Zaid ya barta ta gamsu, cike da ƙwarewa Zaid ke sanya bananarsa cikin HQ ɗin Lylerh, saida yatabbatar dacewa tanutse ciki kafun yasoma aiki, gaba ɗayansu hankalinsu baya jikinsu, domin sunyi nisa wajen aikata zina,,, balaifi Zaid yasamu gansuwa da Lylerh, domin dai Lylerh ta tsuma kanta da maganin mata yanda yakamata,, kuɗi masu yawan gaske Zaid yabamawa Lylerh, amatsayin ladan iskancin da yayi da'ita, duk da cewa itaɗin ba gadon tsiya bace, domin Babanta mai kuɗi ne sosai.....








*16/October/2019*


*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*SHU'UMIN NAMIJI !!*




*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*




*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*




*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*


*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*


*WATTPAD*
@fatymasardauna




*Editing is not allowed 📵*




(```kuyi haƙuri two days kunjini shiru, abubuwane sukai min yawa..```)




*Chapter 10 то 11*




Zahrah ce kwance a ɗaki, bayan ta dawo daga aikan da Inna tayi mata,, zuciyarta cike take da saƙe saƙe kala kala, na farko tanason sanin wayeshi, maikuma yakawosa gidansu, haƙiƙa tasan cewa ya girmewa ajinta, amma sai gashi zuciyarta ta maƙale da tunaninsa, duk yanda taso manta shi a cikin zuciyarta hakan yagagara, amma cire tunaninsa acikin zuciyarta yazama dole, domin kuwa hanyar jirgi da ban, ta mota ma da ban,,,, a ranan nan da ƙyar bacci ɓarawo yayi awun gaba da Zahrah, dazaran ta kulle idanunta, kyakkyawan murmushin sa ne ke yi mata gizo....


Yau tana ƙirga wa kwanansa shida kenan dazuwa wajenta, amma har izuwa yau ɗin tunaninsa yakasa barinta tayi sukuni, bakomai yafi ɗaukar hankalinta a tattare da shiba kamar ƙawataccen murmushinsa mai burgewa, (Murmushin shu'umanci) uwa uba kwarjininsa yana ruɗata, wani irin son sake ganinsa takeyi...



A ɓangaren Zaid kuwa abubuwane sukai masa yawa, yayinda hankalinsa ya karkata zuwaga harkan kasuwancin sa, kwata kwata baya samun zama, amma komai yake Zahrah na maƙale a ransa, burinsa ɗaya shine Allah yakai damo ga harawa, ko baici ba yayi birgima, har ya hasasho, yanda zai keta mawa Zahrah rigar budurcinta, tun da yaganta yayi rantsuwa, cewa sai ya ɗanɗani zumanta, kuma bazai bar rantsuwarsa yatafi a banza ba...


Zahrah na zaune a tsakar gida, idanunta kekan handout ɗin dake riƙe a hanunta,, idan kayi mata kallon farko zakai zaton karatu takeyi, amma idan kakuma kallonta, to akasin haka zaka gani, domin gaba ɗaya hankali da tunanin ta ya tafi ga Zaid ya hanata sakat, karatun ma bako da yaushe yake shiga kanta ba,, wani yaro ne yashigo cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, Inna ce tayi saurin amsa masa, "Wai ana ƙiran Zahrah a waje " yaron yafaɗa, baki Inna ta washe haɗe da cewa "ɗan albarkan nanne yazo na sani, je kace gatanan fitowa yanzu yanzun nan " wani irin bugawa zuciyar Zahrah tayi, hakanan ta tsinci kanta da faɗuwar gaba, take kuma taji zuciyarta tayi sanyi,, lufayan da Inna ke miƙo mata ta amsa haɗe da zurawa ajikinta, kaitsaye tafice daga cikin gidan,,,
Tsaye yake a jikin motarsa yasha ado cikin wata blue shadda, sosai kayan yayi masa kyau, domin kuwa shiɗin ma ba baya bane wajen kyau,, turus haka Zahrah taja ta tsaya, ganin wata baƙuwar fuska ba wacce take tsammani ba,, murmushi yayi mata haɗe da yi mata nuni almar ta ƙaraso,, gaba ɗaya jitayi farincikinta ya gushe, sam bashi taso gani ba, taso ace Mai kyau (Zaid) ɗinta ta gani,, cikin sanyin jiki ta ƙaraso inda yake haɗe dayi masa sallama,, amsa sallamar nata yayi fuskarsa cike da fari'a,, sake gyara tsayuwa Jabeer yayi haɗe da cewa " kiyi haƙuri a wancan lokacin na tsaidaki a'inda bai dace ba, amma yanzu gani nabiyoki har gida, ina fata zakiyi marhaba da zuwana "


Ɗan jim Zahrah tayi, domin ita bata da wani amsa da zata basa, ganin haka yasanya Jabeer ci gaba da cewa " kamar yanda na faɗamiki a farko ni sunana Jabeer, ina zaune ne a unguwar asokoro nida mahaifana, ni ma aikacik banki ne,, tun daga randa na fara ganinki na ji na kamu da soyayyarki, idan har bazan takuraki ba inaso kibani dama don gwada sa'ata agareki... " Jabeer yaƙare maganar yanamai kallon Zahrah, ɗan jim Zahrah tayi kamar wata mai nazari, ita dai batasan maizatace dashi ba, domin ita bata taɓa soyayya ba, kuma ita batama jisa acikin zuciyarta ba,,, ganin bazatace komai ba yasa Jabeer cigaba da yi mata bayanin kansa, haɗe da ƙoƙarin kafa gwamnatin sa wajen ta,, daga ƙarshe dai cewa tayi yabata dama tayi tunani,, yakoji daɗin hakan domin yanasa ran cewa zai samu karɓuwa a wajenta,,,, koda tazo tafiya maƙudan kuɗaɗe ya bata, amma sam Zahrah taƙi amsa, bayanda baiyi da'ita ba akan ta amsa amma taƙi, dole ya haƙura, saida yaga shigewarta gida kafun yayi mawa motarsa key yafice a unguwar tasu baki ɗaya........


Zahrah nashiga gida Inna tayo kanta tana mai cewa " Mai arzikin nan ne ko ? bansan a'ina kika samosa ba,amma gaskia banaso ya kuɓuce mana, saboda haka kiriƙesa da kyau "


cikin sanyin Murya Zahrah tace "Bashi bane Inna, wani ne daban" wata uwar harara Inna ta doka mawa Zahrah haɗe da cewa "to idan bashi bane wani ɗan iskan ne ? nifa kinganni nan banson harka da talakawa, domin a gaskia bazan ƙare rayuwata cikin talauci ba ehe, in ma baƙin ciki ne yasa kika kori mai arzikinnan to yazama dole ki bashi haƙuri ya dawo, kam bala'i ga samu gakuma rashi, ina bazai yi wuba, shi wannan ɗin a mai yazo ba dai a ƙafa ba ?"


"a mota" Zahrah tayi maganar kai tsaye, sam batajin daɗin abun da Inna keyi, shigewa ɗakinta tayi, yayinda tabar Inna tsaye tana faman ɓaɓatu ita kaɗai a tsakar gida....


Jigum tayi, zuciyarta cike da tarin tunani kala kala, "Bazai zo ba, dama nasan ya girmewa ajini, mai yasa nadamu dashi ? maiyasa nake yawan tunasa akowani lokaci ? maiyasa zuciyata keson jefa kanta inda bata dace da zuwa ba ? yazama dole na daina tunasa kwata kwata a rayuwata, to amma yazanyi da wannan daya kawomin tallen soyayarsa gareni ? " Zahrah tayi maganar a fili,, haka dai Zahrah tayi ta saƙe saƙe acikin zuciyarta...


Bayan Kwana biyu da zuwan Jabeer....


Misalin ƙarfe 8:30 pm, Zahrah ce kwance akan ƴar yalolon katifarta, yayinda idanunta ke lumshe, da'alama bacci keson ɗaukarta.... Shigowar Inna da sauri cikin ɗakinnata shiya sanya tayi saurin buɗe idanuwanta, domin shigowar Inna ɗakinnata a dai dai wannan lokacin bainuna alamar lafiya.... " Miye kika wani zura min idanu kamar mayya, tashi kije waje wannan mai arzikinne yakuma da wo wa " Inna ta faɗa cike da zumuɗi,, dumm haka ƙirjin Zahrah ya buga,, ganin Zahrah tayi saƙare yasa Inna, cewa "zaki tashi kijene kokuwa saina mangareki " sumi sumi Zahrah tamiƙe haɗe da ɗaukar hijabinta tana ƙoƙarin sanyawa a jikinta,, saurin fusge lufayar Inna tayi haɗe da wurgi dashi gefe, wani gyale dake hanunta, ta miƙomawa Zahrah'n haɗe da cewa " ungo yafa wannan banson wannan shirmen koda yaushe kina nanuƙe da lufaya kamar wata mayya !" badon Zahrah taso ba haka ta yafa gyalen da Inna ke miƙomata, har zaure Inna ta raka Zahrah, saida taga ficewarta kafun ta koma gida,, kasancewar gari gaba ɗaya yayi duhu hakan yasa bata iya hango wanda ke cikin motar, kuma zuciyarta bata bata akan cewa shiɗinne ba, saboda ba motar da yazo da'ita ranan bane watace daban,, don haka tafara zaton ko bashi bane,, wani irin daddaɗan ƙamshine yashiga yawo acikin ƙofofin hancinta, kallonta ta maida izuwa inda ƙamshin ke fitowa, mutum ne tsaye a wajen amma bazata iya shaida ko waye bane, saboda duhu,, wani irin tsoro taji yakamata kaddai mai satan mutanene yabiyota har gida, da sauri tajuya don komawa gida, taku ɗaya yayi kacal, ya cafko hanunta, wanda hakan ya haifar masa da zubawar tsikar jiki,, jawota yayi gab dashi, cikin wata irin murya yace " Shiiii idan kikayi magana saina yankaki !" jikin Zahrah ne yaɗauki rawa haɗe da ɓari, tsoro ne ya lulluɓeta a sakamakon jin abun daya ke faɗi, shikenan itakam Inna tajawo mata, tana zaman zamanta ta tilasta mata fitowa gashi wani zai yi garkuwa da'ita,, babban abun daya da gulamata lissafi, bai wuce yanda jikinsa da nata ke manne awaje guda ba, ga ƙamshin sa gaba ɗaya yagama rikitata,, a hankali ya ɗaura kansa a gefen wuyanta, wanda hakan yasanya tattausan sajensa gogar fatar wuyanta, lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗesu a lokaci guda, " Kinshirya mutuwa yanzu kokuwa ?" yaje fo mata tambayar data kusa tsinka ƴaƴan hanjinta,, cikin rawan murya tace "dan Allah kayi haƙuri kada ka cutar dani
End Ads