"Da gaske zaki iya takawa da ƙafa daga nan har gidansu Husnah? to shikenan tunda zaki iya, zaimafi kyau ki taka da ƙafan, saboda kisamu ki ɗan rage wan nan ƙiban dakika haɗa, gaba ɗaya duk yasa kin yi muni, kin zama wata super mama dake" yafaɗi haka yana me ƙare mata kallo.
Waro idanu Zahrah tayi haɗi da soma kallon kanta, wai tayi ƙiba, takuma zama super mama.
Take idanunta suka yi raurau dasu, yayinda ruwan hawaye ya soma cika cikin su, "ashe da gaske tayi ƙiba bata sani ba? gashi harya fara goranta mata, to me yasa ita bataganin ƙibanta?" tatambayi kanta...
Dariya Dr.Sadeeq yasanya domin kuwa yalura tayarda da maganarsa, shikuwa wasa yake mata, bawai dagaske tayi ƙiban bane, gashi har tana ƙoƙarin yin kuka, shikam ya lura gaba ɗaya kuka baya bata wahalar yi, hawayenta a maƙale suke, mintuna kaɗan saikaga sun tsiyayo"
"Kintsorata ne dan nace kinyi ƙiba? hmmm nan gaba kaɗan zakiyi bindiga ki fashe saboda tsabar ƙiba"
Sake waro manya manyan idanunta tayi zuwa yanzu kam har ƙwallan cikin idanunta sun gangaro akan fuskarta....
"Au kinfiso ki kumbura ki fashe ɗin kenan?" yatambayeta yana me danne dariyar da ta taso masa...
Kai ta girgiza masa alaman "A'a"
"To kinaso na faɗamiki me zakiyi wanda zaisa bazaki fashe ba?"
Dasauri ta ƙaɗa kai alamar tanaso yafaɗa mata...
"Yauwa ƴar gari ashe de kema bakyaso ki fashe, to abu ɗaya zakiyi wanda shizai hanaki fashewa, kinga de ni likita ne ko? nakumayi zurfi cikin karatun likitanci, saboda tsabar zurfin da nayi ina karatune ma yasanya nagano cewa idan mutum yacika matsantawa kansa da damuwa da kuma yawan koke koke to yakan iya kumbura kamar de yanda kikayi yanzu, daga nan kuma bayan kamar 1 week shikenan sai dai yayi bindiga yafashe fush, shikenan kuma sai de wani bashi ba, kinaso haka ta faru dake?" yafaɗi haka yana me zura mata manya manyan idanunsa.
"A'a" tabashi amsa cikin murya me sanyi, domin kuwa a haƙiƙanin gaskiya ta yarda da kalamansa, ko kaɗan bata gano cewa shiya shirya abunsa ba. take fargaba ya ɗarsu a zuciyarta....
Wata irin dariyane takama Dr.Sadeeq amma kuma ba halin yasaki dariyar tasa, dolensa ya danne ta matuƙar yanaso Zahrah ta gamsu da bayanan sa hundred percent,,, lallai yau yaƙara tabbatarwa kansa cewa Zahrah yarinyace kuma yarinta na damunta, amma inbanda haka ta'ina ta taɓa jin ance mutum ya yayi bindiga yakuma fashe da ransa.
Gyara tsayuwarsa yayi haɗe da cewa "To yanzu de zaɓi ya rage gareki Yarinya, ko ki daina kuka ko kuma ki fashe, saboda haka zaki biyoni muje ne ko kuwa a'a nayi tafiyata?"
Murmushin gefen baki Dr.Sadeeq yayi haɗe da juyawa yanufi wajen motarsa, yana me danne dariyarsa...
Zahrah kuwa tamkar wacce ƙwai yafashewa haka ta bi bayansa.
Saida suka hau titi kafun yajuyo da kallonsa gareta, gani yayi tayi jigum da'ita, da'alama tunani takeyi....
"Amma nace miki yawan sakai a damuwa shike sa mutum ya fashe ko? hala don ba ɓangaren likitanci kike karanta ba shiyasa bakisan da hakan ba"
Kallonsa tayi haɗe da ƙwaɓe fuska, cikin murya me sanyi tace "Ni ae yanzu bawai a damuwa nake ba, kawai de ina kallon hanya ne" ....
Kansa ya jinjina haɗe da cewa tayi masa kwatancen gidansu Husnah'n domin shi basani yayi ba....
A dai dai ƙofar gidan su Husnah ya tsaida motar tasa, haɗe da dawo da kallonsa ga Zahrah wacce ke ƙoƙarin buɗe murfin motar tayi ficewarta...
"Da yaushe zaki koma gida?"
Ɗan jim tayi kana tace "Ko zuwa bayan la'asar ma, irin ƙarfe biyar ɗin nan haka" yanayin yanda taƙai ƙarshen zancen nata tana me juya kyawawan idanunta, shi ya shagaltar dashi har ya tsaida idanunsa akan ta, sosai takeyi masa kyau idan tana juya idanunta, ya kuma lura cewa hakan al'adarta ne, idan hartana magana, to takan juya idanunta masu kyawun gani, musamman idan maganar tazo ƙarshe..
"Ya de?" Zahrah ta tambayeshi sakamakon ganin da tayi yakafeta da idanunsa..
"Babu, kikulamin da kanki kinji, zan zo na ɗaukeki idan 5 ɗin tayi, inafata babu wata matsala?" yatambayeta cike da nuna kulawa.
Murmushinta me kyau tayi masa haɗe da cewa
"Babu wata matsala"
Yana kallonta tabuɗe ƙaramar ƙofar dake jikin gate ɗin gidan su Husnah tashige... Yana tabbatar da shigewarta yayiwa motarsa key haɗe dayin reverse yaɗauki hanyar asibitinsu, saboda dama aiki yabaro yazo gareta, to yazaiyi tunda tazama wani ɓangare na jikinsa...
Da matuƙar farinciki Husnah ta rungume Zahrah tana mejin daɗin ziyarar bazata da Zahrah'n takawo mata, saboda bata faɗa mata zata zoba. Bayan Zahrah ta gaisa da Momyn Husnah ne, suka rankaya zuwa ɗakin Husna'n,,, ba ɓata lokaci Husnah ta cikawa Zahrah gabanta da kayan ciye ciye dasu drinks.
"Naji daɗin zuwanki sosai ƙawata, kamar kuwa kinsan ina kewarki, jiyafa har mafarkin ki nayi, da safe naƙira wayarki kuma najita switch off, ina fata dai kina lafiya?"
Hijabin dake jikinta ta cire haɗe da cewa "Lafiya amma ba sosai ba"
Da sauri Husnah ta dawo da kallonta ga Zahrah
"Meyafaru dear?" Husnah tatambaya cike da kulawa.
Kallon Husnah Zahrah tayi na tsawon minti guda....
Damuwane ya bayyana ƙarara akan fuskar Husnah haƙiƙa tamkar ƴar uwa ta jini take kallon Zahrah saboda haka duk wata damuwa ta Zahrah damuwar tace itama.
"Zaki iya ɓoyewa kowa damuwarki amma bandani Zahrah, sai de kuma babu amfanin takuraki akan cewa lallai sai kin sanar dani, saboda bansan wani hali zaki samu kanki aciki ba bayan kin faɗamin"
Dafa kaɗan Husnah Zahrah tayi haɗi da daure zuciyarta...
"Nasake haɗuwa da.... da....wanda ya yimin fya......." kasa ƙarasawa tayi saikawai tafashe da kuka.
Ko bata ƙarasaba Husnah tafahimci me Zahrah take nufi.
Cike da tashin hankali Husnah tasoma salati...
Sake jawo Zahrah jikinta tayi haɗi da rungumeta...."Ki daina kuka, yanzu ba lokacin kuka bane Zahrah, kinmaci abinci kuwa ?" Husnah ta tambayi Zahrah cikin kulawa...
"Banajin yunwa Husnah!" Zahrah tafaɗi haka cikin shaƙewar murya, wani yunwa zataji ita da take cikin bala'in sake ganin Zaid...
"Kinsan de ba kyau zama da yunwa ko, kinga yau ni namayi abincin dakaina, bana zuba mana muci tare, kuma dan Allah kada kicemin a'a"
Babu yanda Zahrah ta'iya dole tabiyewa Husnah taci abinci, gaba ɗaya Husnah se zuba take tamkar kurna, takasa yin shiru koda na minti biyu ne, tayi hakanne kuma saboda ta gusarwa da Zahrah da muwarta, daga ƙarshe de har game, Husnah ta jona musu a tv suka buga, sosai kuma hakan ya ɗebewa Zahrah kewa....
Tare sukayi sallan la'asar daga nan kuma Husnah ta ɗebi Zahrah, suka tafi shoprite, dangin su ice cream da chocolate suka jida, daga nan sukayo gida.
Kamar yanda yafaɗa ƙarfe biyar da minti ɗaya dai dai ya ƙaraso ƙofar gidansu Husnah.. Ƙiran Zahrah yayi a waya ya tabbatar mata cewa yana ƙofar gidan su Husnah....
Zahrah na ajiye wayarta Husnah ta kalleta haɗe da kashe mata ido ɗaya.
"Ƙawata tazama ƴar soyayya, sosai yanayin soyayyarku da Man ɗin nan yake kasheni, kinfasan gayen naki ya haɗu over, da badan ke bace danayi snatching ɗin sa!" cike da zolaya Husnah ta faɗi maganar...
Dariya suka sanya su dukansu, haɗe da rungume juna.
Har bakin motar Dr.Sadeeq Husnah ta raka Zahrah, bayan Momyn Husnah ta cikawa Zahrah leda da dangin su turare dakuma kayan shafa hadda kyautar wani haɗaɗɗen leshi, sosai Zahrah tayi godia, hakan kuma yana ɗaya daga cikin abubuwan daya sanya bata son zuwa gidansu Husnah, saboda idan dai tazo tofa sai mahaifiyar Husnah tayi ɗawainiya da'ita wajen bata kyautan kayayyaki masu kyau da tsada...
Harsaida Husnah taga tashin motar su Zahrah kafun takoma cikin gida...
"Kinsamo abun daɗi shine kokimin tayi ko?" Dr.Sadeeq yafaɗi haka ga Zahrah wacce ta ɗaura ledan sayayyar da sukayi a shoprite ita da Husnah akan cinyarta...
"Murmushi me sauti tayi haɗe da cewa "Ba'abun daɗi bane, kayan shafa ne"
"Um um ni banyarda ba, kitaimaka kiban ko chocolate ɗaya ne, naci yunwa nakeji, yau duk banci abinci ba" yaƙare maganar yana me shagwaɓe fuska, sai kace wani ƙaramin yaro...
Dariya Zahrah tayi haɗe da satar kallonsa "wai ma ya'akayi yasan cewa acikin ledar hanunta akwai chocolate?" ta tambayi kanta.
"Kina mamakin ya'akayi nasan cewa a ledarki akwai chocolate ko?, ai ba abun mamaki bane, tunda nasan shiɗin favorite ɗin ki ne" yafaɗi haka cikin yanayin shauƙi, amma still idanunsa naga titi..
Buɗe ledar tayi taciro wani chocolate mai kyau da daɗi kusan yafi kowanne ma daɗi acikin sauran chocolate ɗin da ta saya, ta miƙa masa haɗi da cewa "Ga wan nan amma bazan iya baka kyautarsa duka ba, saboda haka kaci rabi kabarmin rabi"
Saurin kallonta yayi fuskar sa ɗauke da murmushi... " Naƙi wayon, idan har kinaso na karɓa saide kibani kyautansa duka"
Turo ɗan ƙaramin bakinta tayi gaba, haɗe da noƙe kai alamar hakan bazai yiwuba, kallon bakin nata yayi, harsai da yaji tsikar jikinsa ƴa zuba, hmmm lallai idan ya auri Zahrah, zai tsotse wan nan ɗan ƙaramin bakin nata ne yanda ya kamata🙈...
"Kici chocolate ɗinki ke kaɗai nikam na gode" yafaɗi haka a taƙaice domin dama wasa yake mata baci zaiyi ba, shi da yake fama da ciwon ciki idan yaci chocolate kuma yake nan?
Lokacin da suka iso gida biyar da rabi har ta gota... kallon Zahrah Dr.Sadeeq yayi haɗe da ɗan nisawa.
"Nagama haɗa miki kayan lefe da kuma sauran abun da suka dace, wace rana kikeso a kawo?"
Saurin ɗaga idanu tayi ta kallesa jin abun da yace.
Idanunsa ɗaya ya kashe mata, wanda yasanya taji gabanta yafaɗi, saboda a wajen mutum ɗaya ta saba ganin irin wan nan kashe idon, kuma shi hakan yazame masa al'adarsa ne, bakowa bane kuma face ZAID.
"Zamuyi waya" Zahrah tafaɗi haka don son kawar da tambayar tasa, saboda a yanzu bata da amsar da zata basa..
Ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da dafa steering motar da duka hannayensa biyu. "Shikenan idan kin nutsu zan ƙiraki" yafaɗi haka cikin sanyin murya..
Murmushi tayi masa irin me tsayawa a rai ɗin nan, kana tabuɗe murfin motar tayi ficewarta, sai de batare da yasani ba, ta aje masa wan nan chocolate ɗin...
Bayan kamar 2 minute da shiganta cikin gida yaja motarsa shima yayi tafiyarsa...
*ZAID*
Tunda yasha wan nan ƙwayoyin baisan inda kansa yake ba harsai ƙarfe uku na yammaci,, ko da ya buɗe idanunsa ji yayi duniyar na juya masa, amma haka adaddafe ya shiga bathroom yayi wanka haɗe da ɗauro alwala, sai yanzu zaiyi sallan Azahar don tsabar asara, gashi har la'asar ma takawo kai....
Yana idar da sallan azahar ya miƙe daga kan sallaya haɗe da zura slipper ɗinsa yafice daga ɗakin... Kai tsaye masallacin jikin gidansu yanufa don gudanar da sallan la'asar wanda ake ƙira yanzu.. Ko a cikin masallacin mutane sai mamakin ganinsa suke saboda abune mawuyaci ka gansa a masallacin da wan nan time ɗin, yafi yawan zuwa sallan isha ko asuba, amma banda azahar da la'asar saboda a wan nan lokacin ma kwata kwata baya gida, sai de yayi sallah a wani wajen. Baidamu da kallon da mutane suke masa ba, yana idar da sallan sa yatashi yayi shigewarsa cikin gida...
Tsab yagama shirya kansa cikin ƙananan kaya, riga da wando na blue jeans wanda suka matuƙar amsar jikinsa. Ba abun da yake sai tashin ƙamshi.
Zama yayi abakin gadonsa haɗe da sanya hanunsa duka biyu ya dafe kansa dake yi masa ciwo kaɗan kaɗan,, wani irin sabon al'amari yakeji a cikin zuciyarsa, baisan da wani suna ze ƙira abun ba, amma tabbas jiyake zuciyarsa na azalzalarsa akan Zahrah, san nan yanajin cewa itace muradinsa, saurin buɗe idanunsa da ke lumshe yayi sakamakon hasko masa marukan da Zahrah ta sharara masa akan fuskarsa da sukayi, hanunsa yakai kan ƙuncinsa ya shafa haɗe da sakin murmushi, tunda yake a a rayuwarsa wata mace banda mahaifiyarsa bata taɓa kai hanunta jikinsa da sunan duka ba ballan tana har akai ga mari, sai gashi yau, Zahrah ta shararamasa lafiyayyun maruka harguda biyu akan fuskarsa, takuma haɗa masa hadda duka, amma ko kaɗan baiji zafin abun ba, anya kuwa shine? kodai an musanyashine bai sani ba? meke damun ƙwaƙwalwa da zuciyarsa ne? shine Zaid kuwa? Yajerowa kansa waƴan nan tambayoyin....
*(Team Zaid saiku basa amsa, shi ɗin ne koba shiɗin bane?)*
*27/December/2019*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Wattpad user name fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈 Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
Yajima zaune a kan gadon nasa, gaba ɗaya kansa ya kulle yarasa meke damunsa, wai shin da gaske SO yake ko kuwa? anya kuwa yanaga zaman sa haka zai yi wu? zaifi masa kyau yanemi Abid domin shi ne kaɗai zai iya fayyace masa halin da yake ciki, tabbas shi koda son Zahrah Abid ɗin yace masa yanayi yanzu bazai musa masaba, idan kuwa har haka so yake to yana mawa Zahrah so me tsanani, saurin laluɓar wayarsa ƙirar Samsung dake kusa dashi yayi. Numbern Abid ya dannawa ƙira, bugu biyu Abid ya ɗaga ƙiran cikin muryan kasala yace "Mutumin ya akayi ne, ka katseni ina cikin holewata"
"mcheeww aikin ka kenan cin ƴaƴan mutane, kana ina yanzu inaso muyi serious magana da kai" Zaid yafaɗi haka cike da zaƙuwa.
Miƙa Abid dake kwance shame shame a gado yayi haɗe da sakin daria, wai yau shi Zaid ke cewa baida wani aiki se cin ƴaƴan mutane, hmm ai duk iskancinsa shikansa yasan a ƙarƙashin Zaid yake, domin kuwa Iskancin Zaid me lasisi ne.
Cike da ƙuluwa Zaid yace " Nifa bana ƙira ka kamin iskanci bane, da zaka tsaya kanamin dariya"
"Yi haƙuri mana nawan, maganartaka ce tabani dariya, zuwa anjima mu haɗu a Millinion Park ina fata de bawata matsala bace ta afku?"
Ɗan yamutsa fuska Zaid yayi haɗe da duban agogon Rolex ɗin dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa. "Shikenan to muhaɗu ƙarfe 5 na yamma banakumason kamin african time, 5 nacika idan bakazoba, bazan tsaya ɓata time ɗina wajen jiranka ba" yayi maganar cikin yanayi da yake nuna cewa ba wasa yake ba..
"Okay" kawai Abid yace haɗe da aje wayartasa yajawo babe ɗin dake kusa dashi, suka ci gaba da watsewarsu ko kunyar Allah dayake ganinsu basayi, Allah karabamu da ƙeƙashewar zuciya Ameen.
Zaid yana aje wayartasa yasanya hanu yashafi cikinsa, sai alokacin yake tuna rabonsa da yasanya abinci acikin cikinsa tun jiya da yammaci, amma saboda tsabar yashiga tension ko yunwarma bayaji, murmushi yayi tunowa da yayi da yanda yaji muryan Abid, dagajin yanda yaji yanayin muryartasa yatabbatar masa cewa holewa da mace Abid ɗin keyi, "hmmm Abid ba dama wajen iya latsa mace" yafaɗi haka a fili, shikamma rabonsa daya kusanci wata mace harya manta, shi yanzu ko mace ma yagani bata wani burgesa, yanzu idan zaiyi sex to badakowacce mace yakeso yayi ba, face Zahrah ita kaɗai yakejin cewa zai iya sauƙewa damuwarsa yanzu, itakuma kaɗaice zata iya basa gamsuwa ɗari bisa ɗari. Miƙewa yayi yanufi wajen fridge ɗin dake ɗakin nasa, fresh milk ya ɗauka haɗe da tsiyayawa a cikin glass cup, zama yayi yasoma sipping fresh milk ɗin a hankali, gaba ɗaya hankali da tunaninsa sunaga Zahrah, ko yanzu wani hali take ciki? Allah masani...
***
Sake narke masa murya tayi cikin shagwaɓa tace "Nide bance bana sonka ba, aikaima kasan inasonka, kawai de nakasa sakewa da kai ne har yau!" taƙare maganar tana me rausayar dakanta gefe tamkar yana ganinta..
Dr.Sadeeq dake zaune cikin luntsumemiyar kujeransa na office ya lumshe idanunsa haɗe da gyara zaman wayar akan kunnensa, sosai shagwaɓan Zahrah ke sauƙar mai da kasala acikin jikinsa, yayinda idan yaji muryarta yake samun nutsuwa a cikin zuciya da ruhinsa...
"To meyasa bakya iya sakewa dani ne My Princess, kinkuwa san irin sonda nake miki? inasonki Zahrah fiye da tunaninki, amma bazaki gane hakan ba, sai idan nasameki a matsayin matata, na tabbata nan da 3 weeks kinzamo mallakina daganan kuma zaki gaskata soyayyata a gareki!" yafaɗi maganar tasa cikin yanayi na shauƙi..
Saurin kulle idanunta tayi haɗe da sanya hanu tarufe fuskarta, saikace wanda take aga banshi, sosai maganarsa yasa taji kunya,, ta lura haka Dr.Sadeeq ɗin yake watarana baruwansa kansa tsaye yake faɗar maganar da zaisanya taji kunya.
"My Princess kinyi shiru" Dr.Sadeeq yafaɗi haka a kasalance.
Numfashi Zahrah ta fesar haɗe da sake yin ƙasa da muryarta cikin shagwaɓan daya zamemata sabo tace "Munyi magana da Baffa, yace ku kawo kayan lefen duk sanda kuka shirya kawai"
Daɗi ne yakama Dr.Sadeeq harsaida yakasa ɓoye murnarsa idan kuwa hakane to tabbas acikin satin nan zai sanar da ƴan uwansa saisu shirya rananda zasu kawo kayan, shida zasuce yauma to tabbas da zaiso hakan.
"Naji daɗin maganarki My princess saboda haka kincancanci nabaki kyauta ta musamman, idan banzo da dare ba gobe zanzo insha Allah"
Murmushi kawai Zahrah tayi haɗi da cewa "Nagode amma kariƙe kyautarka bayanzuba"
"Meyasa?" yatambayeta cikin yanayi na ɓata fuska.
"Saboda hidiman da kakeyi yayi yawa, dan Allah kabari haka kaji!" taƙare maganar cikin yanayin shagwaɓa.
"Inde akan kine Zahrah bazan taɓa gajiyawa ba, zanyi wani aiki yanzu zanƙiraki anjima kinji princess ɗina!" yafaɗi haka cike da lallashi.....
Haka sukayi sallama cike da kulawa ga junansu, yanzu kam tagama aminta da Dr.Sadeeq insha Allah kuma idan ta auresa zata basa farinciki me ɗorewa, iyaka iyawarta.....
Sosai Zaid yashaƙa da irin yanda Abid yasanyasa agaba yaketa yi masa dariya,, tsuka Zaid yaja me tsayi haɗe da kawar da kansa gefe jiyake tamkar ya tashi ya rufe Abid da duka, idan banda iskanci taya zai sanyasa gaba yayi ta masa dariya bayan yagama jin matsalarsa...
Wani mugun kallo Zaid yajefawa Abid me ɗauke da tarin ma'anoni da yawa, ganin haka yasanya Abid saurin gimtse dariyarsa haɗe da kama hanun Zaid ɗin...
"Yi haƙuri Abokina, maganar ce tabani dariya"
Tsuka Zaid yakuma ja batare da yace komai ba.....
"Nafuskanci inda matsalanka ta dosa Zaid amma kuma nasan