x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 7 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 18001 words
  • 21000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 376

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
natsuwa ko fita ta kasa yi, Please dear mu yi video call in ganka, I missed you." Ta ƙare maganar tana bubbuga ƙafa tana kukan shagwaɓa

"Oh! Sweetheart za ki kashe Ni."

A rikice tace, "mene ne? Me ya faru?"

Murmushi yayi yana koma wa ya kwanta tare da lumshe idanunsa yana faman cije baki, sai dai ya kasa magana a wannan lokacin saboda yanda yake ji a jikinsa

Wanda Hanif kuwa kallonsa kawai yake yi yana mamakin ɗan uwan nasa, idan yana waya da Haseena ya kan manta kansa da wanda ke wurin ne, sosai yake jinjina tsantsan soyayyar da SHAREEF yake yi wa Haseena, wanda har ba ya iya control ɗin kansa da tsananin soyayyar nata. Numfashi kawai ya ja yana kawar da kansa domin a lokacin ma ya dena jin mai suke cewa saboda tunanin da ya faɗa. Har sai da ya gansa ya gama wayan yana ƙoƙarin shige wa toilet. Bai ce mishi komai ba sai da ya shiga ya fito sannan ya bi shi da kallo yana murmusawa

Harara ya samu daga wurin SHAREEF ɗin yana cewa, "lafiya Malam?"

"Babu komai."

Sai ya ja tsaki yana cewa, "ka ji da gulman ka, ban san saka ido wlh."

Murmushi Hanif yayi yace, "babu wani saka ido, but Ni dai shawaran da zan baka a rage wannan soyayyar tunda aure ba yanzu ba, ta yiwu ma in riga ka auren tunda na ga Sarauniyar ta gudu ta bar ka, nan kusa zaka ji nayi yi wa su Dady maganar aure."

Baki ya taɓe bayan ya zauna a saman gadon, sai ya ɗauki wayansa yana hawa WhatsApp, tare da furta, "ina ruwana to? Ka haifi Yara da yawa ma bai shafe Ni ba."

Dariya sosai Hanif yake yi. Yana cewa, "Ni dai ba ruwana, kar ka ga nayi kace zaka ɗaga hankalin ka, ina tunanin ma su Dady baza su amince in yi aure in bar ka ba, gwara ka samu solution wlh."


Shiru SHAREEF yayi masa bai ce komai ba. Ya ci gaba da latsa wayan kamar ruwa ya cinye sa

Hakan ne yasa Hanif ya canza topic ɗin. Duk da ba kasafai SHAREEF ɗin yake amsa mishi ba, jefi-jefi suke hira

Daga baya ne su Sadiq suka zo shi da Abokan sa. Shi yasa Hanif ya bar asibitin ma gaba ɗaya.




              Zuwa washe gari aka sallami SHAREEF tunda komai normal. Jikin nasa ya warware shi yasa the following day ya koma bakin aikin sa. Yayinda gefe ɗaya soyayya da shaƙuwa take ƙara gudana tsakanin SHAREEF da Haseena, tamkar zasu cinye junan su

Su Dady ko kaɗan basu yi wa SHAREEF maganar aure ba, duk da suna son su yi mishi domin ya fito da Mata kasancewar abun da Likitan yace

Ga shi yanzu kusan sati ɗaya da kwanciyar sa a asibiti. Lokacin ne kuma Hanif zai koma karatun sa. Shiyasa SHAREEF yace, "zai bi shi har can ya raka sa." Sabida so yake yi daga can ya wuce wurin Haseena

Babu wanda ya hana sa kasancewar an san shaƙuwar su da Hanif. Tamkar Abokan juna suka ɗauki kansu, babu mai kallon su yace Yaya da Kani ne saboda yanda suke gudanar da al'amuran su gunun sha'awa.
[13/01, 12:00 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

      *SHAREEF*
          _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*





*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days











__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE8*
               Tunda aka yi wa Maryamu dukan nan, zazzaɓi ya kwantar da ita tunda bata taɓa shan duka irin wannan ba, musamman ma Baba duk rashin jinta bai taɓa dukan ta ba, iyakan yayi musu faɗa ko ya tsawatar musu, dama Yaya Ashiru ne mai ɗan dukan nasu shima ba sosai ba, domin tunda suka ɗan soma tasawa Baba ya hana ana taɓa su. To kasancewar ta ba mai son a taɓa lafiyar jikinta ba, abu kaɗan sai ka ga ciwo ya rafkar da ita, amma sai rashin jin tsiya, domin Maryamu ba ta jin magana, ita kaɗai ta fita Zakka a gidan su, akwai ta da rashin tsoro ne; uwa uba rashin kunya da fitsara, bare tana tashen balaga jinta take yi kanta ɗaya da kowanne shege

Duk wani abu tare suke yi da Bintu duk da ita bata kaita rashin ji ba, sabida ita akwai shegen tsoro, ba kasafai take biye mata ba, sai dai idan Maryamun ta tilasta ta su yi wani abun, to a nan ne bata da yanda zata yi zata biye mata tunda komai tare suke yi, basu da ƙawaye su kaɗai ne ƙawayen juna. Tunda babu mai iyawa da halin Maryamu, kullum sai an ji ta da sa'annin su suna cacan baki ko dambe, bare yanzu duk sun yi aure sai ɗaiɗaiku


Shi yasa Baba tunda abun nan ya faru ya ƙara matsa musu sai sun fito da Miji

Amma Maryamu fir tace mishi, "ba ta son aure baza ta yi ba." Sai kuka take yi tana rigimar nata tamkar wata ƙaramar yarinya, don wani abun ma ko ƙaramin Yaro bazai yi abin da take yi ba, ko don tana ganin ita ce Auta a wurin Innar ta oho? Shiyasa a kwanakin ba ta iya fita ko ina saboda yanda jikinta ya rikice. Ta saka rigima a ranta a kan auren da Baba yace zai yi musu

Domin a lokacin har manemin Bintu ya turo tunda dama tana da tsayayye. Ɗan uwansu ne ma kuma a ƙauyen yake

Yanzu haka har an tsayar da lokaci idan Maryamu ta kawo wanda take so sai a saka rana

An yi haka da kusan sati biyu, amma Maryamu ta ƙi bin umarnin Baban ta, sai ma ci gaba da rayuwarta da take yi ba ta kula kowa in yazo, Sai cin mutunci da zage-zage da take musu, shiyasa kowa ya ɗauke ƙafa da zuwa wurin ta

Shi yasa Baba ya dinga mata faɗa yace, "tunda ta ƙi kawo wanda take so shi yana da inda zai bada ita." Nan ya yi wa Abokinsa magana saboda yana da Yaro Sule wanda yake sonta dama, kuma Baba ya san da haka saboda ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba; ya sha ganin sa yana zuwa ƙofar gidan wurin Maryamu. Dalilin da yasa yace, "kawai su turo sai a haɗa auren gaba ɗaya." Tunda ya yarda da tarbiyyar sa

Dama yanzu bikin su Yaya Ashiru ya rage saura wata uku ne. Suna gama jarabawar ƙarshe na B8 da suke yi, za a yi auren

Wannan maganar ba ƙaramar rikita Maryamu yayi ba. Kuka sosai ta dinga yi tana cewa, "wlh tallahi babu wanda ya isa yayi mata auren dole, ba ta son Sule baza ta taɓa auren sa ba, sai dai duk abun da za a yi a yi." A gaban Baba take furta waɗannan kalaman nata tana ta birgima da ihu, "wlh ba a isa ba baza ta aure shi ba."

Baba samun sanda yayi, yayi mata dukan tsiya yace, "shikenan zai gani idan ita ta haife shi."

Amma duk dukan nan da ta sha Maryamu ta ƙi haƙura baza ta yi auren ba. Tun abun yana ba wa su Umma haushi, har ta soma basu tausayi saboda yanda ta fige a lokaci ɗaya, bata da aiki sai kuka da nacin, "ita baza tayi aure ba, ba ta son wanda aka kawo mata."

Ranan ma da ya soma zuwa taɗi wurin ta. Dutse ta samu ta ƙwandala masa a kai tana cewa, "wlh in dai bai fasa auren ta ba sai ta fasa masa kwanya ya mutu a banza a hofi, idan kuma ya isa ya aure ta ya gani."


Haka fa Maryamu ta dawo tamkar mahaukaciya. Domin gaba ɗaya ƙauyen sai da suka taru a kanta ana ganin ikon Allah. Sun ga abun tamkar wasa sai kuma abu ya zo ya zama babba. Saboda yanda Maryamun take yi ashe wai aljanun ta ne suka tashi

Har ga Allah ƴan gidan basu taɓa tunanin tana da aljanu ba sai ranan. Kowa ya sha mamaki, amma kuma idan aka ga yanda take yi tun farko dole a saka ayar tambaya a kanta

Yaya Faisal aka kira yayi mata ruƙiya tunda yana da sani sosai a kan addini. Har koyarwa yana yi a Islamiyyar su duk da ba kullum ba, sai sati da Lahadi kasancewar aiki da yake yi a Birni, so ba ya zama sosai, lokacin an ci Sa'a yana gida shi ya zo yayi mata ruƙiya. Daƙyar aka samu ta dawo hayyacin ta

Gaba ɗaya gidan sun yi cirko-cirko har da su Aunty Indo da Aunty Ummita duk suna gidan, saboda tunda labarin abun ya faru kowa ta bazamo gida. Gaskiya hankalin su ya tashi sosai sabida basu taɓa zaton Maryamu tana da wannan laluran ba

Ga shi jikinta ya ƙi daɗi, tunda suka tashi take kwance magashiyan tana faman rawan jiki, sai zazzaɓi ya rufe ta. Dole Inna ta saka mata drip aka bata magunguna don dai aga yanda hali zai yi

Ba a samu kanta ba sai washe gari, sai dai ta tashi tana ta fushe-fushe, kowa ta ƙi kula wa a gidan, kana mata magana ma zata hau gaya maka maganganu tana zumɓure-zumɓuren baki kamar wanda zai taɓo sama

Shi yasa kowa ya shafa wa kansa lafiya tunda basu san yanda Aljanun nata suke ba, kowa ya fita harkan ta

Ƙarshe ɗaki ta shige ta kwanta ta ƙi kula kowa

Dayake suna da islamiyya. Sai Bintu ta zo tana ce mata, "ta tashi ta shirya su tafi ƙarfe huɗu saura."

Banza tayi mata ta juya kai tana kallon sillif idanunta a buɗe. Manyan idanun nan yanda ka san gauta gaba ɗaya sun rikice sun yi jazur

Bintu bata sake kula ta ba, tana gama abun da zata yi ta shirya ta fito

Umma Jummai tace mata, "ya haka kin fito ke kaɗai? Ita Maryamun baza ta je bane?"

"Ni nayi mata magana ta ƙi kula Ni shiyasa na ƙyale ta."

"To shikenan je ki, sai ki gaya wa Malamin naku bata da lafiya ne."

"To." Ta furta tana yin musu sallama sannan ta tafi

Maryamu da ake maganar a kunnen ta duk tana jin komai, miƙe wa tayi fuska a turɓune ta ɗauki Hijabin ta ta saka, cikin kayanta ta duba ta ɗauko dubu ɗaya a ciki wanda dama shikenan ya rage mata a cikin jakar. Wata shegiyar takalmi mai tsini ta ɗauka ta zura a ƙafafuwan nata sannan ta fita. Ko kallon su Inna bata yi ba tabi hanyar waje zata fice

"Ke kuma haka za ki tafi babu sallah?"

Banza ta yi wa Innar da take mata magana ta yi ficewar ta. Ta sha alwashin baza ta taɓa zama a yi mata auren dole ba, gwara ta gudu kawai ta huta da ace ta zauna a yi mata aure. Kai tsaye hanyar barin garin tayi tana ta tafiya ita kaɗai sai faman turguɗe wa take yi, a zuciyarta kuwa lissafin inda yakamata ta nufa take yi; da tunanin matakin da ta ɗauka shi ne dai-dai a wurin ta.





🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆


         Har England SHAREEF ya raka Hanif, a lokacin da suka sauka dare yayi shiyasa ya kwana a can. Da sassafe ya soma shiri zai wuce wajen Haseena

Hanif sai tsokanar sa yake yi yana cewa, "shi gani yake yi kamar ya fi sonta a kansa, sabida ya fi bata kula wa duk yanda suke da shi, amma ace daga zuwan shi sauri-sauri yake ya tafi ya bar shi, maimakon ya ƙara ko kwana biyu ne su ɗan zagaya garin, sai ya je ya ga friends ɗin sa zasu yi farin ciki."

But SHAREEF ko kula sa bai yi ba, sai da ya gama shirya wa sannan ya jefe shi da harara yace, "common tashi ka kai Ni airport, ba na son wannan surutun."

Dole Hanif ya miƙe yana ɗaukar key, tare suka fita zuwa haraban gidan

Ganin yanda Motan tayi ƙura sosai, sai SHAREEF ɗin ya yamutsa fuska yana cewa, "kai bazan hau wannan motan ba, mu je in hau Texsi."

"Ok to." Shima Hanif ya amsa mishi suna yin waje suka fita

Har airport ya raka sa, sai da ya ga ya hau jirgin Australia sannan ya dawo.
**********


              Fannin Haseena, tunda ta san yana zuwa, ta sanya mai aikinta tayi mishi girki kala-kala, ita kuma ta ɗauki wankan ƙananan kaya, ta tsuke a cikin wandon jeans, sai shaining take yi fuskar nan ta sha kwalliya tayi ɗau, dama abun da SHAREEF ya fi ƙauna a gare ta kenan, ya ga tayi irin wannan kwalliyan, sau tari yana yawan gaya mata, "tana tafiya da imanin sa muddin ya ga fuskarta haka." Shi yasa yawanci take yawan yi idan zasu haɗu since bata cika ƙaunar kwalliya ba

Tana zaune ta ji ƙaran buɗe ƙofa, tunda gida guda Abban ta ya kama mata haya, since da ta ji buɗe ƙofan ta san bazai wuce SHAREEF bane, da sauri ta miƙe ta fita wajen, ai kuwa shi tayi tozali da shi

Shima tunda ya hango ta ya tsaya a wurin yana zuba mata murmushin sa mai kyau da ƙara masa kwarjini

Da gudu ta nufo sa cikin tsantsan farin ciki ta rungume shi

Sai ya sa hannu ya manne ta sosai a jikinsa yana raɗa mata magana a kunne, "i miss You sweetheart!"

Ɗagowa tayi tana kallonsa tana murmushin itama, sai tayi masa kiss a laɓɓa tare da furta, "more than you dear."

Kumatun ta ya ja tare da cewa, "Ok let's get into it, I need a break I'm so tired." Yayi maganar yana ɗan yatsina fuska, alamun da gasken ya gaji da yawa

Shige masa jiki tayi sosai, tare da zagayo da hannunta a ƙugunsa, a haka suka shige ciki suka yi wa kansu masauki a saman kujera, kana ta tashi ta ɗauko mishi drinks tana cewa, "Are you going to take a shower first? You will feel better about your body."

"No. I don't need a bath, I will drink." Sai ya sa hannu ya zuba drinks ɗin a cup, tare da kaiwa bakin sa yana sha kaɗan

Murmusawa tayi tace, "ka san me Dear?"

"No. Sai kin faɗa sweetheart." Ya furta yana ajiye cup ɗin tare da kanne mata ido daya

Sai ta shige jikinsa tana cewa, "Today I am happy because you came, we will go out together. Nayi tunanin baza ka zo ba."

"Me zai hana sweetheart? ai duk abun da kike so nima shi nake so, I'd rather see the happiness on your face."

Dariya tayi tace, "I know you love me a lot dear, I also love you very much, let's go eat and I will prepare interesting things for you; domin in burge ka." Sai ta miƙe tana janyo hannunsa ta ɗaga sa

Direct kan dinning suka nufa, ta ja mishi kujera ya zauna sannan ta zauna a side din sa. A one plate tayi musu save, ita ta soma ba shi abincin a baki tana cewa, "haaa bakin."


Dariya yayi yace, "kina son ki mayar da Ni Yaro ko?"

Fari tayi masa da ido tace, "ai ka fi Yaro a wuri na, ganin ka nake yi tamkar Jariri, dole sai da tarairaya kar Matan banza su ƙwace min kai, ka san yanda nake ji da kai." Sai ta ja numfashi tana ƙara wa da faɗin, "ina jin soyayyarka kamar zan yi hauka SHAREEF, ba na fatan ace wani abu ya zo ya raba mu, duk sanda ka bar Ni mutuwa zan yi, don Allah kar ka taɓa rabuwa da Ni, ina matuƙar ƙaunar ka!" Ta ƙare maganar tana shirin zubar da hawaye

Ɓata fuska yayi yace, "kuma za ki fara ko?" Sai ya amshi cokalin tare da ɗibo kaɗan ya kai bakin ta, "ki dena faɗin haka sweetheart, babu wanda ya isa ya raba mu da juna, domin ke ce wacce har zuciya nake ƙauna, ke kaɗai nake so, don haka ki dena wannan maganar; I don't want to see you in trouble. Oya buɗe bakin ki ci sosai mu je mu zagaya gari."

Cike da soyayya yake ci da ita, don shi ya ƙi ci tun wanda ta ba shi, koda tayi masa complain sai ya nuna mata, "ba ya jin yunwa ne." Shi yasa ta ƙyale sa

After ya gama suka fita a tare zuwa yawon buɗe ido, a duk inda suka je suna manne da juna suna shan soyayyar su tamkar zasu haɗiye juna. Sosai SHAREEF ɗin ya saki jikinsa suka sha soyayya, domin ya kasa control ɗin kansa musamman da suka dawo gida, biye mata yayi suka sha romance tunda abun da take so kenan, kusantan ta ne kawai bai yi ba a wannan lokacin, amma sai da suka gama yamutsa juna suka yi wanka a tare sannan suka kwanta, tana jikinsa ta lafe sai matsa ta yake yi kowannen su babu kaya

Har ga Allah ya ji dad'i matuƙa a yau domin duk wata sha'awar sa sai da ya watsar da ita, sosai ta gamsar da shi da wasan da suka sha, tunda ya bata haɗin kai shiyasa har ya fitar da abun da ke jikinsa. Don ma ya ƙi biye mata ya kusance ta amma sun kasance cikin farin ciki a wannan lokacin tamkar zasu haɗiye juna

Saboda haka ne ma, SHAREEF ya kasa dawowa cuz kulawar da Haseena take ba shi ya kasa koma wa. Koyaushe suna manne da juna babu wanda zai kalle su yace ba Mata da Miji bane

Kwanan sa biyu ba shi da alamar dawowa. Sai da Dady ya kira sa yana masa fadan, "kuma sai ya je ya zauna a can haka ake yi?" Tunda a tunanin sa yana wurin Hanif ne, basu san cewa yana wurin Haseena ta riƙe sa ba

Sai da yayi ta lallaɓa ta ma; sannan ta yarda zai tafi, bayan yayi mata alƙawarin, "zai dawo Very soon."

Har airport ta raka sa, sannan suka yi sallama daga can ya dawo Nigeria cike da kewarta da ƙaunarta a rai, tare da burin a ce ya mallake ta a matsayin Mata a nan kusa ko don ya samu abun da yake so, domin a yanzu ba shi da wata buƙata sama da ta zama Matarsa, kasancewar sa mai buƙatar aure a yanzu, amma soyayyarta yasa ya biye mata batare da ya nuna damuwarsa a kan
End Ads