x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 42 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 123001 words
  • 126000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 414

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
sai da ta taho wa Maryamun da breakfast ɗin ta tunda bata ci komai ba

Suna zaune suna jiran ta farka,
Tsawon awanni huɗu tana barcin before ta farka,
Kuma jikin nata da sauƙi ba kamar yanda aka kawo ta ba, garau ta miƙe sai kanta da ke mata ciwon ne kaɗan-kaɗan,
Sun ji daɗin ganin ta a haka sai murmushi suke yi


Likita ya sake duba ta ya tabbatar musu da babu wata matsala, sannan yace, "a bata wani abu ta ci sai ta sha maganin, inyaso sai su wuce gida kawai."
Ganin yanayin jikin nata babu ƙarfi; ya san in aka bata abinci zata samu ƙwarin jikinta sosai, yace, "a hankali shima kan zai dena."
Sai ya fita ya basu wuri

Sai sannu suke mata kamar zasu mayar da ciwon jikinsu sabida yanda suka damu da ita, tamkar ƴar da suka haifa haka suke jin ta a ransu, suna matuƙar tausaya mata,
Momy ta haɗa mata tea a cup, ta soma bata da kanta tana yi mata sannu,
After ta gama sha sai ta ciro maganin; ta bata ta afa a baki, sannan ta ƙarisa da sauran tea,
Cus ta san halin ta a yanzu, ba ta cika son shan magani bane, sai dai a bata da wani abun ban da tsuran ruwa, ta dinga kwarara amai kenan, shiyasa tunda ta laƙanci halin ta sai take dama mata koko ko kunu; ko kuma tea sai ta sha dashi

Bayan sun ga ta samu natsuwa, sai Momyn take tambayar Dady me Likitan yace ke damunta?

Dady bai ɓoye mata komai ba ya sanar mata, da irin ɓacin ran da yake ji a cikin ransa

Ita kanta Momy baƙin cikin hakan take ji, shiyasa ta furta, "wlh Alhaji ina ji a raina idan har wani abu ya samu yarinyar nan; SHAREEF ne sila, komai da ke faruwa da ita shi ne silan komai, kuma duk sabida shi ta shiga wannan halin, kuma ke Maryam sai da na fada miki ki kwantar da hankalin ki in dai SHAREEF ne kin same shi kin gama, mun rigada mun miki alkawarin tarewan ki nan kusa a cikin wannan satin ma ba sai an je da nisa ba, to me yasa baza ki cire damuwa a cikin ranki ba? Kin fi son ki kassara kanki a kan wanda bai damu da ke ba? Kina nan kina haukan sonsa?"

Maryamu da idanunta ke rufe tana sauraron su, dayake ta jingina bayanta da matashin da aka saka mata a bayanta sabida ta ji dadin zama, Momy ta hana ta kwanciya kasancewar yanzu ta gama cin abinci,
Sai da suka gama maganar ta buɗe idanuwanta da suka yi mata nauyi sabida halin ciwo, daƙyar take iya furta maganar nata sabida muryanta ta rigada ta shaƙe ba ta fita sosai, a hankali tace, "Momy Ni yanzu na canza shawara ma, na fi son in yi karatuna tunda na samu dama, ba na son ci gaba da zama a nan ki kaini inda kika ce za ki kaini, ko kuma a mayar dani gida in je in yi karatu na a can, hakan zai fi min kwanciyar hankali."

Shiru suka yi dukkan su, duk da sun ji mamakin maganar nata amma tausayin ta ne ke tasiri a ransu

Ita kuma hawaye ne suke ƙoƙarin fito mata ta sanya hannu tana share wa, yayinda ta hana bayyanan su kan kuncin ta

Dady ya kamo hannunta yace, "Maryam ke ƴata ce halak malak, duk abun da kika nuna kina so ko aina yake in dai bai fi karfina ba zan miki, don haka maganar zancen soyayyar ki da SHAREEF da kuma tarewan ki a gidan sa tana nan daram a yanzu, wannan satin mai zuwa za ki tare a ɗakin shi, ba ki da wata damuwa ki cire komai a ranki kinji ko?"

Girgiza kanta tayi wanda idanunta sun kaɗa sun yi ja kuma ta ƙi yarda ta zubar da hawaye, sai dai ƙwalla da suka taru mata, cikin rauni tace, "Dady Ni dai ba na son in tare yanzu, na haƙura karatu nake so, dama shi ya kawo Ni garin nan shi nake son yi, don Allah Dady ku cika min burina ina son in yi karatu mai zurfi."

"Kin tabbatar hakan kike so? Baza ki saka wani damuwa a ranki ba? Babu wata matsala ko?"

Kanta ta ɗaga mishi alamun eh

Hakan ya yi wa Momy dad'i don wlh kwata-kwata ba ta son Maryamu ta tare tun wannan lokacin bata san ciwon kanta ba, akwai ƙuruciya a kan Maryamu, zata sha wahala a hannun SHAREEF, yanda ba ya sonta ɗin nan kuma ya tsane ta, komai zai iya mata; baza ta taɓa jin daɗin zama dashi ba, itama kuma ba ta son hakan, ta fi so ta zauna da soyayyar SHAREEF, yana sonta tana sonshi wannan shi ne burin ta, tana jin yarinyar kamar ita ta haife ta, musamman yanda take kamanceceniya da ɗanta Sadiq kamar tagwaye, ita kanta suna kama sabida idanunsu da suke kusan iri ɗaya, sai ka ɗauka sun haɗa jiɓi da Momy fiye da Dady ma, sai dai kawai baƙin fatar da take dashi ne amma suna kama sosai, shiyasa soyayyarta take ƙara shiga zuciyarta tana jinta a ranta kamar ƴar cikin ta.
***

          
_____A lokacin Doctor ya zo ya sallame su suka wuce gida, time ɗin jikin Maryamu yayi sauƙi sosai, ita kanta tayi ƙarfin hali wurin ɓoye damuwarta, ta saki jikinta kamar wacce bata yi ciwo ba

Hanif ya ji daɗin ganin ta sai tsokanarta yake yi, yana cewa, "kamar wacce ba ita bace ɗazu ta kusa mace musu, tafiya ma ta kasa sai shi ya ɗauke ta, amma yanzu ta dawo garau da ƙafafuwanta kamar ta fi shi lafiya ma yanzu."

Sai dariya take yi kuwa, ta saki jikinta sosai domin tana jin dad'in yanda Hanif yake wasa da ita, har sanyi take ji a ranta sabida ganin kaman su ɗaya da SHAREEF, tana jin kamar shi ne a gabanta suke magana tare, hakan na saka ta farin ciki

Su kansu sun ji daɗin yanda ta saki jiki tana dariya da raha, kamar ba ita ba, hakan yayi musu dad'i

Koda Sadiq ma ya dawo ya ganta a haka ya ji dad'i sosai, sai murna yake yi domin hankalin sa a tashe yake, ya kasa zama yayi karatun sosai sai da ya kira ya ji ko lafiyarta, ana ce masa an sallamo ta sai ya dawo gida bai tsaya ya ƙarisa lectures din nasa ba

Haka suka taru suna ta sanya ta dariya da barkwancin su, suna zaune sun yi shame-shame a Falon sai hira suke yi har su Dady, shi ne ma gwanin tsokanar yana ta basu labarai lokacin da yake gwagwarmaya a baya yana saurayi,
Har yamma suna wurin Sallah kawai ke ɗaga su, sai kuma abinci da a wurin suka ci suka baje a falon, yau basu zauna a dinning ba

Kamar yanda SHAREEF ya saba dawowa karfe biyar sai ga shi ya shigo gidan

Ganin sa yasa Maryamu ta lallaɓa ta shige ɗaki bata ko kalli inda yake ba, domin ba ta son ta ci gaba da kallonsa tana jin tsananin soyayyarsa a ranta, yanzu dole zata saba wa kanta rabuwa dashi, ada ji take yi zata mutu muddin wata rana aka ce za a raba su, amma yanzu tana jin zata iya jure wa gwara tayi nesa dashi, wataƙil abun da Momy ta sanar mata zai kasance Gaskiya, duk sanda aka ce ta sauya ta zama babbar Mace kuma ya dena ganin ta, ƙila zai ji soyayyarta a ransa,
Amma tana jin ƙunci da baƙin cikin kasancewar wata a ransa ba ita ba, wanda hakan yasa sai da ta kasa jurewa ta dinga kuka a cikin daki, kishi da baƙin ciki ya turniƙe mata zuciya, har yanzu tana jin wannan abun da ya tsaya mata a maƙogwaro ya ƙi tafiyar mata, wurin ya bushe koda ta jiƙa da yawu ba ta jin dai-dai, ta rasa yanda zata yi, tana tunawa dashi sai ta ji hawaye da wani irin zafi a zuciyarta, ga wani nauyi da yake mata kamar tana jin ciwo a wurin

Su kuma su Momy ko kusa basu yi wa SHAREEF maganar Maryamu ba, in fact ma basu nuna mishi komai ba kan face ɗin su ba, asali ma ita kanta Momy yau ya ga sakin fuskarta, shiyasa ya ji dad'i a ransa har ya saki jiki fiye da koyaushe,
Ita kuwa Maryamu bata a cikin ransa, ya san cewa warning ɗin da yayi mata ya shiga kunnen ta baza tayi gigin kuskure abun da ya furta mata ba.
***

   
_____Momy ta so a gobe Hanif ya kai Maryamu Abuja ne,
amma Dady yace, "a'a, a bari zuwa Monday time ɗin jikinta yayi sauƙi sosai."

Momy duk ta kira Surayya ta sanar mata da halin da ake ciki, da kuma irin taimakon da zata yi mata na gyara mata Maryamun; ta zama wayayyiyar yarinya fiye da tunanin mutane, duk abun da ta san zai amfane ta ta koya mata; ita kuma ko nawa ne zata kashe mata

Surayya na dariya tace, "ba ki da matsala Aunty, ko Ni zan bada tawa gudummawar ba dole sai kin biya wani abu ba, ai nima ƴata ce musamman ma da ɗanmu take aure, zan kula da ita fiye da tunanin ki, kuma Insha Allahu sai SHAREEF ya raina kansa wlh."

Momy sai jin dad'i take yi, haka suka ci gaba da wayan, sun jima before suka kammala.



           Ranan Monday aka shirya tafiyar nata, Hanif zai kaita tunda yana son zuwa ya gaishe da Ammeen nasu,
shima sai Sadiq yace, "zai je."
Shi yasa suka shirya gaba ɗaya zasu tafi

Har Dady sai da ya yi wa SHAREEF magana, "ko zai je?"

But yace, "a'a." Sabida ganin har da Maryamu a tafiyan shiyasa ya nuna sam bazai je ba, domin ba ya fata a ce doguwar tafiya ta haɗa shi da wannan bak'ar yarinyar da yake jin tsanarta a ransa, gwara su tafi su kaɗai

Maryamu sai kuka take yi kamar me, duk da kukan nata da biyu ne, na rashin SHAREEF da kuma kewar su Momy, haka suka yi ta rarrashinta kamar zasu goya ta,
Don ma wai tare da su Sadiq zata je shiyasa ta ɗan ji dama -dama

SHAREEF na gefe yana kallon abun mamaki, ji yake yi kamar ya tashi ya nakaɗa mata dukan tsiya, sai kallonta yake yi ransa na ƙara ɓaci saboda jin sautin kukan ta da ya cika masa kunne,
Tsaki ya ja ya miƙe yabar wurin ya koma ɗakin su, ta corridorn sama ya tsaya yana kallon haraban gidan; hannunsa riƙe da goran ruwa da ya ɓalle yana sha sabida jin maƙoshin sa ya bushe,
Yana tsaye a wurin ya hange su sun fito har da su Momy sun raka su bakin Mota,
Yana mamakin yanda suke lalace wa a kan wannan yarinyar, musamman yanda ya ga ta lafe a jikin Momy kamar zata mayar da ita ciki, har lokacin sai kuka take yi,
Daƙyar suka lallaɓa ta ta shiga motan,
Takaici yasa ya kawar da kansa yana kallon wani wurin zuciyarsa na masa zafi da tunanin wani abu a ransa,
To yanzu shi ya zai yi ma da auren ta bayan basu ce masa komai ba?
Ko banza zai ji sanyi a ransa kuma yana ji a jikinsa hakan na nufin sun haƙura da maganar kenan, wannan abun farin ciki ne, jira kawai yake yi suyi masa maganar takardan sakin ta,
Sai kawai ga murmushi a kan kyakkyawar fuskarsa wanda har dimples ɗin sa suna lotsa wa sosai, suka fito da ainihin tsantsan kyawun sa,
Dai-dai sanda ya ƙara kallon Motan still da murmushin kwance a kan face ɗin sa

Karaf suka haɗa ido da ita tana cikin mota itama ta ɗago jajayen idanunta da suka gama rinewa da kuka, bata yi tsammanin ganin sa a wurin ba amma sai ta gansa

Kallon-kallo suka yi wa junan su, inda tuni SHAREEF ya ɗauke murmushin da ke face ɗin sa, kowannen su da irin kallon da suke yi wa juna wanda ya sha bamban

Har Motan ta soma tafiya but Maryamu bata ɗauke ido a wurin ba, domin wani irin sanyi da farin ciki ne ya kawo mata mamaya lokaci guda musamman yanda ta ga kyakykyawar fuskar nan nasa mai cike da haiba da kamala tana fitar da sassanyar murmushi, lokaci guda ta ji wannan abun da ya tsaya mata a wuya ya wuce zuruf, yayinda kaso mafi yawan damuwarta kamar an yaye mata,
Bata damu da irin kallon da yake mata ba, amma har a ranta ta ji dad'i, sai kawai ta sakar masa murmushin da bata san lokacin da ya suɓuce mata ba

Hakan ne yasa SHAREEF yayi saurin ɗauke kansa a ransa yana tunanin wa take yi wa murmushi? Lallai wannan yarinyan bata da hankali, ko giyan wake ya sha zai iya soyayya da ita ne bare har ya ji sonta a ransa? Never, bata kai matsayin ba wlh, ya rasa ma wacce zai so sai ƴar tayin yarinyar nan, ko Haseena da ta girme mata yana ganin tayi masa ƙanƙanta bare wannan ƙaramar yarinyar wacce bata wuce ƴar cikin sa ba, amma ita Haseena ai daban take da wannan, tunda tana da abubuwan kallo fiye da wannan, kuma ta cika Macen da kowanne namiji zai so ta, tana da kwalitin da yake bukata ya samu a kan Mace, ta iya kwalliya, wayayyiya ce ajin farko, wacce ta fito daga gidan Hutu da jin dad'i, babu ƙauyanci a tare da ita, tana da class ta ko'ina zai ina nuna ta a Matsayin girlfriend ɗin sa,
Amma wannan kuma fa? Sai ya ja numfashi yana sakin guntun tsaki tare da jefa hannunsa ɗaya mara riƙe da goran ruwan; a cikin aljihun sa,
In ban da baƙar fata da dogon hanci, sai gwala-gwalan idanunta masu kama dana mujiya, bai san kuma abun da ta ajiye ba, a fili ya furta, "shegiya da wasu idanunta kamar zata yi zawo, in banda Jaka ce ita taya ya zata haɗa kai dani? Ta rasa wacce zata so sai Ni? Lallai ma yarinyar nan ta raina min wayon".
Sai ya juya yabar wurin yana jan guntun tsaki yana sake jin ransa na ƙara ɓaci.
[04/03, 9:00 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

      *SHAREEF*
          _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*





*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days.












__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE48*
 _____Kusan la'asar su Maryamu suka isa Abuja,
A cikin barikin sojoji gidan da ƙanwar Momy take zaune yake, tunda Mijinta Soja ne kuma babba, gidan su yana farko-farkon layi, gida mai number 4,
Babban gida ne kwatas mai cike da flowers da aka ƙawata gidan

Yanayin anguwar da gidan ba ƙaramin burge Maryamu yayi ba, sai baza idanu take yi har suka shiga gidan

Suna tsayar da Motan; Ammee da Yaranta suka fito tarbar su, yanda ka san Momy haka Maryamu ta ga kamannin su da Matar, suna tsananin kama sai dai Momy ta fi su haske, gaba ɗayan su ma ƴan dakin su in ka kalle su sai ka gane jini ɗaya suke, sai dai Ammee ta fi yanayi da Momy har jikin su da ɗan sirantan su, ga yanda kuma ta tarbe ta shiyasa lokaci guda ta ji Ammeen ta kwanta mata a rai,
Ga Yaranta su Yusaira da Aakifah yanda ka san ƴan biyu kansu ɗaya kamannin su ma ɗaya, sai ƴar Autar su Na'ilah wacce ita bata yi kama dasu ba ko kusa, ita yanda kasan Mahaifinsu yayi kaki ya tofar haka suke kama

Da gudu suka zo suka rungume su Hanif suna murnan farin cikin ganin su

While Ammee ita kuma Maryamu ta tarba bakin ta har kunne sabida ganin yanda Maryamun take, faraɗ ɗaya ta shiga ranta musamman yadda ta ganta ƴar kyakkyawa,
Tana riƙe da hannun Maryamun ne take kallon su Hanif tare da cewa, "Yarana yau an tuna dani ko? Sai yau da dalili ya kawo ku shiyasa zan ga ƙafafun ku?"

Dariya suka yi gaba dayansu

"Ok mu shiga ciki, ku kuma ku sake su kun wani maƙale musu daga zuwa."
Cewar Ammeen tana kallon su Aakifah wadanda sai faman murna suke yi

Cikin gidan tace musu, "su shiga."

Sai suka wuce a tare, while Sadiq ya ɗauki Na'ilah a kafaɗa suna dariya su biyun, musamman ita da sai farin ciki take yi sabida an ɗaga ta sama

Cikin Falon suka shiga a tare suka zazzauna a saman kujera, kana Ammee ta nufi wurin fridge tana kiran sunan Yusaira,
Ruwa ta fito da su tare da juice na kwali ta bata, tace, "takai ta ajiye musu."
Bayan ta gama kwaso wa sai ta ɗauko raguwar ta taho dashi, ajiye wa tayi a saman Centre table inda Yusaira ta jera sauran, ta sake ce mata, "ta je ta ɗauko cups ta kawo musu."
Sannan ta zauna tana kallon su da faɗin, "ina SHAREEF ya ƙi biyo ku ko?"

Hanif yace, "wlh kuwa, yace bazai zo ba."

"Hmm shi ya sani, na san dalili ai; cus Aunty ta sanar min komai before ku ƙariso."
Sai ta kalli Aakifah tace, "Aakifah je ki taho da samosan nan da na ajiye a tray ki kawo musu."

Aakifah amsa mata tayi tana miƙe wa tare da nufan kitchen ɗin

While Ammee ta mayar da hankali kan Maryamu da tayi shiru tana zazaare ido a falon, sai kallon hotunan Falon take yi, "Maryam Allah yasa dai baza ki yi min baƙunta ba? Tunda ga Yara nan sa'annin ki ki saki jikinki sosai kamar kina gaban Aunty Khadijah ne, don kulawar da zan ba ki sai ya fi nata ma."
Tayi maganar tana ƴar dariya

Su ma su Hanif dariyan suka yi, while Maryamu murmushi tayi kawai

Sadiq yace, "nima abun da nace mata kenan Ammee tun a Mota, kin san Momy ita ta cika faɗa wlh shiyasa nima nake son dawowa nan, musamman ma in Uncle yana nan na fi jin daɗin zuwa Abuja."

Hanif ya harare sa yace, "ai kuwa kamar a kunnen Momy."

Dariya Ammee ta fashe dashi Maryamu na taya ta; ganin yanda Sadiq ɗin ya kwaɓe fuska yana yi wa Hanif ɗin magiya

Da Yusaira da Aakifan tare suka dawo daga kitchen, ita Yusaira tana riƙe da cups; Ammee ta bata umarnin ta zuba musu ta basu, while Aakifah kuma ta ajiye
End Ads