x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 31 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 90001 words
  • 93000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 396

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
ji kana faɗa a waya za a sauya mishi Ƙoda, don Allah Dady a saka mishi nawa ba na son Yaya SHAREEF ya mutu ya bar Ni."

Da mamaki Dady yake kallonta, sai yace, "Maryam ba yanda za a yi a cire miki ƙoda a saka mishi, ke yarinya ce ƙarama ki dena tayar da hankalin ki a kan wannan matsalar, ba wai an rasa ƙodan bane za a samu kuma za a saka mishi zai warke kamar kowa ya tashi kina jina? Kin yi sallah ma?"

Kanta ta girgiza mishi, sai kuma cike da sanyin murya tace, "don Allah Dady a saka mishi nawa wlh na amince zan ba shi nawa ƙodan, ai shi Mijina ne ina da damar da zan iya taimaka masa a rayuwa."

"Maryam ba ki da hurumin da za ki iya bada ƙodan ki ba tare da sanin iyayen ki ba, in fact ma ke amana ce a wuri na bazai yiwu haka kawai a cire miki ƙoda a saka wa SHAREEF ba. Ko kina da damar taimaka masa sai da sanin iyayenki. Ki bari zamu ga abun da hali zai yi, in ba a samu ba sai a cire naki a saka mishi, hakan yayi miki?"

Da sauri ta ɗaga mishi kai cikin farin ciki

Sai yayi mata murmushi yace, "yauwa to, je kiyi sallan ki dawo sai mu wuce asibitin ma ki duba sa."

Kafin ma ya rufe bakin; har ta amsa mishi ta tashi ta wuce da sauri

Yayinda ya raka ta da kallo yana mai ci gaba da mamakin yarinyar; da kuma wani irin tausayinta da ya kama shi don ya san cewa yanda take ƙaunar SHAREEF har zuciyarta; shi ba ya mata haka, dole zata sha wahala yarinyar, bai san meyasa SHAREEF ya tsane ta ba, kuma shi ba wata budurwa ce da shi ba bare yayi tunanin hankalin sa yana a kanta ne, amma koma dai mene ne bazai taɓa barin SHAREEF ya wulakanta ta ba, ko yana so ko ba ya so sai ya zauna da ita, auren su mutu ka raba ne babu saki a tsakani, Maryamu ita ya zaɓa wa ɗansa SHAREEF

Mike wa yayi ya wuce saman da sauri yayi alwala, sannan ya fito ya wuce masallaci

A tare suka dawo da Sadiq suka tarar da Maryamu tana faman jiran su, shiyasa Dady yace, "su wuce gaba ɗaya zuwa asibitin."

Bayan sun je lokacin Momy ne kaɗai a wurin sa, itama idar da sallanta kenan tana zaune tana lazimi,
Shi kuma SHAREEF ɗin yana kwance a saman gado, sai dai idanunsa biyu amma ya rufe su, jin shigowar su Dadyn ne ya buɗe idon yana kallon su

"My son, ya jikin naka?"
A cewar Dady yana bin sa da kallo tare da shafa masa kai

Murmushi yayi yace, "alhamdulillah Dady."

Sadiq shima ya jikin yayi masa yana ƙara matsowa kusa dashi

Ya amsa cikin kula wa yana kallonsa, har yanzu da ɗan guntun murmushin sa

"Taho nan daughter ki yi masa sannu da jikin, Sadiq janye jikinka tunda ka gaishe shi." Cewar Momy tana kamo hannun Maryamu da ke bayansu

Tunda SHAREEF ya ɗaura ido a kanta sau ɗaya bai sake kallonta ba

Yayinda ita kuma ta matso sosai wurin sa, duk idanunta sun kaɗa sun yi jazur kowa ya kalle ta ya san tayi kuka, muryanta ma a raunane take yi wa SHAREEF ɗin sannu

Amma bai amsa ba sai da Momy tayi masa magana sannan ne ya amsa ta a daƙile. Dukkan su sun fahimci yanayin da ya amsa mata tamkar ba ya so, sai dai ba wanda yayi magana a cikin su, sai Momy ne da ta koma tambayar Maryamun dalilin yin kukan nata sabida ganin yanda idanunta suka yi

Sadiq yace, "ai Momy tunda na sanar mata ta tayar da hankalin ta tana ta kuka wai sai na kawo ta." Ya ƙare maganar yana ƴar dariya
      

Ita kuma ta harare sa tana cewa, "to wa yace ka faɗa mata don ƙaniyar ka? Cewa nayi fa ka ɗauko ta a school ba wai ka sanar mata halin da yake ciki ba, yanzu ga shi nan ka saka min ita kuka." Sai ta ƙara kallon Maryamun da a yanzu take shirin yin wani kukan, don har idanunta sun cika da hawaye ta kasa jure wa, "kar dai a ce wani kukan za ki sake yi? Ya isa haka Maryam ba ki ga ya samu sauƙi bane?"

Gyaɗa kanta tayi tana saurin saka hannunta; tare da share hawayen da har sun sauka a kan fuskarta

While SHAREEF kamar ya maƙure yarinyar haka yake ji; sabida yanda ya ga iyayen nasa sun raja'a a kanta suna bata baki, nufin ta kenan don shi take kukan? Tsaki ya ja a ransa yana lumshe idanunsa tare da sake jin haushin ta sosai,
Allah ya gani ya tsani yarinyar wlh, bai san meyasa ba duk idan ya kalle ta haushi da ɓacin rai; gami da zallan tsanar ta yake ƙara tasiri a zuciyarsa, in so samu ne ya dena ganin ta gaba ɗaya a cikin rayuwarsa, don shi ba ya son abun da zai takura sa bare ya saka mishi damuwa a tare da shi, har yaushe ma wannan ƙanƙanuwar yarinyar da yake ganin ta ƙaramar alhaki; har yaushe ta san soyayya?

Bayan sun gama rarrashinta ne Momy take sanar da Dady zuwan Hanif da ya dage sai ya dawo, "don haka gwara ya kira sa yayi mishi magana don ita ta hana shi amma yace sai ya dawo."

Dady yace, "ok zan kira shi, ai bai kamata ya dawo ba since jikin SHAREEF ɗin da sauki, zan kira sa muyi magana, bari in je wurin Doctor in dawo."

Daga haka ya fita ya bar su a ɗakin. Sadiq ya zauna a gefen ƙafafun SHAREEF

Ita kuma Maryamu tana saman kujera wacce Momy tace ta zauna a kai. Sai kallon SHAREEF ɗin take yi zuciyarta cike da tsananin tausayin sa, musamman yanda ta ga bandage na kansa da aka sanya mishi duk ya jiƙe da jini, wani yawu ta haɗiye mai kauri tana lumshe idanunta, jin wasu hawayen suna shirin fito mata shiyasa tayi saurin buɗe idon don ba ta buƙatar Momy ta sake fahimtar tana kuka. Karaf idanunta suka shige cikin nasa da shima ya buɗe ya aza a kanta,
Wani irin kallo ya watsa mata wanda yasa lokaci ɗaya ta ɗauke nata idon a kansa, sosai take jin bugun zuciya kamar ana zare mata laka daga jikinta, bata sake ɗago kai ta kalle sa ba bare tayi magana, wani irin kuka ne yake son kufce mata, bata san meyasa Yaya SHAREEF ba ya ƙaunarta ba, amma me tayi masa a rayuwa? Hakan na saka ta ta ji zuciyarta tana mata zafi sosai, tana son tayi abun da zai so ta sosai, tana son tayi rayuwa dashi, baza ta iya jure wannan yanayin ba, ba ta son yana nuna mata tsana, tana son ya kasance kusa da ita domin samun farin ciki a zuciyarta, ko kallonsa yanzu ya hana ta yi, tsoron kallonsa take yi don kar ta ɓata mishi rai, amma ya zata yi?

Har suka tashi tafiya ta kasa sakin jikinta a wurin, sabida da zaran ta ɗago kanta sai sun haɗa ido dashi yana sakar mata mummunar kallon nan nasa da ke faɗar mata da gaba, har tsoron kar ya furta wani abu a kanta take yi don ta san tsab zai iya zagin ta ko yace tana kallonsa, shiyasa duk ta kasa sakin jikinta,
Har suka tashi tafiya aka bar Sadiq a wurin sa tunda shi zai kwana dashi,
Daga nan suka wuce gida

Basu tsaya wani hira ba Momy tace, "ta je ta kwanta."
Haka nan babu yanda ta iya dole ta tafi ɗaki ta kwanta, duk da tana jin barci bazai taba zuwan mata ba saboda halin damuwar da take ciki, da kuma tunanin SHAREEF da ya gallabe ta

Dady kuma bai ɓoye wa Momy komai ba halin da ake ciki, a kan zancen Doctor tunda bata san da maganar ba, yanzu dole sai dai su tashi tsaye da yin masa addu'a don ganin an dace an yi aikin nan lafiya, sannan ya faɗa mata abun da Maryamu tace duk da bai ɗauki maganar nata da wani muhimmanci ba

Haka zalika itama Momy, don ta san bazai yiwu a ce Maryamu ce zata bada ƙodan ta bA, ko ma dai mene ne zasu san yanda za a yi a samu kafin kwana biyu da doctor ya ɗiba musu

Amma kuma me? yanda Maryamu ta ga rana haka ta ga dare a ranan, gani take yi kamar in tayi wasa bata taimaki SHAREEF ba zata iya rasa shi a duniya, gani take yi tana da hanyar taimaka masa, wataƙil ma idan aka cire wani abu a cikin jikinta aka sanya mishi zai ƙaunace ta, domin ta sha jin labarin irin hakan, idan aka cire wani abu daga cikin mutum aka sanya wa wani, to jinin su zai haɗu su ji suna ƙaunar juna matuƙa, hakan ya bata ƙwarin gwiwa da tunanin dole sai dai a cire nata ƙodan a saka mishi, baza ta taɓa bari a saka mishi na wani ba tunda ita take sonshi, kuma ta tabbata in har aka sanya mishi zai ji a ransa yana sonta sosai, ko bai san ita ta ba shi ba zai iya ƙaunarta. Don haka da safe ƙin shirya wa tayi ta tafi makarantar, ta sami Dady har da kukan ta a kan, "a cire nata don Allah a saka mishi, wataƙil zai so ta in wani abu nata yana yawo a jikinsa."

Su kansu mamaki ne ya kusa kashe su da zancen Maryamu, don gani suke yi tamkar bata da hankali akwai wauta a tare da ita, don an cire ƙoda an saka wa SHAREEF ba hakan ke nufin zai so ta ba, duk yanda suka so su fahimtar da ita amma ta ƙi gane wa; kuka sosai take musu sun rasa yanda zasu yi da ita

Wannan wanne irin soyayya ce Maryamu take yi wa SHAREEF? Dady yace, "Maryam ko ba ki ba shi ƙodan ki ba ke Matar SHAREEF ne, babu mai raba ku sai mutuwa, don haka ki kwantar da hankalin ki za a yi mishi aiki ba sai an taɓa lafiyar ki ba."

Kuka ta fashe da shi tare da furta, "don Allah ku taimaka min ku saka mishi nawa, wlh zan fi samun farin ciki muddin ƙoda na ta shiga jikinsa, ina matuƙar sonsa, bazan bari a saka mishi na wani ba, Ni ce Matarsa zan iya taimaka masa Ni dai na amince a saka mishi ƙoda na, Ni ba sai kun sanar da iyayena ba wannan sirri ne daga Ni sai shi, ba na son kowa ya sani ku taimaka min kar ya mutu, idan ya mutu nima mutuwa zan yi."

Yanda ta fita hayyacin ta tana musu kuka kamar ranta zai fita, dole suka amince a kan sun yarda da maganar ta, sannan fa suka samu kanta, sun rasa ma yanda zasu yi da ita, duk da basu so hakan ba amma gani suke yi soyayyar da Maryamu take yi wa SHAREEF yayi yawa, sannan ma kasancewar ta Matarsa basu da yanda zasu yi tunda ta matsa sosai, ga halin da take ciki duk ta haukace musu

Bayan Dady ya je wurin Doctor ya sanar mishi da samun kidney ɗin, amma yayi masa bayanin, "ƙaramar yarinya ce in da wata matsalar da za a samu ya faɗa masa, yarinyar ce ta nace dole sai nata za a saka tunda Mijinta ne, baza ta yarda a saka mishi na wani ba."


Shi kansa Doctorn yayi mamakin yarinyar musamman da ya ganta, duk da babu wata matsala don har ya sanya musu ranan da za a yi aikin nan da gobe insha Allahu, tunda an samu baza a tsaya wani jira ba.
  
[18/02, 7:18 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

          *SHAREEF*
            _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*





*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days.













__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE34*
_____A washe gari kamar yanda Doctor ya saka ranan da za a yi aikin,
the operation was done successfully, and everything is fine, there are no problems, inda kowannen su an ajiye sa a ɗaki daban kuma ana basu kula wa

Duk da an yi aikin amma su Dady basu sanar ga wanda ya bada ƙodan ba, domin suna gudun surutun mutane musamman dangin Momy da ba sa iya gani su ƙyale, sun cika gutsiri tsoma, kawai an fada musu an siya ne daga wurin wani Mutumin da yake buƙatar kuɗi, duk da haka dai ana ta ƙananun maganganu

Ita dai Momy bata ce komai ba, domin ko yan uwanta da suke ciki ɗaya bata faɗa musu gaskiyar zancen ba

Sadiq shi ke zama a wurin Maryamu in Momy tana ɗakin SHAREEF tare da mutane, shiyasa babu wanda zai fahimci wani abu

Bare jikin Maryamun ma da ɗan sauƙi, don ita kwana ɗaya tayi ta farka, sai dai ba ta iya yin komai sai an yi mata, in fact ma ba ta gane wasu mutane

Shi Dady ba ya zama saboda wannan kwangilar da suka ɗauka, da kuma asarar da suka samu na ƙonewar kaya, yayinda Turawan sun matsa a kan aikin su, don su basu damu da wata asara ba, ba sa son lokaci ya ƙure ba a fara musu aiki ba, shiyasa Dady yake zuwa Company, inda har ya yanke hukunci dole ya sako su Alhaji Inuwa suka yi raba dai-dai a kan hannun jarin, tunda ba su da yanda zasu yi, an rigada an ja musu asara sun rasa dukiyar su, sannan ko yace zai siyar da ƙadarorin sa za a ɗan ja lokaci, shiyasa da su Alhaji Inuwa suka kawo mishi ƙoƙon baran su na cewan, "a basu hannun jari zasu biya nan take, don a ci gaba da aikin gadan-gadan." Bai ja wata gardama ba ya amince da bukatar su, tunda duk taimakekeniya ce, sannan shi Dady ba kamar SHAREEF yake ba, yana da sauƙin kai, in dai wani zai samu a harkan ba ya ma Mutum baƙin ciki, gwara kowa ya ƙaru, tun farko shi bai ma san da zancen ba; tunda a tunanin sa Companin sa kaɗai aka siyar wa da hannun jarin gaba ɗaya, babu masu bukata, abun da SHAREEF ya faɗa masa kenan, kuma yayi murna tunda ba ƙaramin ci gaba zasu samu ba, amma kuma sai ga shi yanda Allah ya kasance komai muƙaddari ne.
***

_____Inda su Alhaji Inuwa suka yi farin ciki matuƙa da samun nasarar nan, tunda already su saka yi kurɗa-kurɗan da suka yi suka ƙona kayan; tare da taimakon Shuraihu

Babu wanda ya kawo zargin cewa da sa hannun magauta a wannan gobarar, Mahmud shi kansa da farko ya so ɗaura zargi tunda ga abun da ya faru, yana ji a ransa dole da saka hannun su Honourable Ja'e a gobarar nan, amma kuma kasancewar bai sanar da SHAREEF tun farko ba, sannan bai da wata hujjar da zai iya cewa su ne, shiyasa ya bar abun a cikin sa, duk da ya samu Shuraihu da zancen yana faɗa masa, "yana tunanin ko su ne suka aikata hakan domin su samu cikan burin su, tunda ga shi nan sai da hakan ta kasance, daga karshe sun samu hannun jari a ciki, shi dai yana zargin su, kuma dole su tsaurara bincike domin samun hujja mai ƙarfi, daga nan su gabatar wa da SHAREEF."

Shuraihu yace, "a'a; gaskiya ba na tunanin da saka hannun su, taya kake tunanin zasu iya ƙona miliyoyin kaya irin haka; ba tare da asirin su ya tonu ba? Ni dai ina kyautata zaton gobara ne kawai daga Allah, kuma ƙarshe baka ga yanda komai ya zama toka bA? Abun mamakin ya za a yi kaya irin waɗannan su zama toka har da abubuwan da wuta ba ta cin su? Mahmoud kar mu saka kanmu inda zamu kasa fitar da kanmu, Alhaji Inuwa da Honourable Ja'e ba ƙananun mutane bane, muddin muka ce zamu shiga gonan su daga ƙarshe mu zamu kwana a ciki, mu bar maganar nan."

Mahmud yace, "shikenan, dama nima ba wai nace wani abu bane, kawai hasashe na ne ya kawo hakan, tunda ga yanda suka sha alwashi sannan komai ya kasance yanda suke so."

"Mu bar maganar nan don Allah, Ni bari in wuce."

Mahmud kuma har zuciyarsa ya kasa barin zancen, kuma tabbas yana ji a jikinsa su suka aikata hakan, dole zai yi bincike sannan zai sanar da SHAREEF da zaran ya samu lafiya.






🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆

_____Almost two weeks suka yi a asibitin before a sallame su, jikin da sauƙi but koda suka koma gida sun ci gaba da shan magungunan su ne

SHAREEF shi bai san cewa ƙodan Maryamu aka sanya mishi ba, in fact ma bai damu ya sani ba tunda a gaban shi a asibiti ya ji Momy tana yi wa wasu daga cikin dangin ta bayanin yanda aka yi aka samu, to a tunanin shi da gasken siya aka yi, shiyasa bai damu da maganar ba, bai san ma Maryamu bata da lafiya ba sai da suka dawo gida, kuma bai tambaya ya san me ke damunta ba since ba ta gabansa a yanzu,
A halin yanzu farin ciki yake yi kasancewar Haseena ta ce, "zata zo gaishe shi, zuwa gobe ko jibi zata dawo."
Hakan yasa yake farin ciki tare da tunanin gabatar da ita wurin iyayensa don su san wacce yake ƙauna, inyaso da zaran ta dawo hutu sai a yi musu aure, tunda abun yana ransa ba ƙaramin bukatar aure yake yi ba a wannan gaɓar

Itama Maryamu tunda jikin da sauƙi a washe gari Sadiq ya kaita school

Kawayenta su Feena ba ƙaramin tausaya mata suka yi ba, don kallo ɗaya da suka yi mata sun ga ta rame sosai, har haske tayi ta ƙara fresh sai hucewar mura a gefen bakin ta, koda gani ka san tayi jinya sosai

Amina ta kalle ta tace, "I'm sorry friend, wlh mun so zuwa gida mu duba ki amma Allah bai yi ba, ga shi har kin ƙare rashin lafiyar ki bamu zo ba, bamu kyauta miki ba."

Feena itama tace, "kiyi haƙuri
End Ads