peaking wayan,
Bai saurari Hanif da ke masa magana ba ya mayar da hankalin sa a kan Haseena; da ta soma masa ƙorafin rashin kiranta da bai yi ba, har sai da ita ta neme sa
Fita Hanif yayi ya bar sa a wurin yana waya
Ya ɗauki time yana wayan tare da biye wa Haseena tana ta mishi Shagwaɓa. Ya jima zaune a wurin har sai da ya kalli agogon da ke bangon ɗakin, ya ga kusan tara saura, da sauri yayi mata sallama ya faɗa mata, "zai kira ta zuwa anjima in ya je office."
Miƙe wa yayi ya nufi bakin toilet ya zura takalman da ke wurin, ya shige ciki,
Sai da yayi brush sannan ya zare kayan barcin sa; riga da wando da ke jikinsa, sannan yayi wanka ya fito,
Bakin dressing mirror ya nufa yana faman tsane jikinsa da towel, sai da ya gama tsatstsafe jikinsa kaf ya ƙafe babu sauran ruwa, sannan ya soma shafa lotion, after ya gama ya koma bakin closet ɗin sa ya zaro suit sak irin na Hanif,
Fararen kaya ne riga da wando har na ciki, sai dai nashi necktie ɗin red colour ne; while na Hanif sky gree ne,
Sai da ya gama saka wa sai ya ɗauki cover shoes farare ya saka; ba tare da ya sanya socks ba,
Ya koma gaban mirror ya feshe jikinsa da performance ɗin sa sai tashin ƙamshi yake yi, iya ƙalƙaluwa ya ƙalƙalu gashin kan nan sai shining yake yi yana ɗaukar ido, duk da cikin sauri yake yin komai nasa but sai da ya ja time sosai
Amma a haka da ya fita Hanif na can yana jiransa a Falo. Tare da Momy kaɗai suke zaune since Dady ya fita shima yanzu,
Sadiq kuma na dakinsa yana shan barci tunda yanzu sun yi Hutu babu school
"Mom. Morning."
Kallonsa tayi, ba tare da ta amsa ba tace, "sai yanzu? Ka soma lalaci since kana ganin Hanif ya dawo kenan?"
Tura baki yayi
While Hanif da ke shan tea; cup din yana riƙe a hannunsa yake cewa, "haka yace Momy, abun da ke ransa kenan wlh, har ya soma ƙorafin hidima zai yi masa yawa tunda zai yi aure."
Harara Momy ta watsa mishi, tace, "auren da babu amfanin yin sa, har wani murna zaka yi? Ka je kayi breakfast ɗin ka time na wuce wa, in ba dai fasa zuwa zaku yi ba gaba ɗaya, kaima nayi maka maganar ka tafi but ka zauna sai ka jira sa."
Tsuke fuska SHAREEF yayi yana wuce wa wurin Dinnig; ba tare da yace komai ba ya je ya zauna yana ajiye Jakarsa da phone din sa a other side,
Yana jin su suna hira but bai sake saka musu baki ba; duk a kan maganar auren sa ne duk da yana jin babu daɗi da yanda Momy take kushe auren, shi dai bai damu ba tunda ya samu zaɓin shi, kuma ya san cewa wata rana Momy zata so Haseena since bata da wata aibu a ganinsa, yarinya ce wayayyiya zata ji daɗin zama da ita, ya san duk sabida wancan mai bak'ar fuskar ne ba sa son Haseena, amma komai lokaci ne; da sannu komai zai wuce, shi dai bazai ɓata lokacin sa a kan wancan yarinyar da yake ganin ta tamkar mahaukaciya ba
Sai da Momy ta sake mishi magana sannan ya taso suka fita da Hanif ɗin, tsaban son jiki irin na SHAREEF tunda ya ga akwai Hanif, ya ƙi yin tuƙi sai dai Hanif ne ya tuƙa su
Bayan sun isa Companin; tare suka wuce kansu tsaye office din SHAREEF,
PA ya buɗe musu ƙofan sannan suka shiga, ya bi su riƙe da files suna gaisawa da Hanif cikin faram-faram since sun saba
Sai da suka zauna PA ya ajiye files ɗin a gaban SHAREEF, yana faɗa masa, "sabbin contract ɗin da aka amsa ne ana buƙatar ya duba sabida za a yi zama dasu, and sai kuma files na sabbin ma'aikata waɗanda yace za a ɗauke su."
Bai buɗe ba yace mishi, "ya miƙa ma Hanif shi zai duba, ya kai mishi office din sa ya ajiye, and ya kira masa Mahmud su zo tare."
After ya fita. Hanif yace, "nima zan tafi cuz na ga ka fara tuma min aiki, zan wuce in yi abun da ke gabana, amma kuma ana buƙatar masu aiki har guda nawa ne?"
SHAREEF da ke duba file ɗaya da ya ɗauka, sai ya dakata yana kallon Hanif ɗin tare da cewa, "kamar mutane goma muke son ɗauka, ka san yanzu mun kori wasu daga ciki, har Shuraihu yanzu haka ba ya aiki a Companin, we need a new manager."
In surprise Hanif ke kallonsa da cewan, "duk yaushe aka yi haka? Me ya faru ne Please tell me?"
Cikin rashin damuwa SHAREEF ya ba shi labarin komai, har waɗanda suke zargi da suka samu a Companin gaba ɗaya yayi musu koren kare, ya ƙare da furta, "idan waɗannan mutanen ban wulaƙanta su ba; ban cika Ni SHAREEF ba wlh, domin sai sun biya abun da suka aikata, gobe baza su sake wannan gangancin ba."
Cikin rashin jin dadi Hanif yace, "I never thought that from Shuraihu, he surprised me a lot, amma sai dai shawaran da Mahmud ya baka shi yakamata kayi amfani dashi tun farko, domin idan suna Companin nan shine zaka fi samun hujja daga gare su, yanzu ya ake ciki to? Tawanne hanya zamu iya cin galaba a kansu? Tabbas in ba a ɗauki mataki ba nan gaba zasu iya yin fiye da haka, nima raina ya ɓaci. What you have done is right, action must be taken against them."
"Let Mahmud come and see if there is anything at his place."
Suna nan zaune sai ga Mahmud sun shigo tare da PA, zama suka yi bayan Mahmud sun gaisa da su SHAREEF; yayinda Mahmud ɗin ya sake yi wa Hanif congratulations har suna ɗan zolayan juna since sun saba,
Hanif kowa nasa ne
After sun ɗauki lokaci SHAREEF ya katse su yana tambayar Mahmud ɗin a kan ci gaban da aka samu na hujjojin da suke nema?
Mahmud ya ɗan ja numfashi before ya sanar musu, "har yanzu babu wani ci gaba, don ya kasa samun ƙwaƙƙwaran hujja a kan su, sabida su Alhaji Inuwa ba ƙaramin wayon ne da su ba, yanzu ma already har su Shuraihu sun soma aiki a ƙarƙashin Companin su, sun basu office a can."
SHAREEF shiru yayi bai sake magana ba; yana sauraron zantukan su yayinda ya faɗa duniyar tunanin ta'inda zai samu damar ɗaukar fansa a kan waɗannan Mutanen, domin bazai taɓa ƙyale su ba muddin yana numfashi, bazai yarda yayi Failed ba
Sun jima suna tattaunawa sannan suka watse kowa ya tafi office din sa
Bayan Hanif ya koma nashi office din; sai da ya zauna ya natsa sannan ya kira secretary ɗin sa yace masa, "ina ma'aikatan suna ready ko?"
"Yes sir, suna nan a waje suna jira."
"Ok." Sai ya ɗauko files ɗin ya soma duba na farko, sunan da ya gani yace mishi, "ya je ya shigo da mai sunan."
Fita yayi, babu jima wa sai ga wata budurwa ta shigo cikin office ɗin, tana sanye da dogon Hijab baƙi har ƙasa ba a ganin komai nata, sai flat shoes ɗin ta da ta sanya masu ƙyalƙyali su ma baƙi, tana da ɗan tsawo da kaurin jiki, kuma ba fara bace can; za a iya kiranta da wankan tarwaɗa, tana da kyawun ta dai-dai gwargwado tare da dogon hanci kamar bairo mai ɗaukar hankali a kan face ɗin ta,
Bayan ta shigo sai ta tsaya a bakin ƙofan tana ƙwanƙwasa ƙofan
Hakan ne yasa Hanif ya ɗago yana duban ta suka haɗa ido, kallon kallo suka yi wa juna kowannen su bai iya ɗauke ido a kan ɗayan sa ba
While ita kamar da tsoro a tare da ita, amma ta dage tana faman haɗiyar yawu
Yana ganin yanda wuyanta ke motsi, shi mamaki ma yayi ganin ta tsaya ta kafe shi da ido kuma ta ƙi ƙarisowa, ga ta a cikin office din but tana mishi nocking,
Ɗan janye idanunsa yayi sabida yanda ta kafe sa da ido ta ƙi kawar da kanta, sai ya mayar kan computern sa yana cewa, "Yes come in."
Takowa tayi a hankali tana ɗan gyara wuyan Hijabin ta, tare da ƙara kame jikinta tukun ta samu wuri ta zauna; sabida har ya nuna mata wurin zama bai ce komai ba
"Ke ce Amra Abubakar?" Ya furta ba tare da ya kalle ta ba
Ita kuma sai tayi shiru tana kallonsa ganin ba ya kallonta, bata san ta yanda zata yi mishi bayanin ita ce ba,
Sai da ta ga ya ɗago kansa sannan tayi saurin murmusa mishi tana gyaɗa mishi kai
Har sai da gabansa ya faɗi sabida ganin wannan murmushin nata wanda ya ƙara bayyana kyawun ta,
Haka kawai ya ga yarinyar tayi masa kwarjini musamman yanda ta zuba mishi ido tana sakar mishi smile ɗin ta har yanzu bai gushe daga kan fuskarta ba,
Har ya ɗan shagala da kallonta sai kuma ya kama kansa yace, "kin taɓa aiki a wani wuri ne; ko kuma nan ne first inda kika soma?"
Kai ta ɗaga masa tana mishi nuni da hannunta; alamun tana masa bayani cikin kurmanci tunda baza ta iya magana ba
Shi kuma tuni ya waro ido sabida ganin abun da take yi, "kenan kurma ce?" Ya furta a fili ba tare da ya san ya ambata ba; mamaki kwance a kan face ɗin sa.
[07/03, 8:32 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱
__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE51to52*
_____Shiru yayi yana zuba mata ido; ganin yanda take ta bayani da hannu har ta gama tayi shiru itama tana kallonsa
Sai dai a yanzu babu ɗan murmushin a kan face ɗin ta; alamun kamar tana cikin damuwa ganin yanda Hanif ya tsare ta da ido ya ƙi cewa komai, idanunta har sun cika da hawaye domin tana ganin kamar a nan ma baza tayi nasara ba, duk sabida wannan laluran da Allah ya bata ana ganin kamar gazawan ta ne
A lokacin Hanif ya kasa yin magana ne don tsananin mamakin yarinyar, wai kurma kuma ta zo neman aiki a nan?
Shiru yayi yana ganin yanda idanunta suka soma ciko da ƙwalla, hakan ne yasa ya buɗe baki with surprise yace, "are you cry?"
Hawayen ne suka zubo a kan kuncin ta, sai ta sauko daga saman kujeran tayi kneel down tare da haɗe hannayen ta cikin roƙo take masa magiyan da bai san ma me take cewa ba; tunda bai iya maganar kurma ba, kawai dai ya fahimci tana roƙon sa ne tunda ga shi har da hawayen ta
Files ɗin ta ya soma kallo yana ganin duk bayanan ta, yayi mamakin hazaƙan ta amma kuma ga ta ta kasance kurma,
Lokaci guda a kuma yanayin da bai san wanne irin yanayi bane ya same shi, wani irin tausayin ta ne ya kama shi,
Mace kamar wannan amma a ce baza ta iya furta magana ba, Allah ya tauye ta ta wannan fannin, amma kuma ga shi bata zauna ba tana neman na kanta,
Har ga Allah ya ji tausayin ta tunda shi Mutum ne mai tausayi, yana ganin bazai iya bari ta tafi bai taimake ta ba, duk da babban matsala ce rashin maganar nata, ba kowa zai iya ɗaukar aiki kamar na Company ya ba Kurma wacce ba ta iya magana ba, sai dai ta ji magana but bata san ya za a yi ta mayar ba, duk da a yanayin aikin office zata iya yin aikinta normal babu matsala, idan za a duba maganar ta bazai kawo cikas a kan aikin ta ba,
Nuna mata yayi alamun ta miƙe ta zauna
Hakan ne yasa ta miƙe da sauri jiki na rawa ta zauna; tana faman share hawayenta, yayinda take bin shi da kallo tana jiran ta ji mai zai ce, a ranta kuma addu'a take yi Allah yasa ta dace, wannan aikin shi kaɗai ya rage mata a halin yanzu, sun rasa komai nasu,
Mahaifinsu gatan su ya mutu ya bar su a lokacin da basu yi tsammani ba, komai nasu ya ƙare ƴan uwansa sun danne musu haƙƙin su, lokaci guda rayuwa ta sauya musu, ga shi ita ce babba a wurin Iyayenta, sai Ƙanninta guda biyu Mata ƙanana waɗanda ko secondary school basu gama ba,
Ita kaɗai ce tayi karatu har ta kammala NCE ɗin ta; da jajircewar iyayenta duk da ba ta iya magana, amma sun dage sun bata ilmi, ashe akwai ranan da zai yi musu amfani, tunda ga shi a wannan gaɓar da suka rasa komai nasu abinci yana son gagaran su, dole ta ɗauki kwalin ta ta soma ƙoƙarin neman aiki kurɗa-kurɗa,
Amma duk inda ta je bata samun Sa'a; sabida tawayan da Allah yayi mata suna ganin kamar ta gaza, basu iya ɗaukar ta aiki a haka ba,
Amra bata sare ba tunda Yarinya ce mai ƙoƙari da nuna dagiyar ta a kan abu, haka ta ci gaba da nema ana wulaƙanta ta; har wasu suna buƙatar wani abu daga gare ta, amma bata taɓa watsi da tarbiyyar da aka basu ba, ta jajirce dole sai ta nemi nata ta taimaki ƴan uwanta da Mahaifiyarta, bata taɓa sare wa ba,
Tunda ta ji labarin wannan Companin suna neman sabbin ma'aikata a wurin ƙawarta, sai ta bazamo jiki sai da ta samu ta ga kwalin ta sun wuce sannan ta ɗan samu sanyi a ranta, sai ta zauna zaman jiran ranan da za a kira su a yi musu interview,
Kullum cikin zullumi da tunani take; tare da addu'a babu dare babu rana don ganin ta samu wannan aikin,
Baza ta so a ce wannan karon ma bata yi nasara ba, baza ta so hakan ta kasance da ita ba,
Amma ganin Hanif da kuma yanayin fuskarsa sai ta ga kamar yana da tausayin da zai iya taimaka mata, shiyasa har ta duƙa tana hawaye tana roƙon sa a kan ya taimaka mata tana mishi bayanin halin da take ciki,
Amma bai fahimta ba tunda ba sanin Yaren nata yake yi ba
Shi kansa yana son sanin wace ce ita, da kuma yanda ta dage take son sai tayi aiki,
Idanunsa ya kawar a kanta tare da janyo Memo ya miƙa mata, ya haɗa da bairo yana ce mata, "ki fada min dalilin son yin aikin ki bayan kin san kina fama da wannan laluran, kin san ba ko'ina za a iya daukar ki aiki ba, don haka ina son sanin reason din ki sabida in san yanda zan yi in taimaka miki."
Da sauri ta janye hannunta a saman face ɗin ta, bayan ta goge sauran hawayenta, sai ta saka hannu ta ɗauki Memon jiki na rawa ta soma rubuta masa irin halin da take ciki,
Sai da tagama sannan ta ba shi Memon
Ya amsa ya karanta yana yi yana kallon face ɗin ta,
Wanda itama tuni ta kafe sa da ido tana jiran mai zai ce mata,
Shiru yayi na ɗan lokaci yana ƙara nazartan abun da ta rubuta, har cikin zuciyarsa yana jin ya yarda da ita kuma yana jin tsananin tausayinta,
Murmushi yayi mata a karon farko yana duban ta, while ya furta, "zamu ɗauke ki aiki in our company, you don't have any problem now insha Allahu."
Wani irin farin ciki ne ya bayyana a kan face ɗin ta, har ta kasa rufe baki tsaban daɗi, sai ga wasu hawayen sun soma fito mata, har ƙasa ta duƙa tana masa godiya cikin yanayin maganar kurmanci
Shi kuma murmushi yayi sabida har a ransa shima ya ji daɗin yanda ta nuna murnan ta, sai yace mata, "ta miƙe ta zauna."
Nan ya ci gaba da duba file ɗin ta na ɗan wasu mintoci before ya bata iznin tafiya, ya faɗa mata, "gobe zata soma aiki, sai ta shigo da wuri."
Murmushi tayi tana kallonsa, sai ta miƙe cikin farin ciki ta haɗe hannayenta wuri ɗaya tana sake mishi godiya,
Before ta fice a Office ɗin har tana sake waiwayo shi
Shima dai ita yake kallo har ta fice, Allah Sarki! Ashe akwai irin waɗannan mutanen a duniya? Naƙasan su ba ya nuna kasawan su?
Ya faɗa duniyar tunani sai ga Secretaryn sa ya shigo office ɗin,
Hakan ne yasa ya daidaita kansa tare da ba shi wani sunan yace, "ya kira mai sunan".
🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆
_____Farin cikin da Amra ta fito dashi daga office ɗin Hanif; ya gaza gushe wa a kan face ɗin ta,
Ko tsayawa bata yi ba ta nufi bakin gate da saurin ta cike da tsananin murna; da kuma Allah - Allah ta isa gida ta sanar da Mamanta,
Tana fita bakin titi sai ta tare adaidaita-sahu
Bata tsaya yin wata-wata ba ta tusa hannunta a cikin Jakarta da ta saƙale ta a hammata, sai ga shi ta fito da ƴar farar takarda mai ɗauke da address ɗin gidan su, ta miƙa masa fuskarta ɗauke da murmushi
Kallonta yayi, sai kuma ya amshi takardan da take ba shi yana duba wa,
Ya gane address ne shiyasa ya sake kallonta tare da furta, "can za ki je?"
Da sauri ta gyaɗa mishi kai alamun eh,
Domin sau tari hakan take yi idan zata je wuri, sai ta rubuta address ɗin sai ta miƙa musu su karanta,
Daga nan sai ta shiga a kaita in sun faɗa mata kuɗin da zata iya biya, in kuma baza ta iya ba sai tayi musu kwatance tare da ciro iya kuɗin da zata iya basu tana nuna musu,
A nan suke gane Kurma ce ita; har wasu su ji tausayinta su ce ta shiga ba tare da sun ja zancen ba
Yanzu ma wannan ya fahimci kamar Kurman ce, shiyasa yace, "ta shiga su tafi."
Haka ya ja napep ɗin har ƙofar gidan su ya dire ta,
Tare da amsan kuɗin da ta ba shi bai yi gardama ba ya wuce abun sa
Ita kuma da gudun ta; ta isa bakin gidan su tana tura ƙyauren gidan ta shige
Da Mamansu ta ci karo tana bakin famfo zata yi wanke-wanke, zaman ta kenan tana kwaɗa wa Ƙanwar Amra kira, wacce take bin ta mai suna Afra, tace mata, "ta kawo mata sauran Omon