x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 50 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 147001 words
  • 150000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 401

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
sabida har ya fice, ko kusa bata damu da yanda ya nuna ba, amma don ta nuna mishi kamar ta damu, bayan sun shiga Mota sai ta soma ba shi hakuri har da ƙwallan ta

"Is ok, yanda kike so hakan zan yi, amma idan na mutu Haseena ke kika kashe Ni, ban san meyasa kike son canza min ba, akwai hanyoyi da dama da zamu bi wanda baza ki ɗauki ciki ba, duk hakurin nan da nayi ba kya gani ko?"
Ya kare maganar yana kallon fuskarta kamar zai yi kuka

Hannunta ta daura a saman cinyansa tana mai langaɓe kanta, "I'm sorry dear, Kayi hakuri ba a son raina bane, but kwana nawa ne ya rage zan gama karatun wai? Lokaci fa gudu yake yi please ka kwantar da hankalin ka don Allah."

Bai yi magana ba har ya kaita gida ya dire ta,
Sai dai dole ya saki face ɗin sa sabida yanda ta dame shi har da kukan ta wai, "ba ta son ganin sa a haka."

Shi dai ya rasa yanda zai yi haka nan ya biye mata ya wuce gida abun sa,
Tun daga ranan ya dena ma fitan da ita tunda ba ya samun biyan buƙata, ko sun fita karshe wahala yake sha, domin har ciwo sai da yayi a ɗan kwanakin nan, ya ƙwallafa rai a kan abu amma ya kasa samu, ba ya son ya ɗauki zafi a kanta since ba ya son ɓacin ranta,
Tun yana ɓoye wa Hanif dole ya sanar masa halin da yake ciki

Hanif yayi mamakin abun da Haseena take yi wa SHAREEF, amma gani yake yi son da yake nuna mata ne yasa yake biye mata take yin duk abun da take so, to meye amfanin soyayyar da kuma auren in har baza ta cire shi a wannan ƙangin da yake ciki ba?
Shi yasa ya sanar mishi, "shi fa yana ganin kamar Haseena hankalin ta ya soma barin wurin sa, yakamata su zauna su fuskanci juna idan ba haka ba zai iya halaka kansa."

SHAREEF ya kasa cewa komai don bai san me zai ce ba, domin shi kaɗai yasan iya azabtuwar da yake yi, ji yake yi kamar bazai kai gobe ba in har bai samu abun da yake so ba, amma ya zai yi? Har ga Allah yana sonta ba ya son ɓacin ranta, tun farko shi ya nace mata ya lallaɓa ta har ta amince suka yi auren, ya san idan ya matsa mata kamar ya cuce ta ne

"Ni ga shawara Bro in har baza ka bi wannan hanyar ba, mai zai hana tunda ba ita kaɗai bace Matarka; ka koma wurin Maryam domin biyan buƙatar ka, dama ai gida biyu maganin gobara ne, tunda dama ta ƙi sai ka koma hagu."

Sai da gaban SHAREEF ya buga sabida jin zantukan Hanif, shi har ga Allah ya manta da shafin yarinyar can, tab ɗijam! Tashin hankali kenan, mai zai faru idan Haseena ta gane yana da wata Matar? Tabbas akwai aiki a gabansa kenan

A tunanin Hanif yayi shiru ne yana sauraron sa, shiyasa sai ya ƙara gyara zama sabida son ya samu galaba a kansa, "Ni na san baka son yarinyar, amma mene ne amfanin ta? A irin wannan halin da kake ciki zaka iya samun solution Bro; ba tare da ka ɓata wa ƴar gaban goshin ka rai ba, Maryam zata iya ɗauke nauyin ka, zaka iya mu'amala da ita ba wai dole sai kana sonta ba, zaka iya biyan buƙatarka da ace ka cutar da kanka, kayi tunani Bro, itama Matarka ce halak malak".
[12/03, 9:19 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

       *SHAREEF*
           _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*





*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days.












__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE57*
_____Wani kallo SHAREEF yake watsa mishi tun soma maganar nasa, tuni ya ɗaure fuskarsa zuciyarsa na tafarfasa da jin kalaman Hanif ɗin, "lallai baka da hankali Hanif, Ni kake nufi zan nemi wannan Jahilar yarinyar baƙauyiya sabida in kau da sha'awata? That will never be possible, because I was stronger than that girl forever, bazan taɓa neman alfarma a wurin wannan ƙasƙantacciyar yarinyar ba, don't do this to me again or you will see my anger again a second time, zan maka abun da baka taɓa tunani ba."
Ya ja tsaki ransa a ɓace yana miƙe wa yabar mishi ɗakin ma


Yayinda Hanif kuwa murmushi yayi yana shafa gemun sa, ko kusa maganar SHAREEF ɗin bai ba shi haushi ba, sai ma taɓe baki da yayi a ransa yana cewa, "akwai ranan ƙin dillaci."
Sai ya ɗage kafaɗa alamun bai damu ba yana mai miƙe wa tare da ajiye wayansa, ya nufi hanyar toilet ya shige.

          Wasa-wasa har hutun su Haseena ya ƙare ta koma school; SHAREEF bai samu abun da yake so ba, amma ya ya iya? Soyayyarta ta rinjayi duk wani abu,
But ya saka a ransa da sannu dole ne ya shawo kanta, ko bai yi nasara yanzu ba zai yi wani lokaci.
***

_____Yau da gobe rayuwa ta ɗaura ta ci gaba da tafiya kamar yadda ta saba, kwanaki na shuɗewa haka ma satikai, yayinda aka ɗaura watanni a kai

Kuma har wannan lokacin soyayyar SHAREEF da Haseena bai canza ba, tun tafiyarta bai samu ya je wurin ta ba, duk da yana ta mata mitan ta ba shi time but ta ƙi, ya lallaɓa ta har ya gaji, shiyasa ya yanke hukuncin zuwan mata a bazata,
Bai samu matsala wurin Iyayensa ba tunda yace musu, "zai je duba Haseena ne."
Ganin Matarsa ce babu wanda ya hana sa, iyakan jan masa kunne da Dady yayi a kan, "bazai riƙa zirya zuwa wurin ta a duk sanda ya so ba, don haka yasan da sani tun wuri dole ya riƙa sanin abun da yakamata, koda Matarsa ce bazai riƙa ziryan zuwa wurin ta a kai- a kai ba."

Shi dai tunda sun bar shi a murnan sa,
Shi yasa ya sanya rana, on Friday ya tafi, since zai dawo Sunday saboda aiki

While Hanif kuma ya ci gaba da kula da companin

Dady kuma shi yake zuwa Abuja idan hakan ta taso, ko shi ko su Mahmud tunda aikin yayi nisa yanzu sosai, gadan -gadan ake yi tunda akwai kuɗi, don ma companin yana da girma ne, ko kwata a yanzu dai ba a yi ba,
Alhamdulillah suna jin daɗin aikin har yanzu babu wata matsala,
Kuma har wannan lokacin suna nan suna neman hujjar da zasu kama su Alh Inuwa sabida ƙona musu kaya da suka yi,
Yayinda su Alh Inuwa sun ƙi barin kowanne kafa domin cin galaba a kansu, sosai suke takun-saƙa yanzu da su SHAREEF, ko magana ba sa yi idan sun haɗu a Abuja, dariya ma su Honourable Ja'e suke mishi don sun mayar dashi bai san ma abun da yake yi ba, tunda sun san sun toshe duk wata kafa da zai samu wata hujja bare ya ɗauki mataki a kansu

Amma SHAREEF ya ƙi haƙura, a ganin sa dole ya ci nasara a kansu, bazai taɓa yafe musu a kan abun da suka yi mishi ba, sai ya ɗauki fansa, SHAREEF akwai kafiya bare irin wannan babban laifi da aka yi mishi, ba zai ɗauki faɗuwa ba.




      🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆

_____Fannin Amra rayuwa ta soma sauya musu sosai, tun sanda ta soma amsar albashi ta mayar da ƙanninta makaranta na boko dana islamiyyar, a yanzu babu abun da ke gagaran su, sun fi ƙarfin komai, Alhamdulillah sai godiyar Allah suke yi, wurin aikin ta ma babu wata matsala tana gunadarwa cikin kwanciyar hankali; musamman yanda Hanif yake jin daɗin aikin ta, don har wani sabo suka yi a yanzu, duk da ita tana ja da baya sosai dashi, kasancewar ta Mace mai kamun kai, bata taɓa kai kanta inda Allah bai kaita ba, tana girmama Hanif matuƙa tamkar mahaifinta, domin gani take yi ya gama mata komai wlh, musamman a albashin ta na farko har ƙara mata kuɗi yayi kyauta,
Ya faɗa mata, "ta kawar da matsalolin gabanta since ta sanar mishi halin da suke ciki."

A lokacin ta ƙi amsa, amma sai da ya tilasta ta, har hawayen dad'i sai da tayi, tayi ta masa godiya har da duƙa masa

Sai ya nuna mata ɓacin ransa yana cewa, "kar ta ƙara duƙa mishi daga yanzu, duk abun da zai yi mata yayi mata ne don Allah."

Tabbas ta yarda, domin lokaci guda ta fahimci wane ne Hanif? Matuƙa yana da sauƙin kai da son mutane, Mutum ne mai kirki fiye da ɗan uwansa, tun bata jima da soma aiki ba ta kula da haka, tana mamakin yanda halin su ya bambanta da SHAREEF, sabida yanda shi yake mu'amalan sa alamun yana da girman kai da nuna isa, kowa ba kowa bane a wurin sa, bambancin halayya ne kawai a tsakanin su, a farko ma da ta fara ganin SHAREEF a zaton ta Hanif ne, sai daga baya ta bambance su since SHAREEF ya fi hasken fata, sannan a halin sa ko fara'a ma bai dashi bare yayi wasa da ma'aikatan

Ita a yanzu matsalar da yake damun ta bai wuce Jabir bane, ɗan uwanta da yake damun ta matuƙa, ya takurawa rayuwarta sosai,
Duk yanda Mama ta so ta ɗauki mataki a kansa abun ya faskara, ga shi Mahaifinsa ba ya ganin laifin sa, ko takai ƙara cin mata mutunci yake yi yace mata, "tana son yin ma ɗanshi sharri."

Abun dai sai gaba-gaba yake yi ya takura wa Amra, shiyasa yanzu kwata-kwata bata da sukuni a ɗan kwanakin nan, sauƙin ta ɗaya ma bata zama a gida, dalilin da yasa kenan da duku-duku zaka ga tabar gidan ta wuce wurin aiki

Har Hanif yana mata ƙorafi yace, "wai kwana biyu tana riga su zuwa. Sai kace a companin take kwana?"

Ita dai dayake tasan matsalarta ba ta iya ce mishi komai sai murmushi,
Bai san cewa akwai dalili ba, hakan ne yasa ko sun tashi ta dena koma wa gidan, takan kai Magriba a ma'aikatan kafin ta tafi, lokacin kowa ya gama tafiya sannan itama take tafiya, su Hanif tun biyar zasu wuce amma ita baza ta tafi ba, saboda tasan tana komawa zata ga Jabir, amma in ta koma gida da duhun Magriba ba ta ganin sa

Mama tayi mata faɗa amma ta ƙi ji, don a ganin ta hakan shine maslaha gwara ta dawo da Magriba tunda baza ta haɗu dashi ba

Shi yasa yau ma tun ƙarfe biyar Hanif ya sallame ta,
Amma sai ta zagaya cikin ma'aikatan; ta ƙi tafiya har kusan shida da rabi, sannan ta fito ta samu abun hawa ya wuce da ita gida, suna zuwa lungun gidan su kamar yanda ta saba sauka, ta sauka ta miƙa mishi kuɗin sa sannan ta nufi gidan su, sai sauri take yi kamar zata tashi sama tunda har an soma kiraye-kirayen sallah,
Gab da zata shige gidan su; sai ta ji an cafko ta an dawo da ita baya kamar zata zube, amma sai jinta tayi cikin jikin Mutum babu zato,
Baki ta buɗe da nufin yin ihu sabida tsananin tsoratan da tayi,
But sai ta ji an rufe mata bakin ana faɗin

"Shiiii! Don uwarki Ni ne."

Take kuwa ta gane mai muryan, shiyasa nan da nan jikinta ya soma rawa kamar mazari, ta soma ƙoƙarin ƙwace kanta amma inaa; ya fi ƙarfin ta,
Kiciniya suka soma yi

Shi kuma sai ya bushe da dariya yana cewa, "shegiya ƴar shila, Ni za ki gwada wa ƙarfi ko? Wato saboda Ni kike ƙin dawowa gida sai kin kai dare? Ko kuma wani cikan kika samu a can yake danne ki kika guje Ni? Yo dama na san ai sai haka babu wani aiki da kike yi, yawon banzanki kike zuwa, amma Ni kin hana Ni na shana da wannan jikin naki mai yalwan albarka."
Ya ƙare yana tatse ta tare da ƙoƙarin ɗaura hannunsa a ƙirjinta

Kuka ta fashe dashi duk da muryanta ba ya fita, da sauri ta sanya hannunta tana riƙe nashi, jikinta sai faman rawa yake yi

Shi kuma sai ya soma yunkurin saɓa ta zai bar wurin da ita, inda har lokacin ya ƙi sakin bakinta

Amma ina Amra ta ƙi yarda, duk da ya fi ƙarfin ta but ta hana faruwar hakan, illa ma kiciniyar fincike jikinta da ta soma yi gaba ɗaya ta ruɗe sai fitar da ruwan hawaye take yi, ga ba bakin magana, tattakura tayi ta dinga yakushin shi a hannu ta kafe sosai ta ƙi bari ya ɗauke ta

Ganin haka sai ya gaura mata mari cikin zafin yakushin da tayi masa, "dan ubanki Ni za ki ji wa ciwo? Ai kuwa zan ga uban da zai ƙwace ki."
Hannu yasa dukka biyun ya kama ta da karfin tsiya ya saɓa ta a bayansa, sai ya nufi hanyar barin wurin yana huci

Nan ta sake rikice wa ta saka kuka tana yarfe ƙafafu da nufin sauka a jikinsa, Allah ya bata Sa'a ta zamo ƙasa but ya riƙe ta gam ya ƙi sakin ta sai ƙoƙarin shi na sake ɗaukar ta yake yi,
Ita kuma ta ƙi yarda kuka take yi sosai tana roƙon sa alamun ya sake ta

"Wlh sai na ci ubanki in ba ki min shiru ba, yau sai na kawar da kwaɗayi na a kan ki ko kina so ko ba kya so."
Take ya ja Hijabin ta ya cire sa da ƙarfin gaske, haka ya soma ƙoƙarin keta mata mutunci da karfi da yaji, duk ya yamutsa ta ya matse ta gam a jikinsa

Ita ko baiwar Allah kuka kawai take yi kamar ranta zai fita, takalmanta da Jakanta gaba ɗaya sun yi gefe, iya galabaita ta galabaita a hannunsa but duk da haka ta ƙi haƙura da kiciniyar ƙwacewa, a ranta addu'a take yi Allah ya kawo mata ɗauki, sai dukan sa take yi amma ina bai saurara mata ba, har rigan ta sai da ya yaga shi gida biyu gaba ɗaya albarkatun ƙirjin ta suka bayyana a idanunsa. Wani irin kuka ta saka mishi tana ƙoƙarin zame wa ƙasa

Amma sai ya tallabo ta jikinsa yana sambatu da ƙwaƙume ta, sai famar jagula ta yake yi kamar wani zautacce, faɗi yake yi, "ka ga ƴar tselan ƴa zata yi min tsakiyar da ba ruwa, wlh bazan taɓa barin ki ba, kaii! Ashe haka kike da kaya iya kaya amma kike min mugun fata?"
Haka ya dinga sambatu yana lashe ta kamar maye, tuni ya sake cafko boobs ɗin ta yakai musu damƙa cikin mugunta da fitan hayyaci, don a lokacin ma ya rigada ya manta a inda yake tsaban Jaraba da son kaiwa inda yake buqata

Yayinda Amra kuwa a time ɗin itama bata san inda kanta yake ba, tsananin tashin hankali da gigicewa yasa ta sume lokaci guda saboda ta kasa ɗaukar abun da ke shirin faruwa da ita.





🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆


_____ *AUSTRALIA*
        *SYDNEY*
Da misalin ƙarfe goma na dare SHAREEF ya isa kofar gidan Haseena, a lokacin da ya isa ya so ya ɗauki waya ya kira ta, but yana taɓa ƙofan gate ɗin sai ya ga a buɗe yake, hakan ne yasa ya zura kansa ciki ba tare da tunanin komai ba, sai ya mayar da wayan cikin aljihu ya tunkari cikin gidan, zuciyarsa cike da farin cikin tozali da muradin ransa,
A bakin ƙofan shiga Falon ya tsaya, ya sanya zara-zaran hannunsa da nufin bude wa, but sai dai nan a rashin Sa'a kamar an sanya lock, hakan ne yasa ya ɗan yamutsa face ɗin sa, ya so har ya shiga ciki ba tare da ta san da zuwan sa ba sai dai ta sha mamaki,
Nocking ya soma yi a hankali while hannunsa ɗaya cikin aljihu, yayinda ya rataya Jakarsa a kafaɗa,
Shiru-shiru ba a buɗe masa ba sai ya ƙara gyara tsayuwar sa tare da kai hannu ya ci gaba da yin nocking ɗin, daga ƙarshe kuma ya koma buga door bell sabida jin shiru har ya soma gajiya,
Guntun tsaki ya ja tare da ciro wayansa,
Har ya soma lalubo numban ta sai ya ji kamar ana ƙoƙarin buɗe masa; at the same time ana faɗin,

"Who is there at the door?"

Jin wata murya daban bana Haseena ba, hakan ne yasa ya ƙi amsa wa sai yayi shiru yana tsira idanunsa a wurin,
Few seconds aka buɗe ƙofan; Nana ta bayyana a gabansa yayinda idanuwansa suka shige cikin nata,
Kallon kallo suka soma yi wa juna while shi SHAREEF tuni ya bi jikinta da kallo da wani irin yanayi da tuni mood ɗin sa ya sauya

Tana tsaye ne riƙe da ƙofan daga ita sai ɗaurin ƙirji, farin towel ne ƙal a jikinta ta ɗaura; wanda ya rufe mata saman ƙirjinta da cikinta, but gaba ɗaya santala-santalan cinyoyinta a waje suke, haka ma gashin kanta wanda ta baza shi har kafaɗun ta na attachment mai ruwan goro da style ɗin ja a ciki,
Kasancewar Nana ta taɓa ganin sa sau ɗaya duk da a ɗan nesa ne, ba sanin ƙurilla tayi masa ba, amma sai da gabanta ya faɗi haɗa idanun da suka yi, ko ba a faɗa mata ba ta tabbatar wannan kyakkyawar saurayin da ke gabanta shi ne Boyfriend ɗin Haseena

Yayinda a wannan lokacin SHAREEF shi kuma mamakin ta yake yi, musamman kallon da yake sauke mata a karon farko a kuma kallon farko zuciyarsa sai da ta hautsine sabida ganin ta, kallo ɗaya da yayi mata ya fahimci wace ce ita, idanunta da suke a tsaitsaye a buɗe sun fallasa mishi ba ƙaramar ƴar duniya bace, bare yanda ya ga bakin ta da hancin ta an zura ɗinkunne, idanun nan sun sha eyelashes duk da babu MakeUp a face ɗin ta, hannayenta ya bi da kallo waɗanda suka sha zobuna ga zaƙo-zaƙon ƙumbuna, sai ta fito sak a karuwarta irin tantiran ƴan barikin nan waɗanda idanuwansu a buɗe suke

Kamar yanda ya kasa yin magana yana bin ta da kallon ƙurilla, haka itama ta kasa furta kalma ko ɗaya illa bin beauty face ɗin sa da kallo da take yi, a ranta tana ayyana abubuwa da dama duk da ba ƙamarin kwarjini yayi mata ba



Muryan Haseena ne ya ratsa kunnuwan su ya katse musu kallon da suke aikawa juna,
End Ads