ranta tana jin tamkar wani abun ne ya same sa, yanda zuciyarta ke beating kamar zai faso ƙirjin ta; ta kasa natsuwa ta ci abincin da ke gabanta
Tana nan zaune sai gani tayi an fito da SHAREEF ɗin, Dady da Sadiq sun riƙo sa
Take hawaye suka silmiyo mata a kan kuncin ta, da sauri ta tashi tana bin su da kallo ta kasa motsa wa, sai rawa da jikinta yake yi,
Ganin sun fita waje itama sai ta take musu baya da saurin ta, a gabanta aka saka shi a Mota tana tsaye kusa da Momy wacce take maganar zata bi su
But Dady ya hana ta, yace, "su zasu je asibitin, ta zauna a gida."
Dole ba don ta so ba ta haƙura, suna gani Motan ta fita before su koma ciki
Maryamu kasa cin abincin tayi tana zaune tana kallon Momy da ke ta faman zirga-zirga fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa
Sai daga baya ne itama ta kula da halin da take ciki, ta kalle ta cike da tausayin ta, sai ta nemi wuri ta zauna tana ce mata, "ci abincin ki Maryam, kar yayi sanyi."
"Momy bazan iya ci ba." Tayi maganar tana ƙoƙarin fashe wa da kuka
"Kar ki yi min kuka a nan, ki ɗauki abincin nan ki ci, SHAREEF babu abin da zai same shi zai warke insha Allahu."
Sai ta soma rarrashinta tana bata baki, daƙyar ta samu ta ƙara yin loma a cikin abincin, sannan tace, "su je suyi sallah, sai su yi masa addu'a Allah ya basa lafiya."
Jiki babu ƙwari Maryamu ta koma ɗakin ta, sai a lokacin wasu hawayen masu ɗumi suka soma sintiri a kan fuskarta, hannu ta sanya tana share wa before ta shiga toilet ta daura alwala, sallah tayi sannan ta yi wa SHAREEF ɗin addu'a, tana gama wa ta tashi ta koma Falo ta zauna
Lokacin ma Momy bata fito ba sai daga baya. haka suka zauna zugum duk da Momy tana gwada kiran numban Dady, but wayan tana ring bai ɗauka ba, zuwan sa ɗaki yin alwala a can ya bar wayan, sai daga baya ne dabaran kiran Sadiq ya faɗo mata, ta danna masa kira tana fatan a ce ya dauki wayan.
Ai kuwa bata daɗe tana ring ba ya ɗauka, hankali a tashe take tambayar sa jikin SHAREEF ɗin?
"Mom har yanzu dai duba sa ake yi, basu fito ba Likitocin."
"Ina Dadyn naku?"
"Ya shiga office din doctor ya kira sa."
"Ok, idan ya fito sai ka sake kira na."
Sai ta kashe wayan tana ajiye wa tare da kallon Maryamu, "Maryam ki je ki sake zuba abincin nan ki ci, sai ki je ki kwanta ki huta, kinga kin wuni a makaranta."
"A'a Momy, na ƙoshi, kuma ba na jin barci."
Shiru tayi bata sake ce mata komai ba, sai ta kunna musu TV ta kamo Sunna TV ana haska wa'azin Bin Usman. Kallon suke yi amma ba wai fahimtar me ake yi suke yi ba, daga ita Momyn har Maryamu
Kusan ƙarfe goma suna wurin amma har yanzu su Dady basu dawo ba, duk da Momy ta sake kira sun yi magana da Dady ya faɗa mata, "ba gado za a basu ba zasu dawo yanzu."
Lokacin Maryamu har ta soma gyangyaɗi sabida mugun barci take ji, amma ta hana kanta yi, da ta fara zata tashi ta mayar da idanunta a kan kallo
Cike da tausayin ta Momy take kallonta, don ta san ta damu sosai da SHAREEF ne, tana tausaya wa yarinyar, ƙarama da ita amma ta mace a soyayyar namiji, tayar da ita tayi tace, "ta je ta kwanta, sabida ya samu lafiya yanzu ma suna kan hanyar dawowa."
Jin wannan bayanin yasa hankalin Maryamu ya ɗan kwanta, har ta samu ƙwarin gwiwan zuwa ɗaki ta kwanta, tana shiga ta faɗa kan gadon sai barci babu ko addu'a, tunda barcin ne kaɗai a idanunta, burin ta kawai ta samu ta kwanta.
***
_____SHAREEF kuma an basa taimakon gaggawa ne, bayan Likitan ya gama duba sa sai ya fita ya bar Male Nurse a wurin sa after ya ba shi umarnin yin masa wasu allurai da aka kawo masa,
Sannan ya fita zuwa office din sa shi da Dady. A nan yayi masa bayanin, "kar ya damu, ciwon da yake fama dashi ne na ƙoda ya tashi masa, kuma gaskiya abun yana ɗan yin gaba ne ba kamar baya da suke tunanin idan yana shan maganin za a dace ba, don haka da yiwuwar kowanne lokaci za a iya buƙatar yin mishi aiki domin a canza mishi guda ɗaya, tunda ɗayan ya fi lalace wa da yawa, hakan ne yasa ciwon zai riƙa tashi masa at any time."
Dady yace, "ai babu zancen kwantar da hankali kenan, tunda ba ci gaba aka samu ba."
Murmushi Doctor yayi yace, "to ya zamu yi Alhaji, dole ku kwantar da hankalin ku tunda idan ku ka tayar da hankali, shi kansa mara lafiyar zai damu kuma hakan ya zo yayi effected din sa, don haka a yanzu dai baza mu rike ku a asibitin ba, zaku iya tafiya gida sai ya ci gaba da shan magungunan da muka rubuta mishi, one week sai ku dawo daga nan sai a yi maganar aikin, don shi zai fi gaskiya."
"Shikenan, na gode Doctor, ba damuwa, duk abun da ka ce haka zamu yi."
Ya miƙa masa hannu suka gaisa, sannan suka miƙe a tare suka fita suka wuce room ɗin da SHAREEF yake ciki
After an kawo maganin, sai suka riƙe shi suka fito da shi zuwa bakin Mota, duk da jikin nasa da ɗan sauki ba kamar yanda suka kawo shi ba, amma hakan bai sa Dady ya ƙyale shi ba sai da suka riƙe shi har ya shiga Mota,
Sadiq ya ja motar suka wuce gida
Lokacin da suka isa Momy tana nan zaune tana tsimayen su, tana jin ƙaran Mota ta fito da sauri ta nufi wurin su,
Time ɗin har sun fito cikin Motan, da sauri ta ƙarisa tana kallon SHAREEF ɗin har zuciyarta tayi sanyi ganin alamun da sauƙi jikin nasa,
Sai ta amshi maganin da ke hannun Sadiq tana masa sannu,
A haka suka ƙarisa ciki suka zauna a saman sofa
Dady yace, "ta samo masa abinci ya soma ci, sai ya sha waɗanda aka ce ya sha yanzu."
Mike wa tayi ta nufi kitchen ta ɗibo abinci, since ta kwashe komai na saman dining ɗin ta mayar can, a plate ta ɗibo mishi ta kawo, sannan ta ɗauko warm water ta ajiye masa
Dady da ke duban Sadiq, yace mishi, "Sadiq je ka ɗaki ka kwanta tunda dare yayi, ka ga gobe kana da school."
"Nima abun da na gani kenan, gaba ɗaya yau a school ya wuni, tashi Auta ka je ka kwanta."
Tunda shima yana jin barci bai yi gardama ba, sai da safe yayi musu tare da ƙara yin ma SHAREEF sannu da jiki, sannan ya wuce
Momy tace, "ka ci abincin mana ka zauna ka tasa a gaba, ya kamata ka ci kaima ka je ka kwanta ko?"
A hankali ya sanya hannu ya dauki spoon ɗin yana ɗibo abincin, daure wa kawai yake yi sabida yanda ya ga sun damu dashi suna ta lallaɓa shi, haka ya ci abincin kaɗan sannan ya sha maganin,
Har ɗaki suka raka sa; sai da ya kwanta sannan suma suka je suka kwanta.
***
_____Can cikin dare Maryamu na cikin barci ta ji kamar Mutum a jikinta, duk yanda ta so tayi barcinta ta manta da yanda take jin motsin, but ta gaza, saboda yanda ake taɓa mata wasu sassa na jikinta ana mata wani irin wasa da ta kasa jure wa, dole ta buɗe lumsassun idanuwanta masu cike da barci, a hankali take buɗe su har ta ware su a saman fuskar SHAREEF da hasken wata ya haska mata shi, mamaki ne ya kama ta duk da wani irin barci ne ke fizgar ta a lokacin, amma hakan bai sa ta ƙi wartsake idanunta ba; nan take ta sake ƙura masa ido zahiri dai take gani, wani irin doka wa zuciyarta tayi sabida jin ya kai kansa saman ƙirjinta ya manna a wurin, take ta buɗe baki da nufin yin ihu, amma sai ta ji gum ya rufe mata bakin yana ɗago kansa tare da zuba mata jajayen idanunsa da suka ƙara girma suka yi wani irin kala da su,
Mutsu-mutsu ta soma yi tana ƙoƙarin kwace jikinta, domin sai a lokacin ta gama fahimtar babu kaya a jikinta, haka shima, suna cikin blanket ya rufe su,
Duk yanda ta so ta motsa ta ƙwace jikinta ta kasa,
Sai kawai tayi shiru tana jan numfashi yayinda zuciyarta take beating kamar zata faso ƙirjin ta
"Kar ki hana Ni abun da zuciyata take so, na san kina so na da yawa baza ki so na mutu a irin wannan halin da nake ciki ba, Ni Mijinki ne ba ki da hurumin hana Ni kanki, ki bar Ni in yi yanda nake so da ke, idan kina hana Ni kanki mutuwa zan yi, ko kina so in mutu?"
Gum tayi masa sai zuciyarta da ke ci gaba da buga wa, ita har yanzu ganin abun take yi kamar a mafarki, tabbas mafarki take yi SHAREEF bazai zo wurin ta da wannan buƙatar ba
Kamar ya san me take magana a zuciya, sai ya haɗa bakinsa da kunnen ta, tare da furta mata, "na san me kike tunani, ba mafarki bane, zahiri ne, don haka in har kina son in so ki; sai kin taimake ni, ba na son kina min musu, ke Matata ce."
Yana gama furta wa ya haɗe bakin su wuri ɗaya
Abu kamar wasa Maryamu ta kasa gane kanta, ta kasa hana sa abun da yake mata, in fact ma daga lokacin tamkar bata san me ke faruwa ba, idanunta a rufe suke tana jin duk abun da yake yi da ita amma ta kasa motsa wa bare ta hana shi, kuma ta kasa yin kuka, komai yana wakana ne kamar a mafarki, daga baya ma ta dena gane komai bata sake sanin inda take ba sai da gari yayi haske sosai, bata farka ba sai da Momy ta zo ta tashe ta, sannan ta tashi ta ganta babu kaya a jikinta, take komai abun da ya wakana jiya ya dawo mata fil, zahiri ta yarda cewan ba mafarki bane, SHAREEF ne yake bibiyan ta, a fili ta furta, "kenan ya san cewa ita Matarsa ce har yana bibiyan haƙƙin sa?" Maimakon ta ji haushin abun, sai ma farin ciki da ya kama ta, tabbas tana ganin cewa wata rana dole SHAREEF ya ƙaunace ta, tunda har yana iya biyo ta ɗakin ta domin amsar wani abu daga wurin ta, ta tashi da fargaba amma sai ta ji wasai a zuciyarta, tare da jin farin ciki har cikin ƙasan zuciyarta
Da sauri tayi wanka ta shirya sabida tunanin cewa SHAREEF ya ji sauƙi an dawo dashi gida jiya, ta ƙosa tayi tozali dashi,
Koda ta fita falo babu shi, har suka gama breakfast ita da Sadiq zasu tafi amma bata ga SHAREEF ba, shiyasa ta tambayi Momy tace, "Momy ko in je in duba Yaya SHAREEF ne?"
Murmushi Momy tayi tace, "har kin san cewa ya dawo ne ashe? Kin damu da wannan Mijin naki, maza tashi ki je ki gaishe shi sai ku wuce, kin ga time ya kusa ƙure wa za ku yi late."
Farin ciki ne ya cika ta, jiki na rawa ta nufi benen zata haye
Momy ta ɗaga murya tana cewa, "ki yi a hankali don Allah, ba na son wannan rawan jikin naki."
Tana jin Sadiq yana mata dariya, amma bata juya ba sai da ta ganta a bakin ƙofan ɗakin nasa, sannan ta saki ajiyar zuciya tana tunanin wanne abun zata tarar? Har a ranta tana jin tsoron shiga, amma kuma tuna abun da ya faru daren jiya, sai hakan ya bata ƙwarin gwiwa tana murmusawa tare da buɗe ƙofan ta shige ciki
SHAREEF na zaune a saman gadon sa yana tsane jikinsa, cuz fitowar sa kenan daga wanka, yayi domin ya samu ƙwarin jikinsa, duk da Momy ta takura masa ya fito yayi breakfast sai ya sha maganin sa. Yana jin motsi kamar an shigo masa part ɗin, amma ya ji shiru ba a yi magana ba, hakan ne yasa a hankali ya lallaɓa ya miƙe yana nufan ƙaramin falon nasa
Lokacin Maryamu tana tsaye ta kasa shigowa ciki sosai saboda ganin babu kowa, kuma ta ƙi magana sai kallon tsarin falon take yi tana buɗe ƙofofin hancin ta tare da shaƙar ƙamshin SHAREEF da ke ratsa mata har cikin ƙwanya, wani irin daɗi na ratsa ta, har wani lumshe idanu take yi tsaban farin ciki
"Kee."
Muryan SHAREEF ɗin ne ya dawo da ita hayyacinta, firgigit ta dawo da kallonta gare shi, yanda ya tsare ta da kallo babu kaya a jikinsa, da sauri ta kawar da kanta sabida wani irin yanayi da ya riske ta, wani yawu ne mai ƙauri ta haɗiye yayinda ta kasa furta ko kalma ɗaya
"Me ya kawo ki nan? Kin tsaya kamar wata munafuka; ban miki gargaɗin shigo min ɗaki ba? I don't like to see this black face. get out."
Ya daka mata tsawa muryansa alamun a ɓace
Hakan ne yasa ta ɗago manyan idanunta ta zuba mishi, maimakon ta fita kamar yanda yace, sai kawai ta saki wani murmushi wanda sai da dimples ɗin ta suka fito sosai, ya ƙayata kyakkyawar fuskarta, ba komai ne yasa ta yin murmushin ba, sai tuna kamar ba shi ne jiya ya zo wurin ta da buƙatar sa ba, amma yanzu kuma yana ɗaure mata fuska, hakan ne ya bata dariya har ta murmusa tana sake bin jikinsa da kallo kamar zata haɗiye shi
Hakan ne ya fusata SHAREEF, tare da mamakin ganin yanda ta kifa masa manyan idanun nan nata kamar wata mayya kuma tana masa dariya, takowa yayi ya nufo inda take,
Kafin ya ƙariso har ta ruga zata fice cikin ɗakin, amma sai yayi caraf ya cafke ta yana mayar da ƙofan ya rufe, "ke kina da hankali da za ki shigo har ɗaki na kina min dariya? Mene kika gani a jikina da ya ba ki dariyan? Oya tell me ko in kakkarya ki."
"Wlh babu komai Yaya SHAREEF, ba da kai nake yi ba, wani abu na tuna."
Ta furta tana runtse idanunta ganin tayi kusa dashi wadda yasa ta kasa kallonsa
Tura ta yayi yana yatsina fuska, tare da furta, "shashshan banza, fitan min a daki ko in ci ubanki, idan kika sake gigin shigo min ɗaki a karo na uku, sai na canza wa mumun fuskar nan taki kamanni, Oya tashi ki fita mana."
Tashi tayi tana fice wa da sauri kamar ana hankaɗa ta, sai da ta fita sannan ta sauke ajiyar zuciyar tsoro, dantsen hannunta ta kama tana shafa wa, dai-dai wurin da ya kama mata, yayinda take jin wani sanyi da farin ciki a zuciyarta, komai nasa abun kyau ne, kwata-kwata ba ta jin haushin abun da yake mata, a fili ta furta, "ina sonka wlh, koda yanka Ni kake yi haka nan zan jure, domin in rayu da kai, kai kaɗai ne farin cikina a yanzu, Allah zan iya bada raina sabida kai."
Sai ga tagwayen hawaye sun fito daga idanunta sun sauka a saman kuncin ta,
Jin motsi kamar ana taho wa, shiyasa tayi saurin share hawayen; ta nufi hanyar downstairs da saurin ta; tana kaɗa kanta.
[13/02, 10:12 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱
__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE30*
_____Yau ma bayan an tashi daga school, Feena tace ma Maryamu, "ta zo su ajiye ta a hanya."
Sai tace, "a'a baza ta bi su ba, ta san za a zo ɗaukar ta."
Duk yanda Feena ta so ta biyo su but ta ƙi, sai da ta wuce ta shiga Motan, Hunaip ya tambaye ta; take sanar mishi yanda suka yi
Shi da kansa ya sauka ya ƙarisa wurin ta, ya tsaya yana kallonta fuskarsa ɗauke da murmushi yace, "haba friend, ya za a yi mu tafi mu bar ki a nan bayan ba a zo ɗaukar ki ba? Ki zo mu sauke ki tunda mu ba baƙi bane a wurin ki."
Ɗago kai tayi ta ɗan kalle sa kaɗan tana dauke idanunta a kansa, sai ta haɗe fuska da cewa, "gaskiya bazan bi ku ba tunda jiya an min faɗa, ku tafi kawai za a zo ɗauka ta, Momy sai da tayi min gargaɗi za a aiko driver."
Murmushi yayi jin zancen nata, yana ɗan shafa gemun sa a yanzu yake kallonta cike da burge wa, komai nata mai kyau ne har yanda take maganar tana yatsina fuska alamun tsiwa a tattare da ita, tsab ya ƙare wa halittar ta kallo yana jin a ransa gaskiya ya samu Mata, yarinyar tayi masa duk da ƙarama ce sosai, amma har a ransa ta kwanta masa, shiyasa ya ɗan ƙara kwantar da murya tare da furta, "don Allah kar ki yi min katanga ga hana Ni taimakon tsaleliyar budurwa kamar ki, haba taya ma zan bar ki a nan wurin in tafi? Please ki taimaka ki biyo mu tunda har yanzu drivern bai ƙariso ba, Ni zan shiga da kaina in yi wa Momyn bayani tunda na san bata fahimci motan da kika hau bane."
Yanda yake mata maganar raɗa-raɗa cikin kwantar da murya, da kuma jin abun da yace, shiyasa ta sake kallonsa kaɗan tana dauke idonta, ba wai don ta yarda da maganar nasa bane, sai don ganin girmansa da tayi, kuma ga shi sai wani lallaɓa ta yake yi da wasu kalaman da ta kasa gane musu, baza ta iya masa musu ba tunda babban Mutum ne, shiyasa ta gyaɗa kanta alamun ta amince
"Yauwa ko ke fa, har na ji sanyi a raina, mu je in bude miki ƙofan."
Ya nuna mata hanya alamun ta wuce
Babu musu tayi gaba duk da har ranta tana mamakin yanda yake nuna mata a yanzun ɗin, musamman yanda ya saki jikinsa har yana mata murmushi, bata dai kawo komai a ranta ba ta shiga Motan bayan ya buɗe mata