zamu yi, don haka mu fuskanci abun da ke gaban mu zai fi mana." Sai ya ɗago computern sa da ke hannunsa yana cewa, "Ni yanzu na riga da na fitar da sumfurin building na komai, sai a duba a gani in akwai wata shawara."
Sai ya ajiye computern a gaban SHAREEF yana matso mishi dashi yanda zai gani
Kallo ɗaya SHAREEF ya yi wa fuskar computern yana ɗauke idanunsa; da suka rage haske saboda halin da yake ciki, har yanzu a hassale yake da ɓacin ran su Honourable Ja'e, shiyasa cike da taƙama irin nasa, and kuma cikin sanyin muryansa wacce ko a ɓacin rai yake ba ta sauya wa, sai ma dai ta ƙara sanyi sabida isa da izza ta yanda yake sarrafa ta kamar bazai yi ba, a yatsine yace, "ba na buƙatar wannan zanen, already mun yi magana da Hanif shi zai fitar, abun da nake so da ku." Sai ya ɗago kai ya tsira wa Sharaihun ido yana ƙara wa da faɗin, "kai da Mahmud da PA zaku fara zuwa ku ɗauko mana hotunan wurin gobe, da komai na tsarin wurin." Sai ya janye idanunsa tare da matsar da computern Sharaihun yana ɗaura nasa a wurin, tare da soma daddanna wa ba tare da ya sake ce musu komai ba
While Shuraihu duk yanda ya so ya ɓoye abun da ke ransa ya kasa, ransa suya yake yi da jin hukuncin da SHAREEF ya yanke, wanda har hakan ya bayyana a kan fuskarsa batare da ya sani ba, sai ya kasa haƙura yace, "but sir, na ga Ni nake yin zane idan irin hakan ta kasance, and kuma already na rigada na fitar da zanen tunda sun bamu jadawalin wurin, wannan babban aiki ne fa, idan muka ce zamu fara amfani da sabon zane a hannun wanda bai taɓa yi ba akwai matsala..."
"To and so what? Hanif zai yi wannan zanen ba na son gardama." Yayi maganar bai ɗago da kansa ba yana ci gaba da danne-dannen shi
Shi kuma Sharaihu sai ya haɗiye yawun takaici yana ƙoƙarin danne baƙin cikin sa daga fuskarsa, musamman yanda ya ga PA yana kallonsa
Wanda shi PA ya san dama za a rina, don ba a yi wa SHAREEF gwanin ta, shi dama haushin Sharaihu yake ji yanda yake kane-kane a companin don an ba shi dama, amma ga shi lokaci guda abun mamaki SHAREEF yana son daƙile shi a kan wasu harkokin
"Wannan shi ne sumfurin zanen da Hanif ya tura min, zan tura maka ta e-mail sai ku je dashi ku duba, and ga wanda Mr. Pitter ya tura min." Sai ya ɗan yi shiru yana jan numfashi kaɗan, tare da furta, "make sure today you all check and send me again."
Dukkan su suka amsa mishi, while Shuraihu yana dauke nasa computern tare da duba zanen da SHAREEF ya tura mishi, sai ya miƙe tsaye yana mishi sallama ya fice
"Ka je ka tattaro min files ɗin nan na sabbin ma'aikata, ka kai ma Mahmud ya duba a tantance waɗanda za a ɗauka, kar su gaza mutane biyar."
"Ok sir." Cewar PA cike da girmamawa yana tashi, sannan ya fice daga office din
Shi kuma SHAREEF sai ya ci gaba da latsa computern sa bai sake ɗago kai ba. Like a ten minutes ya ɗauki wayansa yana latsa wa, jima wa kaɗan ya kara a kunnen sa tare da manna wayan da wuyan sa still yana duba computern
Daga can Hanif ya amsa call ɗin yana cewa, "Bro how fer?"
"Fine. And you?"
"Alhamdulillah komai normal."
"Ok, mun gama magana a kan aikin nan nasu Mr. Pitter, zan tura maka iya girman wajen, but zuwa gobe za a sake zuwa a ɗauka gaba ɗaya zan tura maka, sai ka duba Please Do everything for us in one week, everything will be ready."
"Wow! Masha Allah. Did you say that everything is finished? They agreed to give you the shares?"
"Yeah, sai dai waɗannan ƙananun mutanen suna son kawo min cikas, and babu wanda zan raga mishi ciki wlh muddin suka ce zasu taɓa Ni."
Murmushi Hanif yayi tare da cewa, "wooh! Na Haseena, ba da kanka a sare ka je gida ka ce ya faɗi, calm down mana, me zai sa ranka ya ɓaci a kan su?"
Murmushi SHAREEF yayi yana cije laɓɓansa, sai ya ɗan ja numfashi tare da rufe computern, at the time yana ba shi amsa da cewan, "har ka sa zuciyata tayi sanyi, but raina a sama yake tunda muka fito meeting ɗin nan." Sai ya ɗan ja guntun tsaki tare da cewa, "bari in wuce gida, zamu yi waya idan na koma, ina jin yunwa sosai." Ya ƙare maganar yana langaɓe kai kamar zai yi kuka
Hanif da ke murmusawan shima yace, "Ok bro, bari in bar ka nima ina son shiga school now. And stop worrying about these people, since everything is in our hands. Congratulations, fatan nasaran aiki."
SHAREEF smiled and said, "Thank you my brother."
Daga nan suka yi sallama ya katse wayan yana tashi tsaye. Jakarsa ya ɗauka bayan ya mayar da wasu files a ciki, sannan ya nufi ƙofa ya fice yana zura wayansa a cikin aljihun wandon sa. Babu PA a office nasa, shiyasa ya fice kawai yana nufan lifter ya shiga ya saukar dashi ƙasa
Duk inda ya wuce ma'aikata ke gaishe shi, amma ko ci kanku bai ce musu ba. Idan ma da sabo sun saba, ba ya amsa gaisuwar su sai ya ga dama, ko zai amsa sai dai ya ɗaga musu hannu, sosai girman kanshi ya yi yawa da ganin mutane a ƙasƙance, ba ya damuwa da damuwar mutane sai nashi, ba ruwan shi da shiga harkan mutane bare ya san matsalar su, in dai sun yi mishi ba dai-dai bane ko kuma sun shiga gonan shi, yanzu za ka ji ruwan bala'i da masifa, kuma daga ƙarshe ya yi maka koran wulaƙanci; don ba ya iya ba wa mutum dama ta biyu
Motansa ya hau ya figa zuwa gida, a ɗan ƙanƙanin lokaci ya isa gida ya dinga danna horn kamar zai tashi sama
Da sauri mai gadi ya wangale mishi gate ɗin jikinsa yana rawa. Shi kuma ya kutsa motan ciki ya nufi packing space. Tsayar da Motan yayi ya fito hannunsa rike da Jakar sa, tare da nufan cikin gidan yana zura hannunsa ɗaya a aljihu, tare da taka wa a hankali tamkar ƙwai ya fashe mishi kansa a ƙasa
Lokacin su Momy dawowarsu kenan daga Market. Shi yasa ta tasa Maryamu suka shiga kichen domin su haɗa lunch
Maryamu sai farin ciki take yi tana wani rawan kai, yau ga ta a kichen ɗin ƴan gayu zata yi girki, kamar ba ita ce wacce ko tsinke aka saka ta ta kawar a gida; ta dinga ƙunƙunai kenan kamar zata bigi Mutum. Amma yanzu daga Momy ta ce, "ta taso su je kichen." Da gudunta da rawan jiki ta bi ta tana taya ta sai hira take mata. Ita kuma tana mata murmushi da sauraron ta
Jin an buɗe ƙofan shigowa, shiyasa Momy ta kalli Maryamu tace, "duba ki gani wane ne? Na ji shigowar Mota maybe Sadiq ne ya dawo."
"To Momy." Maryamu ta amsa mata da sauri tana share hannunta a kayanta, tare da nufan ƙofan ta fice kamar ana ingiza ta.
[25/01, 8:45 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱
*HIRA MAI DADI TSAKANIN NANA A’ISHA (RA) DA MANZON ALLAH (SAW).*
Wata rana Nana A’isha {r.a} suna zaune da Manzon Allah {s.a.w} ta kura masa ido tana kallonsa, can sai tace, "ya Rasulillahi wai don Allah ya ya wannan yusif din yake? aka ce Mata saboda tsaban kyansa idan sun ganshi har yanka hannayensu suke??"
Sai Manzon Allah {s.a.w} ya bude tafin hannunsa mai albarka, ya nuna mata fuskar Annabi Yusif yace mata, "ga Yusif din," sai Nana A’isha tayi murmushi tace, "wani abu sai Mata. Inama baku yanka hannayenku ba kuzo kuga shugaban kyawawa," ta ƙara da cewa, "ya Rasulillahi {s.a.w} tafin hannunnan naka yafi fuskar Annabi Yusif din kyau".
Ya Allah ka sada fuskokinmu da ta shugaban kyawawa Annabi Muhammad Sallallaahu'alaihi Wasallama. Amin.
__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE15*
Lokacin da Maryamu ta fita Falo, har SHAREEF ya soma hawa matattaƙalan benen, shiyasa ta koma da sauri tana ce ma Momy, "Yaya SHAREEF ne ya dawo."
"SHAREEF kuma? A wannan lokacin?" Sai kuma ta zazzage maggin da ta gama ɓare wa a cikin miyan, tana ɗan juya wa kaɗan tare da cewa, "taho nan ki juya min miyan ina zuwa, ki yi a hankali fa kar ya tsillan miki a idanu."
"To Momy."
Ta sakar mata ludayin tana fice wa. Kai tsaye saman itama ta haura sabida ganin babu SHAREEF. A hanya suka ci karo ya fito daga ɗakin ta shima
Sai yace, "Momy."
Tana kallonsa tace, "ya aka yi ka dawo kuma yanzu?"
"Mom na gama abun da nake yi ne, na dawo na karya ne sai na koma zuwa anjima."
"Ai ba ka jin magana ne SHAREEF, yanzu da ka karya ai baza ka sake wahalar dawowa ba kuma. We have now entered the house, da baka ganmu ba ai." Sai ta juya tana cewa, "bari in haɗa maka ko kunun gyaɗa ne ka sha since muna da ƙullun."
Sai ta sauka ƙasa ta koma kichen
Shi kuma sai ya shiga ɗakin sa ya rage kayan jikinsa, ƙaramar t.shirt ya saka sai wando three quarter, dukka kalan ruwan zuma, da suka yi masa kyau matuƙa suka sake fitar mishi da haibar sa da kamalan sa. Wayansa ya zura a aljihu sai ya ɗauki maganin sa ya fice. Direct falo ya nufa ya wuce bakin fridge, ya buɗe ya ɗauki ruwa tare da kora wa da maganin, sai da ya haɗiye sannan ya ɗan lumshe ido yana buɗe wa, ya nufi hanyar kichen ɗin a natse tare da zaro wayansa a aljihu yana duba wa; jin ƙaran messages na shigo wa
Ƙamshin turaren sa ne ya soma sauka a hancin Maryamu, da sauri ta juya kai suka haɗa idanu lokaci guda. Ware idanunta tayi a kansa yayinda zuciyarta ta shiga wani irin zillo gami da sanyin da ke ratsa ta lokaci guda; ga wani farin ciki da ya mamaye mata zuciya sabida arba da tayi da kyakkyawar fuskarsa
Shi kuma yatsina fuska yayi, lokaci guda ya ɗauke idanunsa a kanta sabida ko kusa ba ya ƙaunar suna haɗa ido, ganin yanda idanunta suke da girma tamkar na mahaifiyarsa, yanda take kifa masa idon shiyasa lokaci guda yake jin tsanarta na mamaye mishi zuciya, gami da haushin ta a cikin rai, amma girman kai da izza irin nasa bazai bari yayi mata magana a kan yanda take bin sa da kallo kamar ta samu TV ba. "Mom. Ba a gama ba?" Yayi furucin yana mayar da idanunsa a kan Momy da ke ta faman haɗa masa kunun
"Eh ban gama ba SHAREEF, ka jira kaɗan yanzu zan gama, sai in soya maka ko ƙwai biyu ne ka ci dashi, and ga arish ma."
"No, kunun ya wadatar Mom, zan sha haka nan."
"Ok. Go and I will send Maryam to bring you to the living room."
"Kin san ba na son masu aiki suna taɓa abun da zan ci Mom. I hate dirty girls."
Sai lokacin Momy ta juya tana kallonsa. She said in surprise, "Is this your sister? Ita ba ƴar aiki bace."
"What is their difference? Dukkan su ƙazamai ne, and bazan iya cin abun hannunta ba, idan kin gama zan zo in amsa." Yayi maganar cikin ko'in kula da rashin damuwa, ya juya yana fice wa tare da kara wayansa a kunnen sa
While Momy ta bi shi da kallo kamar an datse mata baki, sai kuma ta dubi Maryamu da tayi tsimi a wurin tana kallon SHAREEF ɗin kamar zata haɗiye shi, ita kawai bakin sa take kallo da yanda kumatun sa suke lotsa wa irin nata gaba ɗaya ta gama shagala da kallon sa. Momy ta taɓa ta tana cewa, "Maryam. Tunanin me kike yi haka? Ai ya tafi ko?"
Kunya ne ya kama ta, tayi saurin rufe idon ta da hannayenta biyu, tare da cewa, "Momy wlh ba shi nake kallo ba."
Dariya Momy tayi, sai ta girgiza kanta tana cewa, "bari in gama ki kai mishi kunun nan, and ki dena zuba mishi ido irin haka don ba ya son kallo kinji Ni?
Kai Maryamu ta gyaɗa mata itama tana kallonta, yayinda ta mayar da hankalin ta a kan yanda Momyn take haɗa kunun, bata ce komai ba har ta gama ta zuba mata a cup, tare da ɗaura mata a plate ta miƙa mata. Sai ta amsa ta nufi ƙofa da sauri kamar zata kifa
Mom ta kira ta tana cewa, "ya ki Maryam."
Dawowa tayi tana kallonta
"Ki dena tafiya irin haka, kiyi a hankali kar ki je ki zubar."
"To Momy." Sai ta juya ta fita tana sanja takun tafiyan nata
Momy ta bi ta da murmushi har ta fice, "lallai akwai aiki a gabana, SHAREEF yana da matsala fa." Sai ta ja numfashi tana ci gaba da aikin ta
While Maryamu ganin babu SHAREEF a falo, sai ta dawo tace ma Momyn, "babu shi."
Momy tace, "to ya koma daki kenan, ki hau sama za ki ga ƙofofi uku a jere, idan kin wuce su akwai lungu da bene a wurin, to ƙofan da ke wurin nan za ki buɗe ki shiga, yi sauri kar ya gaji da jira."
Fita Maryamun tayi ta nufi upstairs kamar yanda Momy tayi mata kwatance. Ɗakin ta tura ko sallama ta shige ciki
SHAREEF na kwance a kan gado yana waya da Haseena, sai kashe murya yake yi idanunsa a lumshe, ya ji kamar motsi shiyasa ya buɗe idanun yana zuba su a kan Maryamu da ta shigo masa ɗaki. Da sauri ya miƙe zaune cikin tsawa yace, "Who brought you to this room, who gave you permission to enter my room da waɗannan kazantattun kafafun naki? Kee!.
Rawa jikin Maryamu ya soma yi sabida tsawan da ya daka mata, kasancewar bata saba da jin irin wannan tsawan ba nan da nan ta rikice tana sakin plate ɗin hannun ta
"What...!" Ya furta cikin zaro idanu waje sabida ganin aika-aikan da tayi mishi
Daga cikin wayan Haseena da take jin maganar SHAREEF ɗin, sai ta soma tambayarsa tana cewa, "dear lafiya wai?"
Da sauri ya katse wayan yana miƙe wa kamar ƙiftawar ido ya isa inda Maryamu ke ƙoƙarin guduwa. Sai ji tayi ya cafko ta ta dawo baya ta faɗi dirshan a ƙasa. "Dan ubanki uban wa ya ba ki damar shigo min ɗaki har kika zubar min da wannan abun a ɗaki? Ke Jakar ina ce wa ya ba ki permission shigo min ɗaki?"
"Momy ce... Momy." Tayi maganar cikin rawan baki sabida gaba ɗaya ta gama ruɗewa ganin yanda ya hayayyaƙo mata da alamun a fusace yake, lokaci ɗaya tsoron sa ya ɗarsu a ranta musamman da ta ganshi a gabanta
Cikin baƙin ciki da takaicin yanda take kallonsa, ya saka hannu ya jawo ta yana kifa mata kyakkyawar mari a face ɗin ta
Lokaci ɗaya ta yanka uban ihu tana kururuwa kamar zata tsaga mishi kunne
A take ya sake ta shima sabida yanda ƙaran ya doɗe mishi kunne. Ganin yanda take ihu sai ya daka mata tsawa yace, "ki yi min shiru ko in kakkarya ki a nan wurin, I said to shut up or I will kill you."
Yayi maganar yana ɗaga hannayensa kamar zai shaƙe ta don Jaraba
Lokaci guda ta shanye kukan nata tana kama bakinta cikin rawan jiki, tare da matso hawayen da suka kasa fitowa daga cikin idon nata, sai dai sun cika idanun har sun soma sauya kala alamun ta ji shigan marin
Huci kawai yake yi tsaban takaici da tsananin tsanar ta, ya kasa ma ce mata komai sabida yanda ya ga ta ƙi kawar da idanunta a kansa kamar wacce zata haɗiye shi duk da tsoratan da tayi dashi. Cije laɓɓan sa yayi yana jan numfashi cike da ɓacin ran da ke ƙara kunno mishi, sai ya dubi inda ta zubar mishi da kunun ransa sai ƙara suya yake yi. Nuna wurin yayi da yatsa yace, "Get up quickly and clear the place for me; ko in kashe ki a nan wajen, maza tashi."
Da sauri ta rarrafa wurin tana rawan jiki, ta soma ƙoƙarin ɗauke cup ɗin, hannayenta biyu ta saka tana kwalɓe kunun tana mayar wa a cup ɗin
Yayinda shi kuma yake bin ta da kallon ƙasƙanci yana sake jin ransa na ƙara baƙi, ji yake yi tamkar ya je ya mangare ta, amma sai ya ɗauke kansa yana nufan wurin wayansa da ke ta faman ruri, zama yayi yana mayar da ajiyan zuciya tare da sassauta yanayin sa. Ya ɗauki wayan yana kara wa a kunne
"Dear me ke faruwa ne? Kai da wace ce haka?"
Ɗan jan numfashi yayi yana lumshe idanunsa tare da shafa gefen kumatun sa, a hankali cike da sanyin muryansa yace, "Ni da wata Jaka ce ƴar ƙauye, ta zo tayi min ɓarna a daki."
"What...! A ɗaki kuma dear? Meye haɗin ka da ita da zata zo maka ɗaki?"
Ido ya buɗe yana kallon wurin da Maryamu take, tana ta faman kwalɓe kunun da hannu cikin rawan jiki. Ƙin magana yayi sai da ta sake tambayarsa, sai yace, "sweetheart ki share maganar nan raina ɓaci yake yi."
A fusace Haseena tace, "taya zan share maganar after telling me you are in the same room with another woman? I can't."
"Calm down mana sweetheart, wata ƴar aiki ce Mom ta aiko ta kawo min kunu, and shi ne ta zubar min a ɗaki."
Haseena cike da kishi tace, "You know I'm jealous, I don't want you to be in the same place as any other woman dear, ba na son ka ci amanata."
"Oh! Sweetheart meyasa kin cika rigima ne? Akwai wata Mace da nake so bayan ke ce? Ba a haife ta ba har yanzu, idan kina duniya babu wata wacce ta isa in kalle ta, put in your heart I am yours forever. I love you so much!" Sai ya sakar mata kissing yana lumshe idanunsa
Yayinda a wannan lokacin Maryamu kamar zuciyarta zata fashe don baƙin ciki, tsaya wa tayi ta kasa ƙarisa abun da take yi tana