x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 38 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 111001 words
  • 114000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 404

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
su zuwa kan sofa, bayan sun zauna sai itama ta zauna a gefen Amina; while Feena na kan one seater da ke facing nasu, tace, "alhamdulillah ai Ni yanzu garau nake ji na, kwanan nan zan dawo school."

"Ai kuwa yakamata, domin next week exams." In ji Amina tana ƴar murmusawa

Feena kuma tace, "ina Momy ne? Gidan shiru kamar ke kaɗai?"

"Momy tana sama yanzu ta haura, a kichen ma take shine ta shiga ɗaki yanzu, mu kenan mu biyu, su Yaya Sadiq ba sa nan tun shekaran jiya, sun je wurin Yaya Hanif."

"Wai ya gama karatun sa ne? Na ji Mamana tana maganar da Abba kamar ya gama, haka dai na ji suna tad'i." Feena ta furta tana kallonta

Ita kuma Maryamu ta bata tabbacin ya gama, sannan ta miƙe tana ɗauko musu ruwa da drinks a tray ta kawo musu, sai ta wuce kiran Momy a sama

Har Amina tana cewa, "da ta bari kawai sai ta sauko, sabida ƙafanta kar su wahalar da ita."

Bata ce musu komai ba ta wuce tana dariya

Su kuma suka bi ta da kallon tausayi, gaba ɗaya ta sauya musu duk ta zabge na ban mamaki, har sanyin hali ta koya, sai idanunta da suka fito waje kamar zasu faɗo, haka ma wuyan ta duk ƙashin wuya ya bayyana alamun ta rame ba kaɗan ba, tunda Maryamu Allah ya bata jikin Mata; bata da cika sosai amma babu rama a jikinta ko kaɗan, kuɓul-kuɓul take,
Koda ta tafi ma maganar ta suke yi har sai sanda suka ji motsin saukowan su

Tare suka dawo da Momy,
Momy da fara'a take cewa, "ah ah! Su Nafisa ne a gidan ashe?"

"Eh Momy, ina yini?"

"Lafiya lau. Ya su Maman naki?"

"Lafiya ƙalau Momy, suna gaishe ki."

Itama Aminan gaishe ta tayi cikin girmamawa tana ƙoƙarin ajiye ruwan da take sha

Ta amsa cike da fara'a tana tambayarta itama mutanen gida?

"Alhamdulillah Momy."

"Masha Allah! Haka ake so."
Sai ta miƙe tace, "tana zuwa."
Ta wuce kichen,
Babu jimawa ta ƙwala wa Maryamu kira,
Bayan ta je ta miƙa mata abincin da ta zuba musu tace, "takai musu."

Tana kaimusu ta ajiye tana cewa, "wai yanzu dole zan koma school ranan Monday kenan? Ni da bana zuwa ban san ma me aka yi ba?"

Feena tace, "haka ne kam, ga shi duk an yi Tests babu wanda kika samu sai na maths guda ɗaya, shi har three tests yayi mana, amma kar ki damu sai in yi wa Abbana magana tunda rashin lafiya ne, na san zai samu Principle da maganar komai zai wuce. Kodayake Dady ma ai zai yi wa Abban magana da kansa."

"Ai insha Allahu bata da matsala tunda komai hanya ne, bare kuma rashin lafiya ne kika yi, but ranan Mondayn za ki zo ko?" In ji Amina tana kallonta

Maryamu tace, "insha Allahu zan zo, ai na ji sauki sosai, tunda ina tafiyana ko'ina zan iya zuwa."

Daga nan hiran su suka ci gaba da yi duk na school ɗin, suna bata shawaran yanda zata yi karatu kafin ranan Litinin,
Feena tace, "zata kawo mata books ɗin ta sai tayi copying wasu abubuwan."

Momy kuma nata aikace-aikacen ta a kitchen tana jiyo hiran su but bata ce musu komai ba, har ta gama ta wuce ɗaki ta bar su a nan duk sun shantake kowacce ta cire hijabi sun zauna a ƙasa suna cin abincin har Maryamu; suna labarai da dararraku

A haka Dady ya dawo shima ya tarar da su, suka gaishe shi cikin girmamawa, ya amsa su da fara'a yana tambayar su iyayensu?
Har yana ɗan zolayan su suna ta dariya,
Daga baya sai ya wuce ɗakin sa; a can Momy takai masa abincin sa

After an kira sallan la'asar sai suka wuce ɗakin Maryamu suka yi sallan a can suka dawo,
Suna zama suka ji sallaman su Sadiq, domin har Driver ya je ya dauko su a airport,
Da drivern da Sadiq suka ɗauko wasu jakunkunan Hanif, suna gaba while Hanif da SHAREEF suna bayan su sun jero a tare kamar tagwaye domin basu da bambanci komai nasu iri ɗaya ne, har t.shirt ɗin jikinsu da suka saka fari, wando kuma na SHAREEF blue ne; na Hanif baƙi

Su Feena tuni sun gyara zaman su kowacce ta natsu suna ɗan bin su da kallo

Momy da ke sauko wa daga kan bene fuskarta dauke da farin ciki tana yi wa Hanif ɗin lale marhaban

Direct wurin ta ya nufa yana dariya tare da rungume ta yana cewa, "Momyna I'm back."

"Yr welcome Son, kun sha hanya."

"Wlh kuwa Momy, ina wuni na same ku lafiya?"

Tana shafa kansa ta amsa before ta riƙe masa hannu suka isa cikin falon tana kallon su SHAREEF da ke tsaye basu zauna ba,
While driver har ya fice ma tunda ya ajiye Jakunkunan hannunsa,
Shima Sadiq wurin Momyn ya nufa yana rungume ta

Sai lokacin su Feena suka buɗe baki suna gaishe su,
Hanif da ke kallonsu yana murmusawa, shi kaɗai ya amsa su yana nufo su tare da furta, "my sister, babu Oyoyo baza ki taso ki rungume Ni ba?"
Ya ƙare maganar yana kallon Maryamu da hankalin ta ke a kan SHAREEF duk ya tafi da wani natsuwar ta, zuciyarta sai buga wa take yi, ba ƙaramin sanyi da farin ciki taji a cikin zuciyarta ba saboda arba da tayi dashi

But shi gogan bai san ma tana yi ba, don tunda yayi musu kallo ɗaya ya mayar da kansa saman waya, dalilin da yasa bai zauna ba kenan yana duba abu a wayansa

Jin abun da Hanif yace, shi ne dalilin tasowar ta cikin farin cikinta ta nufe sa yayi hug nata, "sannu da zuwa Yaya."
Ta furta tana washe baki

"Yauwa our ƙanwa, ashe haka kike da kyau fiye da a waya? Sadiq bai ɗaukar min ke da kyau ba, Mom ƙanwar mu ashe Babbar Mace ce, ai a waya nayi tunanin ƴar ƙarama ce cuz ganin wannan cute baby face ɗin nata."

Dariya suka yi daga su Momy har su Amina da ke zaune a ƙasa basu tashi ba suna kallon su

Momy tace masa, "dama ai Autana Babbar Mace ce, don ma tayi ciwo ta zabge; amma tubarakallah Masha Allah ƙin kowa ƙin wanda ya rasa, yanzu ku zauna bari in kawo muku ruwa ku sha."

Sai lokacin SHAREEF ya ɗago kansa yana sauke wa a kan Momy tare da furta, "Mom Ni ba ki yi min komai ba, su kawai kika yi kewa kenan?"

Wani harara ta narka masa, bata kai ga yin magana ba Dady ya fito yana musu magana,
Hakan ne yasa bata ce komai ba ta wuce kitchen

Dukkan su suka nufe sa suka rungume sa,
Daga bisani ya kama hannun Hanif suka zo har kan sofa suka zauna a tare yana masa congratulations

Momy lokacin ta kawo musu ruwan, sai ta zuba wa Hanif kaɗai ta miƙa masa

Ganin haka ne yasa Sadiq ya dauka ya zuba yana sha tunda ishi yake ji

While SHAREEF kuma sai ya haɗe fuska har yanzu yana a tsayen ya ƙi zama, sai kawai ya juya ya nufi saman benen bai sake cewa komai ba

Maryamu ce kawai ta bi sa da kallo kamar zata zilalar da yawu, tana jin wani irin ƙaunarsa na ƙara mamaye mata zuciya, shi kaɗai take ganin kyawun sa a wurin, farar fuskarsa ta fi komai saka ta nishaɗi

Su Feena da suka kula da ita, suna ganin irin kallon da take yi wa SHAREEF ɗin, abun ya basu mamaki duk da su ma kallonsa ɗin suke yi, musamman ma Amina wacce bata sanshi ba, ita gani take yi kamar ƴan biyu ne da Hanif, baza ta tantance wanda ya fi kyau a cikin su ukun ba, sai dai SHAREEF ya fi kwarjini ne da ɗaukar ido sabida hasken sa mai kyau da dimples ɗin sa da ke bayyana in yayi magana, hakan ke jawo hankalin mutane gare shi; ba ƙaramin kyau yake ƙara masa da haiba ba, sai kuma sassanyar muryan sa ko magana yayi sai ka juya ka kalle sa,
But a zahiri Sadiq ya fi su kyau tunda shi yana da manyan idanuwa masu haske; kuma yana da ɗan fara'a a fuska,
Bata taɓa ganin waɗanda suka bata sha'awa irin waɗannan samarin ba, daga ita har Feena sun kasa sakin jikin su sabida ganin Samarin; kowacce tana jin kunya duk sun takure, ga shi Hanif sai jansu yake yi da hira kamar ya daɗe da sanin su, amma kunya ya hana su zama, dole suka yi musu sallama suka ce zasu tafi

Momy tace, "su je su yi wa Driver magana sai ya kaisu gida."

Tare da Maryamu suka fita har haraban gidan, sai da ta ga tafiyan su sannan ta ɗingisa ƙafa ta dawo ciki,
A wurin Hanif ta zauna suna hira a tare suna ta dariya gaba ɗaya,
Amma ban da SHAREEF don ya ƙi fitowa yana can ɗaki,
Sai da aka kira sallan magriba sannan ya fito suka haɗu da su Hanif suka wuce masallaci

Sai bayan sallan isha'i suka dawo gidan, dukkan su a saman Dinnig suka zauna a tare suka ci abinci yau,
Bayan an gama suka dawo suka ɗan taɓa hira kaɗan,
Shi Hanif tuni ya wuce daki tunda akwai gajiya a jikinsa, sai da ya ɗan jima da shigewa before SHAREEF ya bi bayansa

Dady yace, "kai Sadiq baza ka je ka kwanta bane; ka huce gajiyar?"

"No Dady ba na jin barci, ina nan tare da ku muyi hiran mu, ban jin gajiyar komai."

Murmushi Dady yayi

Ita kuma Momy tace, "mu ma ai ba jima wa zamu yi ba yanzu zamu kwanta, hiran ya isa haka."

"Ita dai daughter tuni tayi barcin ta ta huta, saura mu." Inji Dady yana ɗan muskuta zaman sa

Momy tace, "ai tun ɗazu nake kula da ita tana ta hamma, ban ma farga ba ashe har tayi barcin? Sadiq ko zaka kaita ɗaki?"

Ɗan waro ido yayi yace, "kai Momy wlh bazan iya ba, kina ganin ta nan wasa-wasa nauyi ne da ita."
Sai ya miƙe da ɗan kuzarin sa yana cewa, "nima dai na tafi, bari in je ɗaki in duba books ɗina, good night Mom, Dad."

Sai da ya tafi sannan Momy ta ɗauke ta takaita ɗaki, suka wuce su ma ɗakunan su suka kwanta

A washe gari sai ga su Aunty Najwa da Aunty Zainab sun zo yi wa Hanif murnan kammala karatu,
Dayake Aunty Najwa ita ta taɓa zuwa sau ɗaya time ɗin Maryamu bata da lafiya Momy ta faɗa mata, har ta zo musamman ta gaishe ta,
Aunty Zainab ce bata santa ba, bayan ta ganta take cewa, "kai yarinyar ga ta kyakkyawa kuwa Khadijah, Allah ta shiga raina, anya bazan yi wa Habeeb kamu ba kawai a yi dashi?"

A lokacin Maryamu tana wurin, dariya kawai tayi bata ce komai ba

Bayan tabar wurin ne; Aunty Najwa take cewa, "wannan tuzurun? Ai tayi mishi ƙanƙanta wlh, me ma zata yi dashi? Yarinya ƴar ƙarama da ita beauty a cuce ta."

Aunty Zainab ta ɓata fuska tace, "kai Aunty Najwa gaskiya ban son haka, ina laifin don na ce a haɗa su? Wlh na ga dacewar su Allah ba wasa nake yi ba."

Sai lokacin Momy take cewa, "ai kwanan nan ma zata wuce wurin Surayyya; a can zata ci gaba da karatun ta."

"Haba dai? To sabida me? Bayan ke ma kina buƙatar yarinyar; ke da kike son ƴaƴa mata sai ki bar ta ta koma can?"
Inji Aunty Najwa tana kallon ta

Sai Momy ta ja numfashi; tare da zayyane musu ainihin abun da ke faruwa na auren su da SHAREEF

"Ikon Allah! Wai kina nufin abun nan ya faru amma ba ki sanar mana ba Khadija?" Inji Aunty Zainab tana ɗan ware ido a kanta

"Kuyi haƙuri, na so faɗa muku amma ba yanzu ba, dalili kuwa ita kanta yarinyar bamu so ta tare a ɗakin ta ba tunda kunga yarinya ce, sannan ba ma son ma SHAREEF ya sani a time ɗin, amma yanzu komai ya fito fili har ya nuna ra'ayin ba ya ƙaunar ta sai wata yarinya da ya kawo, gaba ɗaya hankalin mu bai kwanta da ita ba; amma ganin take-taken shi nema yake yi ya bijire mana a kanta shiyasa kawai muka amince, Ni kuma ba na son Maryam ta tare a yanzu ba tare da ta mallaki hankalin kanta ba, tunda SHAREEF ba ya ƙaunar yarinyar sai fama muke yi dashi, idan ta tare akwai cutuwa a wurin ta, kun san halin sa shiyasa nake son tayi nesa da mu ta je tayi karatunta ta samu wayewa ta yanda zata mayar masa da martanin duk abun da yayi mata, ba na son ya cuce ta bare mu mu tauye mata haƙƙin ta."

Aunty Najwa tace, "dama wannan Yaron yana yi da wasu ƙananun idanu ai ba mutunci ne dashi ba, SHAREEF bai da kirki ga shegen jin kai da wulaƙanci, wlh dole zata sha wahala, gwara da kika ɗauki wannan matakin, ba don Ni a nan nake ba ai da na ɗauke ta ta dawo wuri na."

Aunty Zainab ta karɓe zancen tana cewa, "bare Ni da ta fi shiga raina, gudun kawai matsala ne tunda ta zama Matarsa shiyasa bazan ɗauke ta ba, amma da babu igiyar kowa a kanta wlh Yarona zan yi wa kamu tunda shi ba ya so; ai mu muna so ato."

Momy murmushi tayi tace, "shine mu ma abun da ke damun mu, kuma ba ma son raba auren amma da mun haɗa su da Hanif, shi ya fi shi sauƙin kai bazai taɓa bijire mana ba, amma yarinyar itama tana sonshi shine matsalar, shiyasa take bani tausayi wlh, hakan ne yasa muka yi magana da Surayya nace zan kaita can, da mun so sai an yi hutu sai mu kaita ta soma zuwa makarantar, amma tace mu kawo ta kawai yanzu tunda Jarabawa ya rage musu ranan Alhamis zasu fara; sai a kawo ta zata san yanda zata yi ko jarabawar sai tayi ai babu matsala, tunda Hanif ya dawo shi zai kaita ko zuwa jibi tare da driver sai su je."

"To Allah yasa hakan shi ya fi alkhairi." Aunty Zainab tace hakan

Suka amsa da Amin, daga nan suka koma hiran maganar auren SHAREEF ɗin da za a ɗaura da zaran yarinyar ta dawo hutu,
Duk da ransu bai so ba duk sun bada rashin goyon bayan su, a cewar su, "wanne aure ne za a yi yarinya ta tafi wata ƙasa da aurenta babu Miji? Wannan ba yi bane, ai tun farko gwara kar a ɗaura a bari sai ta dawo gaba ɗaya sai a yi bikin."

Momy dai bata da yanda zata yi tunda a so samun ta ne ma kar ya auri yarinyar, amma ba damuwa tunda haka Allah yaso, yanzu abun da ya rage mata kawai ta fahimtar da Maryamu; domin baza ta so ta tafi batare da ta san da maganar ba, ko don gudun wata matsalar.
[27/02, 9:04 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

          *SHAREEF*
               _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*





*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days.












__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE42to43*
_____Momy ita da kanta ta zaunar da Maryamu tayi mata bayanin tafiyar nata; da suke shirin tura ta Abuja ta zauna a can tayi karatun ta

Maganar ya zo mata a mugun bazata, shiyasa bata yi ƙasa a gwiwa ba tace wa Momy, "don Allah Momy ba na son a kaini can, na fi son zama da ku Momy don Allah."
Sai ga hawaye sharr; domin abu ɗaya yasa ta ruɗe lokacin sabida ganin za a raba ta da SHAREEF, wadda ba ta jin zata iya jure wa, baza ta iya nesa dashi ba, baza ta iya ba

Momy kuma sai ta kama hannunta tana kallonta na ɗan wani lokaci bata ce mata komai ba, daga baya sai tace, "ki yi shiru haka nan ba na son wannan kukan naki, abun da yasa kika ji nace hakan sabida can za ki fi jin daɗin zama ne Maryam, kinga ita tana da Yara sa'annin ki za ki yi karatun ki cikin kwanciyar hankali, ai mu ma ba a son ranmu zamu bar ki ki koma can ba Maryam."

Sai tayi saurin girgiza mata kai tana hawaye sosai a wannan lokacin, yayinda cikin rawan murya take furta, "wlh Momy na fi son zama daku, ba na son na je wani wuri, nan ya fi min can."
Sai kawai wasu zafafan hawayen suka ƙara ɓulɓulowa, taya ya zata iya sanar da Momy baza ta iya zuwa can bane duk saboda SHAREEF? Taya ya zata iya yin nesa dashi? A'a bazai yiwu ba gaskiya. Yayinda take girgiza kanta ba tare da ta san tana yi ba

Inda ita kuma Momy ta bi ta da kallon tausayi, ta san meye a zuciyarta, lokaci guda ganin ta ruɗe shiyasa ta soma rarrashinta tana faɗa mata dalilin da yasa take son tayi nesa da nan, bayan ta gama ta ƙare maganar nata da cewan, "ki yi haƙuri kinji ko Maryam? Na san SHAREEF ne a ranki, amma idan kika yi nesa dashi hakan zai kawo soyayyarki a zuciyarsa, kuma zai rage ƙiyayyar da yake miki, ki je can ki yi karatun ki; ki sauya daga yanda yake kallon ki Bagidajiya ba ki kai ba, duk sanda kika dawo zai ƙaunace ki fiye da yanda kike tunani, kuma idan kika ci gaba da zama a nan baza ki yi karatu sosai yanda ya kamata ba; kinji Ni ko?"

Ita bata fahimci mai Momyn take nufi ba, taya ya tafiyar ta zai kawo canji a kan irin ƙiyayyar da SHAREEF yake mata? Taya ya hakan zai kawo sauyi? Zata tafi ta dena ganin sa ne, zai manta da ita gaba ɗaya bazai sake tuna ta ba, ita bata ga hanyar da zai sa ya so ta ba in har bata zauna a nan kusa dashi ba, sannan ma zuciyarta baza ta taɓa iya jure wa ba, wlh mutuwa zata yi, ko dai-dai da rana ɗaya ba ta son tayi missing ganin fuskarsa, hakan kaɗai yana saka ta farin ciki

Duk yanda Momy ta so ta fahimtar da Maryamu, amma ta kasa gane wa, ta tubure a kan, "babu inda zata je."
Dama Maryamu akwai gardama, don su Momy basu san halin ta bane, tunda ta zo wurin su bata nuna musu ainihin wace
End Ads