da kallon ƙira da baiwar halittar da Allah ya yi mishi
Komai nashi fes-fes ne kamar ka latsa shi jini ya zuba, ko daga kallonsa ka san yana ji da tsabta da gayu, fararen shadda ne a jikinsa bugaggiya da alamun ma sabo ne fil, don har wani ɗaukar ido take yi tsaban sabunta da yanda take shining, uwa uba da kallo ɗaya ka san kuɗin ta ya wuce a tsaya ana lissafi, sai shigan ta ƙara fito mishi da tsantsan kwarjinin sa gami da kamalan sa, kansa ɗauke da baƙin hula da ya mirza ta ta zauna mishi daram, yayinda sajen sa sai ɗaukar ido yake yi ya kwanta luf-luf har zuwa ɗan tsut ɗin gemun sa mai ban sha'awa. Sosai Maryamu ta gama shagaltuwa da kallonsa, har ta manta ma a inda take sabida yanda ta shige tunani tana ayyana abubuwa da dama a cikin ranta
Sai ji tayi ya dakatar da Motan, wanda hakan ne ya dawo da ita cikin hayyacin ta nan take, sai ta sake ware manyan idanunta a kansa tana jin zuciyarta na buga wa da sauri tare da fargaban kuma abun da zai biyo baya, musamman yanda ta ga ya fice daga cikin Motan, shiyasa itama sai tayi tunanin fice wa kar tayi wani laifin kuma. Tana jan ƙofan ta ga ta buɗe; shiyasa ta fice da sauri tana manne da kwalin takardun ta
Kallo ɗaya yayi mata ya wuce ba tare da ya sake bi ta kanta ba, har yanzu kuma akwai face mask a kan fuskarsa, sai ma ƙara gyara mishi zama yayi saboda ba ya son a ga fuskarsa tare da wannan kucakar yarinyar; It is his greatness that will spill
Da sauri Maryamu ta bi bayansa ba tare da tunanin komai ba, can daga nesa take biye da shi a hankali sabida ganin shima tafiyar da yake yi, kamar bazai taka ƙasa ba don taƙama da izza, "komai nasa shi dai mai kyau ne, ji be yanda yake tafiya?" Har shagaltuwa tayi da kallon tafiyar nasa zuciyarta na fari; ta kasa ko kallon tsarin makarantar ma bare ta san inda take jefa ƙafafun ta
Kasancewar school ɗin kowa na aji, tsit makarantar babu hayaniyar students kowa yana class yana ɗaukar darasi
Dayake SHAREEF bai taɓa zuwa school ɗin ba, shiyasa sai da ya tambaya wani Malami da ya gani a hanya, ya tambaye sa office ɗin principle, shi ne yayi mishi kwatance har ya dangana ga can
The principal is sitting on his chair, wanda alamun fitowar sa kenan daga ban-ɗaki yana share hannunsa da handkerchief. After he heard knocking, he gave permission to enter and looked at the door
SHAREEF ya shiga ciki, Maryamu na biye dashi a baya kamar wata jela sai zare manyan idanunta take yi
Cikin mutunta wa principal din yayi masa iso, tare da nuna masa wurin zama. Bayan ya zauna sai suka yi musabaha daga bisani kuma SHAREEF yace
"My dad told me to come and meet you, because you know about my arrival." Yayi maganar daƙyar fuskarsa babu walwala
Sai principal din ya ɗan sake kallon sa da kyau, sai kuma yace, "ok ko kai ne ɗan wurin Alhaji Ahmed da zaka kawo yarinya?"
Kai ya jinjina mishi Without saying anything
Sai ya ɗan faɗaɗa fara'an sa tare da cewa, "well. Doctor ya faɗa min ai, ita ce wannan yarinyar?" Ya ƙare maganar yana duban Maryamu
A yatsine dai SHAREEF ɗin ya amsa mishi, idanunsa a kan wayansa yana duba wa
Sai principal din ya kira Maryamu ta matso inda suke, ya dube ta da kyau yace, "ƴan mata mene sunan ki?"
Kai tsaye tace mishi, "Maryamu Haruna."
"Good. What school did you come from?"
Ɗan jim tayi, sai kuma tace, "Shaikh Ibrahim Arab Zaria."
"Masha Allah, kawo takardun mu gani, duk da dama already Doctor yayi min bayanin ajin da zamu saka ki.." sai ya tsayar da maganar nasa yana duba takardun. Bayan ya gama ya ɗauki waya yayi kira
It was not long before a teacher entered the office
Sai ya dube sa yace, "ku je da yarinyar nan sai a yi mata interview, SIS 1 za a bata, A. ko B. duk wanda ka ga ya dace da ita, sai ku je a ɗaukar mata har da uniform, a bata komai na school please ka hanzarta ko?"
"Ok sir." Ya amsa mishi cikin girmamawa, tare da duban Maryamun yana ce mata, "su je."
Haka Maryamu ta bi bayansa suka tafi
Kamar yanda principal din yace, hakan aka yi mata, tunda dama private school ne, komai su suke bayar wa har kayan makaranta da littafai, shiyasa duk aka bata ta dawo dashi office ɗin, after Malamin ya kaita har ajin da zata zauna ya nuna mata, SIS 1B
Daga nan SHAREEF ya miƙe suka yi sallama da principal ya fice abun sa. Kai tsaye motansa ya shiga ya kunna yana jiran ta shiga, yana jin sanda ta buɗe Motan ta shiga shiyasa ya ja da ƙarfi ya nufi bakin gate
Inda ta zauna ɗazu, yanzu ma nan ta zauna, don bata yi gigin sake zama mishi a kan kujera ba, yanzu sai farin ciki take yi sabida ganin an gama mata komai, sai zuwa school kenan? Ga Makarantar mai kyau kuwa, sosai ya bata sha'awa, musamman yanda students ɗin suka soma fitowa a lokacin da zasu fito daga school ɗin, alamun an tashe su break ne. Numfashi ta ja tana bin kayan hannunta da kallo; amma bata iya motsa su ba bare ta buɗe ta gani, tana tsoron tayi motsin da zata ɓata wa SHAREEF rai, shiyasa ta haƙura ta lafe kai a jikin kujerar tana ta satan kallon sa
A lokacin ma waya yake yi, da alamu ransa a ɓace yake, sai tsitsiya faɗa yake yi duk da muryansa ba a sama take ba, kuma da turanci yake maganar bata fahimci mai yake cewa ba, amma alamu ya nuna tsiya yake yi. Sai can kuma ta ga ya ja tsaki yana tsayar da Motan a dai-dai kan layin gidan su
Ba tare da ya juya inda take ba ya bata umarnin fita. "Get out."
Yanda muryan nasa ta ratsa mata kunne, nan da nan sai jikinta ya soma rawa, da sauri ta saka hannu ta buɗe motan ta fice. Kafin ma ta ƙarisa rufe murfin motan; ya figa motan a guje ya bar wurin da reverse. Da kallo Maryamu ta bi shi har ya ƙule ma ganinta, kana ta sauke ajiyan zuciya tana ɗan lumshe idanunta, meyasa take samun sauyin yanayi idan tana tare da shi? Bata san meyasa take firgita ta rasa ƙarfi da kuzarin ta ba, uwa uba tsoron shi da take ji wanda ba sabon ta bane hakan, sosai take jin shakkar sa da ganin girmansa a idonta, shi ne mutum na farko a rayuwarta da take tsoron ɓata mishi rai
Kayan ta kwashe a wurin, sabida tun lokacin da ta fito daga motan jiki na rawa ta sake su sabida ƙoƙarin ta na ganin ta rufe mishi ƙofan motan. Kwashe wa tayi ta miƙa hanyar da ta ga sun biyo ɗazu, Allah yasa an shigo anguwan kuma daga nan babu nisa, shiyasa ta gane gidan. Tana zuwa ta buga gate ɗin; Mai gadi ya buɗe mata ta saka kai ciki.
***
While SHAREEF kuma, kai tsaye hanyar Company ya nufa, mirza Motan yake yi a hankali, yayinda yake duban wayansa yana laluban numban PA, The phone was ringing in his ear, while his eyes were looking at the street. A natse ya soma magana cike da izza yace, "Are you gone or kuna nan?"
"Ok, ka bar su su tafi kawai, you stop and wait me, ka kira Mahmud su wuce tare."
PA bai tambayi meyasa ba, don haka ya amsa mishi cikin girmamawa
Shi kuma sai ya kashe wayan yana ƙoƙarin ajiye wa. Amma sai kiran Hanif ya shigo wayan, hakan ne yasa ya rage speed na Motan sosai yana ɗauka, in a slow voice yace, "Hey Guy, ina ka shiga na kira ban ji ka ba?"
"Bro I went to school, I was there taking a lecture, kai ya ɗauki zafi. I didn't see your call sai yanzu."
"Oh! Kuna shan gwale-gwale kenan?" Sai ya ɗan yatsina fuskarsa tare da furta, "na ɗan tausaya maka kaɗan."
Dariya Hanif yayi yace, "I didn't say I needed tausayin ka, nima na kusa huta wa since aski ya zo gaban goshi, mun kusa zuwa ɗaya ai."
"Ba wannan ba, ka duba message da na tura maka ta e-mail?"
"No, ban duba ba, yaushe ka tura?"
"Yau da safe ne, ka duba zamu yi waya later. I am driving now."
"Ok Bro, ya su Momy? Ban samu na kira su ba."
"Fine."
"Ya kanwarmu? Is that why you didn't tell me about her coming to the house? Kuma at least kai ya kamata in fara jin maganar a wurin ka."
Cikin rashin fahimta SHAREEF yace, "I don't understand you, who are you talking about?"
"Maryam mana, yarinyar da Dady ya kawo ta ƴar wurin sister ɗin sa. I am very happy, you see we got a sister, a little sister." Ya ƙare maganar da farin ciki
While SHAREEF sai ya ja tsaki tare da furta, "You are not serious wlh, I thought it was an important statement, to ina ruwana da ita?"
Da mamaki Hanif yace, "it is our sister ai, at least zamu yi farin ciki da zuwan ta, ko ba haka ba? Kuma don naga zata zauna tare da mu ne."
"I am also saddened by her arrival, kai baka ganta bane that's why kake furta hakan, wata mumu da ita, baƙa sai ƙaton ido a tsakar ka, ga kallon tsiya; alamu tsohuwar mayya ce yarinyar nan, duk yanda aka yi a ƙauyen su sun saba cin mutane." Sai ya ja guntun tsaki sabida takaicin tuno fuskarta da yayi
Yayinda Hanif kuma dariya ya kwashe da shi sabida jin abun da SHAREEF ɗin ya furta, "oh! Akwai aiki kenan Bro?"
Da rashin fahimta yace, "na me fa?"
"Har ina tunanin ko zamu haɗa ƴar gida ne, We just give her to you to marry, ashe kana mata kallon mayya ce...?"
"What...! Am I kidding you Hanif? Have you ever seen us play this game with you, or you want to annoy me?" Ya faɗa cikin tsawa da ƙoƙarin jan burki a bakin tanƙamemen gate na Companin su
Jin hakan da Hanif yayi ya san ya taɓo ƴan Maza, don ya san halin ɗan uwan nasa, shiyasa sai yace, "Sorry Bro, wasa nake maka Allah, Let's leave the conversation since you don't want to."
Cikin ƙunai rai yace, "dole ka faɗa haka mana, sabida baka kusa da Ni wlh da sai ka ga mai zan maka, shashasha kawai." Ya ja tsaki yana katse wayan,
Sai ya ajiye yana danna horn da ƙarfi ransa na suya,
Ana buɗe masa gate ɗin ya harba Motan ciki kamar zai banke mutanen da suke zirga-zirga a haraban Ma'aikatan, since ransa ya gama ɓaci da maganar Hanif ɗin.
[30/01, 9:06 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱
__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE19to20*
Maryamu Sarkin zumuɗi, ta ƙosa Monday yayi ta soma zuwa school, kullum maganar ta kenan, har su Momy sun gaji da ji suyi ta mata dariya. Dole Momy ta saka Sadiq ya ɗauki Maryamun ranan Sunday suka je kasuwa aka sake mata siyayyar abubuwan da zata buƙata na makarantar, shoes and socks da kuma bag da littafai duk sai da aka sake siyo mata, dama dayake makarantar text books suka bata wanda dole a school zaka siye su tare da uniform. Komai an kammala mata; fara zuwa kaɗai ya rage
Ranan Monday kuwa da duku-duku Maryamu ta tashi, yau tana zumuɗi shiyasa ta tashi da wuri. Kafin ƙarfe shida da rabi har ta gama shirya wa ta saka uniform ɗin, ai kuwa ba ƙaramin kyau suka yi mata ba, duk da kasancewar ta Black beauty sai kayan suka haska ta, rigan fari ne da Hijabin, sai coffee color na wando irin mai zane-zane da aka yi shi da kalan farin, babu ɗankwali tunda Hijabin mai hula ne da aka yi da kalan wandon, ba ƙaramin mugun fito da kyawunta kayan suka yi ba, kamar don ita aka yi, sai tayi ƴar ƙarama a kayan yarintan ta ya fito ainun, ta sha Powder tare da ɗigon goshin ta, sai ta saka lipstick a laɓɓanta sai shining suke yi,
Ƙafafunta kuma sanye da cover shoes baƙi da farin socks dogo, sai ta goya Jakarta mai ruwan zuma babba wanda daƙyar take iya ɗaukar ta ma don girma,
A haka ta fito Falo ta tarar da su Dady zaune
Dady na riƙe da jarida tunda babu inda zai je yau, kayan jikinsa ma Jallabiya ne, suna ɗan taɓa hira da Momy, wacce take zaune gefen sa tana fifita mishi tea. Sai ganin Maryamun suka yi ta fito tana washe baki
"Inye.. inye.. wow daughter, ke ce kuwa?" Cewar Dady kenan cikin barkwancin sa yana dariya da kallonta
Ƙarisowa wurin tayi still tana washe baki; baki har kunne alamun farin ciki ya cika ta ne
Momy ma tace, "kin ganki kuwa ƴar Dady? Kin yi kyau Masha Allah, so beautiful."
Dariya tayi tana kama hannayenta wuri ɗaya, kanta a ƙasa ta kasa furta komai tsaban murna
Momy tace, "taho nan ki zauna, kuma haka ake yi har da ɗigo bayan kin san makaranta za ki je? Zo in goge miki."
Ƙarisa wa kusa da ita tayi, ta zauna Momyn ta kama mata hannu tana saka daya hannun nata tare da ƙoƙarin goge mata
While Dady kuma yana kallonsu da murmushi a face ɗin sa, sai yace, "to daughter yanzu sai fara zuwa makaranta, kinga sai ki mayar da hankali kiyi abun da ya kaiki, ban da wasa da shiririta kin ji ko?"
"To Dady."
"Masha Allah, ƴar Dady Allah yayi miki albarka."
Daga Momy har Maryamun suka amsa da Amin
Momy tace, "yanzu sai ki je ki karya kafin Sadiq ya fito ya kaiki, tashi maza ki je kar lokaci ya ƙure."
Miƙe wa Maryamun tayi ta wuce wurin dinning ɗin
Ajiyan zuciya Dady ya sauke tare da furta, "na so SHAREEF ne zai riƙa kaita tunda kinga muna bukatar shaƙuwar su sosai, amma taurin kai ne da Yaron nan wlh, duk da haka zan matsa mishi dole ya riƙa kaita wata rana, duk ranan da Sadiq bai da lecturen safe sai shi ya kaita in zai wuce wurin aiki."
"Nima haka na gani Alhaji, bari in duba Sadiq ɗin ko ya gama shirya wa tunda time ya kusa." Sai ta miƙa masa tea ɗin tana tashi ta wuce sama,
Ɗakin Sadiq ta shiga ta ganshi har ya gama shirya wa yana saka takalma a ƙafan sa,
Murmushi tayi tace, "Autana kayi kyau!"
Kwaɓe fuska yayi yana kallonta da cewa, "Oh! Momy, Ni yanzu fa na tashi a Auta, Maryam ne Auta ba Ni ba."
Shafa kansa tayi tace, "ban da abun ka, ai akwai Autan Maza, don haka har yanzu kai Autana ne, sai kayi aure sannan zaka girma a wuri na."
Dariya yayi yace, "kai Momy."
"To tashi mu je kar ka sa Maryam tayi late, har ta shirya ga ta can tana jiran ka."
"Ok mom I'm coming."
Fita tayi ta bar sa a nan yana gama ida shirin nasa, bayan ya gama ya ɗauki car key ya fito rataye da ƴar ƙaramar Jaka na Maza. Falon ya sauka ya ƙarisa wurin su Dady yana sake ma Dadyn Barka da safiya
Ya amsa shi cike da fara'a yana ƴar tsokanar sa kamar yanda ya saba wani lokacin, "ina ka shiga ka shuka min daughter tana faman jiran ka? Ka sa zumuɗi ya hana ta zama sai sunturi take yi."
Ya ƙare maganar yana kallon Maryamun da ta taso da sauri sabida ganin Sadiq ɗin ya fito
Dariya suka yi, har ita wacce ta iso wurin
Momy tace, "kin gama karyawan ne da kika taso?"
"A'a Momy, na ga Yaya Sadiq ya fito ne zamu tafi."
"To ban da abun ki, ai shima bai karya ba, ku je tare ku gama sai ku wuce kar lokaci ya ƙure."
"Mu je Little sister." Ya furta yana yin gaba,
Sai da suka ƙarisa wurin sannan ya kalle ta yace, "kin yi kyau my dear, dole na miki hoto in mun fita, I will save the history to remember another day."
Murmushi tayi duk da bata san me yace daga ƙarshe ba, sai tace, "amma Yaya SHAREEF bai ga kyawun da nayi ba? Ba na son nayi asarar kwalliyan nan nawa tunda nima nayi kyau."
Yanda tayi maganar cikin alfahari shiyasa shi yin dariya, yace, "kai Maryam kina da abun dariya wlh, and he will not wake up now, amma idan nayi miki hoton zan tura mishi ko?"
Kai ta ɗaga mishi, sai kuma ta ɗan yatsina fuska da cewan, "ba haka na so ba fa amma. Anyway..." Sai kuma tayi shiru saboda bata san taya zata furta maganar da take son yi da turanci ba
Murmushi Sadiq yayi yana mamakin kakkamban yarinyar, tamkar ba a ƙauye ta fito ba, sai yace mata, "Oya mu ci abincin mu tafi."
Ita ta haɗa mishi tea, shi kuma ya zuba arish da ƙwai a plate, suka ci a tare tana korawa da ruwan tea ɗin ta wanda ta haɗa shi tun ɗazu, har ta cinye nata arish ɗin, but ganin ya zuba nashi ta saka hannu suna ci tare
Bayan sun gama suka dawo Falo, Sadiq yace, "zasu wuce."
Tare suka yi musu addu'a da fatan Nasara, sannan suka fita suka wuce inda Motan Sadiq ɗin yake, gaba ta shiga ya ja suka bar gidan
Sai surutu Maryamun take mishi a cikin Motan, tana faɗa masa yanda take jin zuciyarta na harba wa da fargaban makarantar
Shi kuma sai dariya yake mata yana cewa, "oh! Ashe kina da tsoro haka?"
Murmushi tayi tace, "kar in manta Yaya, kayi min hoton ka ji."
"Ok, let's go to the school, I'll do it for you. Da alamu ba kya son kyawun nan ya wuce Yayana?" Ya ƙare maganar cikin smile
Ita kuma sai ta rufe fuska tana ɗan jan numfashi tare da murmusawa. She feels happiness coming from the bottom of