x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 26 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 75001 words
  • 78000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 406

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
🌱🌱🌱🌱🌱

      *SHAREEF*
          _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*





*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days.










__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE28*
_____ *NIGERIA*
            *KANO STATE*
Bell ɗin da aka buga, shiyasa ɗaliban makarantar suka dinga fitowa kowa yana nufan hanyar gate cike da farin ciki

Amina, Feena da Maryamu suka fito a jere suka nufi bakin gate ɗin,
Bayan sun fita bakin gate babu wanda aka zo ɗauka a cikin su, shiyasa suka ja gefe suka tsaya suna ɗan taɓa hira, duk da hiran daga Amina sai Feena suke yin ta, Maryamu kuma na sauraron su tana baza idanu a kan hanya don ta ga ta'inda Motan SHAREEF zai zo ɗaukar ta, domin ta fi saka ran ganin sa since shi ya zo ya ɗauke ta ranan farko

Feena ce ta taɓo ta tana ce mata, "wai Ni kam Maryamu in tambaye ki?"

Dawo da idanunta tayi a kanta, sai ta gyaɗa mata kai alamun tana sauraren ta

"Ɗazu na ga kamar Sadiq ne ya kawo ki school ɗin nan, right?"

"Eh, kin sanshi ne?"

Dariya tayi tace, "haba, wlh na ga kamar ta ɓaci, Ni dai kamar shi na hango a cikin Motan. Na san shi mana, anguwan mu ɗaya dashi fa, and kuma Dad ɗin sa Abokin Abbana ne."

Ɗan washe baki Maryamu tayi jin abun da Feena take faɗa; sai tace, "ashe ke ma a anguwar mu kike?"

"Eh a nan nake, tazaran gidan mu da gidan su ba wani mai nisa bane, mu muna layin farko ne, su kuma na biyu, amma ban taɓa sanin ki a gidan ba; because a baya ina zuwa kafin karatu yayi zafi na dena samun time. But Momy tana yawan zuwa mana."

Maryamu tace, "nima ba a gidan nake ba, ban jima da zuwa ba, Ni ƴar Zaria ce, da Dadyn su Yaya Sadiq da Innata brother and sister ne."

Dariya suka yi, sai Feena tace, "wow! Amma duk da haka kuna yanayi da Sadiq wlh, yanda kike da manyan idanu haka shima, wani in ya ganku zai ce ƙanwarsa ce ta jini, duk da dai dama akwai jinin ƴan uwantaka."

Murmushi kawai Maryamu tayi bata ce komai ba, duk da a ranta ta ji dadin ce mata da aka yi suna kama da Sadiq ɗin

Amina tace, "Friends bari in wuce, ga driver na nan ya zo, but I am glad to hear that you are the same the village, wata rana idan na kawo miki ziyara sai ki raka Ni gidan su Maryamu ko?"

"Kar ki damu ƙawalli, ai har sai kin gaji da zuwa ma, duk sanda za ki zo tare zamu kai mata ziyara in har tana so?"
Feena ta ƙare maganar tana ƴar murmusawa da kallon Maryamu

Ita kuma tace, "mai zai hana? Zan yi farin ciki da hakan."

"Ok na tafi, kar ya gaji da jira na, sai tomorrow."
Ta ɗaga musu hannu ta wuce wurin Motan

Yayinda su kuma suka ci gaba da tsayuwa a wurin har an watse amma ba a zo ɗaukar su ba

Feena tace, "anya baza mu samu abun hawa mu wuce ba since duk wuri ɗaya zamu tafi, hakan zai fi ko?"

Maryamu da ba ta son tafiyan, sai ta girgiza kai tace, "a'a mu ƙara jira, Ni dai na san za a zo ɗaukana, kuma idan ya ga babu Ni ransa zai ɓaci."

Dariya ta ɗan yi, tace, "Sadiq kike nufi?"

"No, Yaya SHAREEF."

In surprise Feena tace, "haba, shi yake zuwa daukar ki?"

Jinjina mata kai tayi tana bin Motan da ta zo ta faka a gefen su

Hakan ne yasa Feena bata ce komai ba sai ta kalli Motan tana cewa, "yauwa ga Yayana nima ya zo, ki zo mu je sai ya sauke ki a gida tunda duk anguwa ɗaya muke, kar mu tafi mu bar ki a nan."

"A'a, ki tafi kawai, zan jira."

"To Shikenan, tunda ba kya son taimakon nawa, bye sai gobe." Ta furta tana mata murmushi

Itama murmushin tayi mata tare da ɗaga mata hannu, sai ta sake gyara tsayuwa a wurin tana kallon hanya

Wurin Motan Feena ta nufa, ta buɗe ɗaya side din ta shige, fuskarta yalwace da murmushi tace, "Yaya Hunaip, I didn't think you would come and take me, ashe da gaske kake yi?"

Murmushi yayi mata, yana ɗan duba agogon sa tare da furta, "dole na ne ai, duk da ina da wurin zuwa but ɗauko ki ya fi min komai muhimmanci."
Sai ya ɗan ɗaga kansa yana duban wurin da Maryamu ke tsaye sai baza manyan idanunta take yi tana kalle-kalle, a natse ya furta, "wancan fa?"

Wurin da yake kallo ta bi da kallo, sai tace, "oh! Maryamu, tana jiran Yayanta ne itama ya zo ya dauke ta."

Tsira mata ido ya ɗan yi, sai kuma ya dubi Feena yace, "but time ya wuce sosai, baza mu iya ɗaukar ta bane; in bata da nisa?"

Jin hakan ne yasa Feena shiga farin ciki, don ta san halin Yayan nata zai yi wuya ya kula ta ma, amma abun mamakin da kansa ya nemi rage mata hanya, shiyasa cikin farin cikin jin hakan tace, "Yaya Hunaip, ai gidan su Dadyn SHAREEF take, sister ɗin su ne ita."

Ɗan waro ido yayi tare da furta, "serious Auta?"

"Allah kuwa Yaya."

"Ok, ki kira ta tazo mu wuce."

Fita Feena tayi tana ajiye Jakarta, sai ta nufi wurin Maryamu tace, "friend, ki zo mu je, Yayana ya ce ki zo mu ajiye ki a gida, kinga time ya ƙure har six ta kusa, dare zai yi miki a nan in har kika zauna, maybe wani abun ya tsayar dashi bai samu damar zuwa ba, but tunda duk wuri ɗaya zamu je why not ki biyo mu."

Ita kanta Maryamun tana tunanin bazai zo ɗaukar ta ba, maganar Feenan akwai ƙamshin gaskiya, shiyasa ta gyaɗa kanta ta bi bayanta zuwa wurin motan

Da kanta Feena ta buɗe mota back sit ta shiga, sannan ta rufe itama ta shiga gaba

Maryamu na daidaita zamanta a kan kujerar, ɗago kan da zata yi suka haɗa ido da Hunaip da ke faman kallonta ta cikin mirror, kallon kallo suka yi wa juna, before ita ta dauke kanta tana mayar da hankalin ta a kallon hanya

Shi kuma mamakin yanda suka haɗa ido da ita har ta kalle shi, sannan ta ɗauke kai a kansa yake yi, at least ko gaisuwa ya kamata tayi masa since taimakon ta suka yi ai.






🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆


_____Slowly ya cusa hancin Motan cikin gidan har zuwa packing space, dakatar wa yayi tare da kashe Motan yana ɗan jan huci kaɗan, kallon kansa yayi a mirror yana ganin yanda tulin gashin gaban kansa ya cukurkuɗe tamkar babu gyara, shi kansa ya manta rabon da ya je ya gyara gashin bare har yayi aski ya rage tsawon sa, sabida aiki da yayi masa yawa a ɗan kwanakin, ga rashin jin dad'in jikinsa da yau yake jin cikin sa yana ɗan takura masa da ciwo, musamman gefen cikin sa, duk wani abu da yake yi duk na karfin hali ne, amma har ga Allah a ɗan kwana biyun nan ba daɗin jikinsa yake ji ba, kuma ba ya son zuwa asibiti bare ya nuna alamar da ƴan gidan su zasu gane, ya san dole Dady zai matsa mishi zuwa ganin Likita. Ɗan yatsina fuskarsa yayi yana hura hanci kaɗan, sai ya saka hannu ya gyara gashin sa yana ɗan kwantar wa tare da shafa saman sajen sa har zuwa gemun sa da ya ƙara tsawo sosai a yanzu. Numfashi ya ja ya buɗe ƙofan yana ɗaukar jakarsa tare da fito wa, rufe ƙofan yayi ya nufi hanyar shiga ƙofan gidan cike da takun ƙasaita; yana yi yana kwaɓe fuska kamar ya ga kashi, tura ƙofan yayi da sallama a bakin sa

Dady da ke zaune a saman one seater, Yana sanye cikin shuɗiyar Jallabiya ƴar Dubai, ya ɗaura ƙafafunsa a saman Centre table yana karatun Jarida, idanunsa sanye da medical glasses. Ɗago kai yayi yana duban SHAREEF wanda ya shigo ciki a yanƙwane kamar zai zube tsaban yanda yake tafiyan, amsa masa sallaman yayi yana masa murmushi, sai da ya ga ya iso daidai wurin sa yake cewa, "oh! Ka ga ragwon my Son, duk wannan tafiyar don ka nuna mana ka gaji ne?"

Yatsina fuska yayi yana zama a saman two seater wanda yake facing Dady, sai yace, "Dady baka san ya nake ji bane, but ina shan gwale-gwale everything is too much for me, things are starting to be too much for me, wlh na ƙosa Hanif ya dawo."

Dariyan da Dady yake yi, shi ya fito da Momy daga kichen riƙe da bowl ta zuba fruits a ciki, sai tace, "dariyan me kake yi ne haka Alhaji?"

"Ni da my Son ne, ya zama ragwo yanzu, I see his efforts but now he is showing me his failure, ki ce ko aure ma yayi zai riƙa nuna wa Matar tasa ragwancin nasa."
Ya ƙare maganar yana ci gaba da dariyan sa

While Momy na taya sa, sai tace, "ban da abun ka, ai aiki daban riƙe Mata daban, i know ko Mata biyu aka hada wa SHAREEF zai iya riƙe su kuma a ga sauyi cikin one month ma, don haka Yarona ba daga nan ba, dole abun yayi masa yawa aikin Company guda ba wasa ba."

Ɗan janyo eyeglasses ɗin sa yayi zuwa saman hancin sa yana dalalo wa Momy idanunsa da fadin, "Oh! Yau kuma? Ke ce da kare SHAREEF?"

"To ai na ga kana nema ka mayar min da shi weak man ne, bayan na san Jarumin namiji ne ɗana. Amma tsaya muna magana ban ga Maryam ba? Ko baku dawo tare bane?"
Ta ƙare maganar tana kallon SHAREEF wanda ya rufe idanunsa yana faman cije laɓɓansa

Maganar Momyn ne yasa ya buɗe idanun, sanin da yayi da shi take yi

"Basu shigo tare ba, maybe bai ɗauko ta ba kenan?" Dady ya furta shima yana mayar da hankalin sa ga SHAREEF domin jin mai zai ce


"Wai SHAREEF ana magana, ina yarinyar nan? Kar dai a ce baka dauko ta daga school ba?" Momy ta ɗan yi maganar a zafafe sabida ganin yayi musu shiru yana tsilla ido

Shi wlh shaf ya manta da yarinyar, kuma ya ga jiya ba shi ya ɗauko ta ba shi yasa yau bai yi tunanin zuwa ba, in fact ma bai tuna da ita ba bare yayi tunanin zuwa school har ya dauko ta, since Dady yayi masa gargaɗin he will always come and pick her up.
"Mom wlh na manta."

Salati Momy ta saka tana tafa hannunta, "to hurry up and go get her tun kafin in saɓa maka wlh."

"Mom don Allah ki yi hakuri, wlh ba na jin daɗi, call Sadiq to pick her up since it was too late before I went."

Harara ta watsa mishi tace, "miƙo min wayar ka."

Miƙa mata yayi yana tura baki

Dady yace, "wato baka ji maganar da nayi maka ba? Na ce kullum kai zaka na zuwa ka dauko ta but ashe ta bayan kunnen ka ya bi ko?"

"Dad, the problem in my head is why I forgot, and today I passed five thirty before leaving the office, I forgot."

Girgiza kansa kawai Dady yayi yana mai ɗaukar jaridar shi da ya ajiye, sai kuma ya sake duban sa yace, "ya maganar wurin aikin? Ina fata komai normal?"

"No Dad, har yanzu dai kayan nan basu iso ba, i think akwai wata matsalar ne."

"Meyasa baka faɗa min ba? Ba yau ka ce za a kawo ba?"

"Eh Dady, but I don't know the problem, har yanzu kayan bai wuce Singapore ba."

Guntun tsaki Dady ya ja yana ajiye jaridar tare da furta, "But you should inform me of this important matter, amma ba wai ka bar maganar ba."
Wayansa ya ɗauka yana latsa wa

At that time, Momy finished talking to Sadiq, sai ta miƙa masa wayan tana cewa, "riƙe wayarka, and from today if you come back to this house without her; zaka ga mai zan maka."
Ta ja ƙwafa tare da ɗaukar wuƙa ta soma yanka fruits ɗin

Shi kuma SHAREEF miƙe wa yayi bai ce komai ba, ya nufi upstairs, yanayin da yake ciki ma bai sa ya damu da faɗan Momyn ba, tunda sosai yake jin ciwon na ƙara taso masa a yanzu, dauriya kawai yake yi

Tsayar dashi Dady yayi sabida ya gama wayan da yake yi, yana kallonsa yace, "kayan nan baza su samu ba sai zuwa three to four days, ina tunanin akwai matsala gaskiya." Yayi maganar cike da damuwa

Tsaya wa SHAREEF yayi a saman benen yana kallon Dady, sai kuma bai ce komai ba ya juya ya wuce zuwa dakin sa, since bazai iya jure tsayuwa ba, gwara ya je ya sha magani idan ya dawo sai su yi maganar.
 




🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆


_____"Wai ƙawar taki ba ta magana ne? Since we started walking, she didn't say a word."

Dariya Feena tayi tace, "she talks a lot Yaya." Sai kuma ta ɗan juya tana kallon Maryamu tace, "friend, ga Yayana Hunaip, ba ku gaisa ba?"

Sai time ɗin itama ta tuna basu yi gaisuwa ba, sai tace, "ina yini?"

"Lafiya lau Friend, ai nayi tunanin laifi nayi baza a yi min sannu ba?"

Dukka murmushi suka yi sabida jin me yace,
Ita kuma sai ta ɗauke kanta daga kallon inda yake ganin suna haɗa ido dashi ta cikin mirror, ita abun da ke ranta ma ya fi damun ta, har ranta bata ji daɗin rashin zuwa ɗaukan ta ba, ta saka ran ganin SHAREEF amma kuma babu shi, maybe don an tilasta mishi ne shekaran jiya shiyasa ya zo, maybe kuma ba shi zai riƙa zuwa ya ɗauke ta ba.
Tunanin da ke ta faman yawo a cikin kwakwalwar ta kenan, har ma ba ta jin hiran da suke yi, sai da aka kawo ƙofar gidan su sannan ta jiyo sauti kamar na muryan Feena tana kiran sunan ta, firgigit tayi ta zuba musu ido

While su ma haka kallonta suke yi cike da mamakin ana ta magana amma ba ta ji

Feena tace, "friend ina ta magana ba ki ji ba? Kin faɗa dogon tunani. I hope kina lafiya?"

Gyaɗa kanta tayi, sai tayi duba ga inda suke, ganin ƙofar gate ɗin su ne yasa ta ajiye ɓoyayyen numfashi tana kallon su, "na gode."

Hunaip yace, "ba godiya tsakani, ki gaishe da mutanen gidan."

Kai ta gyaɗa mishi tana tura ƙofan ta buɗe, sai da ta fita sannan suka yi sallama da Feena ta rufe musu ƙofan, ta wuce bakin gate ɗin ta shige

Shi kuma ya ja Motan a hankali bayan ya ga shigewar ta, sai da ya juya kambun motan sannan yace, "na ga ƙawar taki kamar wani abun na damun ta? Ko haka take ba ta son magana?"

"I don't know Yaya, since nima jiya na fara sanin ta, ranan Monday ta fara zuwa but ban zo ba, amma ina tunanin rashin lafiyar da tayi ne har yanzu bata wartsake ba."

"Rashin lafiya? Kina nufin bata da lafiya?" Yayi maganar yana ɗan kallon fuskarta

"Eh, jiya mayar da ita gida aka yi ba ta jin dad'i, i think shi ne dalili."

Jinjina kansa yayi ba tare da yace uffan ba, yayinda yake ƙara tuna zanen fuskarta daga idanunsa, numfashi ya ja a ransa yace, "she's very beautiful, ta shiga raina".
[12/02, 9:13 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

      *SHAREEF*
          _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*
*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days.












__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE29*
_____Suna nan zaune sai ga Maryamun ta shigo cikin falon da sallaman ta,
Amsa mata suka yi suna bin ta da kallo,
Momy tace, "ina Sadiq ɗin? Ashe har ya ɗauko ki?"

Kwaɓe fuska tayi tana takowa wurin su tare da zame Jakar; take cewa, "a'a Momy, bai zo ba, na jira na jira but ban ga kowa ba."

"Bai zo ba? To wane ne ya ɗauko ki? Kar dai a ce da kanki kika dawo?"

"A'a Momy, wani ya ɗauko Ni, Yayan wata class mate dina, sun ce a nan suke shiyasa suka rage min hanya."

"Kawai ba ki san Mutum ba sai ki hau Motan sa Maryam? Duka-duka yaushe kika fara zuwa school ɗin da za ki yarda da wani?"

"Tunda ta dawo lafiya dai, a dena maganar Deeja, ki bar yarinya ta huta, maza tashi daughter ki je ɗaki ki cire kayan, time na sallah ma yayi, sai ki yi sallah kafin ki fito."
Dady ya furta yana mata murmushi

"To Dady."
Ta miƙe da Jakar nata a hannu ta wuce hanyar ɗakin ta

Ita kuma Momy sai tace, "bari in kira Sadiq sabida na san yanzu haka ya tafi ɗauko ta, since yace min yana kan hanya ne dama."

"Ok, gwara haka dai, ki kira sa, nima bari na je nayi alwala na wuce masjid."

A tare suka miƙe suka wuce upstairs ɗin,
Momy ɗakin ta ta tafi, ta kira Sadiq ta faɗa masa, "ya dawo kawai tunda Maryam tana gida."
Daga nan bayan ta ajiye wayan itama alwala tayi ta zo ta tayar da sallah.
***

_____Wasa-wasa SHAREEF tunda ya shige ɗaki basu ƙara jin ɗuriyar sa ba, ashe har masallaci bai je ba tunda cikin sa ya matsa mishi, kwanciya yayi tunda ya afa maganin ya kasa kataɓus, jikinsa sai rawan sanyi yake yi dole ya rufe kansa yana murƙususun ciwo

Dady ne da ya kula bai je sallah ba, after sun dawo yace, "Sadiq ya je ya duba sa a ɗaki."

Zuwan Sadiq sai ya ga halin da yake ciki, hankalin sa ya tashi ya nufi wurin sa yana faman kiran sunan sa

"Sadiq, I'm not feeling better, go and tell Daddy."

"Ok Yaya."
Ya amsa mishi cike da tausayin shi yana juya wa ya fita da sauri,
Kai tsaye Falo ya je ya sanar musu halin da ya ga SHAREEF

Sosai suka tashi hankalin su, da sauri suka taso a tare suka nufo dakin nasa

Maryamu na zaune bata tashi ba sabida tsoron ya hana ta shiga dakin sa, amma har ranta ta damu da jin cewa ba shi da lafiya ne, dama a
End Ads