x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 35 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 102001 words
  • 105000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 402

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
sa before ya kalle sa yace, "ka tsaya min ƙerere ka zauna mana zamu yi magana."

Zama yayi a saman kujerar kansa a ƙasa bai ɗago ba

Shi kuma Dady yayi banza dashi yana ci gaba da kallonsa

Sai daga baya Momy ta fito itama tunda ta ga SHAREEF ɗin zaune ta haɗe fuska, ta taho tana zama tare da ninyar yin magana

Sai Dady ya katse ta da furta, "Momyn Yara ina fruits ɗin da nace ki yanka min?"

Ta sha'afa sabida Allah - Allah take yi ta fito ta samu SHAREEF, shiyasa ta manta dasu bata ɗauka ba, "wlh na manta Alhaji, ɓacin ran da Yaron nan ya saka min na manta ban taho da shi ba."
Sai ta mike ta shiga kichen ɗauko wa

While Dady ya dubi SHAREEF yace, "ashe SHAREEF akwai ranan da zamu nemi alfarma a wurin ka ka kasa mana? Mu aura maka yarinya amma ka nuna mana bamu isa ba dole sai kayi yaƙi damu? Ko wasu suka yi maka wannan kyautar ba Iyayenka ba zaka iya watsa musu ƙasa a ido? Mu mu Iyayenka?" Ya ƙare maganar yana nuna kansa da yatsa, sai ya jinjina kansa yana jan numfashi

SHAREEF kuma yana sauraron sa but kansa a ƙasa ya kasa cewa komai

A sa'ilin Momy ta dawo ɗauke da tray ta ajiye a saman Centre table tana matso mishi dashi

"To abun da kayi yayi maka kyau, amma ka san da sani Maryam ƴar uwanka ce kuma Matarka, wlh summa tallahi babu mai raba auren nan naku dole ne ka zauna da ita ko kana so; ko ba ka so, kayi kaɗan mu zaɓa maka abu ka ƙetare mana, muna ganin abun da ya dace da kai tunda kai Yaro ne, amma nema kake yi ka nuna mana ka fi mu wayon ko? Bamu san me ya kamata da kai ba ko?"

"Alhaji ai wlh kai ka zauna kana masa magana cikin sanyin rai, kuma don kai fitsarrare ne yarinyar da ka nuna ba ƙaunarta kake yi ba; ba ka sonta amma don kinibibi ka zagaya kana neman ta har kayi mata ciki, kuma kake tunanin zaka iya tsere wa auren ta? Ai baka isa ba SHAREEF, kayi kaɗan don Ubanka, Maryam dole sai ka zauna da ita tunda ka nuna tana da amfani a wurinka har ka iya zuwa ka biya bukatar ka a wurin ta."

Cikin tashin hankali SHAREEF ya ɗago yana duban Momyn wacce take tsitsiya mishi tsiya cikin fushi da ɗaga murya, kwata-kwata bai gama fahimtar maganar nata ba don ya kasa gane cikin da take cewa yayi mata, bakin sa na rawa yake cewa, "Momy ciki kuma?"

"Ciki fa, ko zaka ce ba kai kayi bane? Ko kuma don ka ɗauki Maryam ɗin ƴar ƙauye bata da wayon da zata nuna ka tace kai kayi mata cikin ne? Ai Allah ya kama ka tunda ga shi har da result ka samu, sai ka shirya zama da ita har ƙarshen rayuwarka, ba kai ba yarinyar nan mara tarbiyya wacce basu san darajar kansu ba, ita wannan ɗin da ka tsana ita ce dole ka zauna da ita."

Da sauri ya miƙe kan ƙafafunsa duk da wani irin jirin da ke mamayan sa, cikin tsananin damuwa da tashin hankalin da ya bayyana a kan fuskarsa da still yana ɓarin laɓɓa yake cewa, "wai Momy taya ya zaku ce nayi mata ciki? Ni... Ni ne zan yi wa yarinyar nan ciki? Ta ina nayi mata cikin? Wlh ƙarya take min sharri ne bazan taɓa iya haɗa shimfiɗa da ƙasƙantacciyar yarinyar nan ba, never..."

Mari Momy ta kwaɗa masa don tsananin fushi da takaicin maganar nasa, "dan Ubanka ƙarya zata yi maka? Ko kuma Cikin da Likita ya faɗa mana karya ne ba gaske ne ba? SHAREEF kana cikin hayyacin ka kuwa mu kake son ka wulaƙanta?"

"Momy wlh ban yi mata ciki ba, Ni ban yi mata ciki ba." Ya furta hawaye na tsiyayan mishi riƙe da kuncin sa

Takaicin sa yasa Momy ta kasa magana sai kallonsa take yi kamar zata shaƙe sa, tana masa kallon mara hankali da tunani

Shi kansa Dady mamakin SHAREEF ɗin ne ya cika sa, "to idan ba kai kayi mata cikin ba waye yayi mata? Zata yi maka ƙarya ne?" Dady ya furta a ɗan hassale yana bin sa da idanu

Sai kawai SHAREEF ya fashe da kuka sabida ya kasa jure abun da ke faruwa, taya ya zai yi mata ciki yarinyar da ya tsana? Ta ina yayi mata cikin? Kawai gani yake yi suna son ɗaura masa wannan sharrin don kawai ya zauna da ita, wlh bazai taɓa zama da ita ba, ko me zai faru sai dai ya faru ba ya sonta bazai zauna da ita ba, wace ce ita da ta isa tayi mishi wannan sharrin? Sai ya karya ta ya kashe shegiya muddin ta shigo hannunsa.
[22/02, 8:57 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

          *SHAREEF*
               _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*





*DATA SHARE*

Call, message or whatsap 07065334256

*MTN*
500MB 150
1gb 280
2gb. 560
3gb. 840
4gb. 1120
5gb 1400
6gb. 1700
Verlid for 30 days.












__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE38*
_____"Wlh ko kukan jini zaka yi SHAREEF sai ka amshi cikin nan a matsayin naka, kana son ka nuna mana bamu san me muke yi ba ne? Kuma yarinyar zata yi maka ƙarya ne? ko kuwa Maryam tana da wayon da har wani zai yi mata ciki sannan ta laƙaba maka ne? To ka canza tunani da dabara, babu yanda za a yi Maryam tayi maka wannan mummunar sharrin, ai dama Likita ya faɗa kana buƙatar Mace a tare da kai, sai ga shi kayi amfani da damar ka ka shiga ka titsiye yarinya ka biya baƙatun ka; sai ya zamana Allah ba azzalumin Bawan sa bane ya nuna maka Iyakan ka, sannan ita ɗin Matarka ce, kai ko ba Matarka bace tunda har ka iya keta mata mutunci dole kai zaka aure ta, tarbiyyar da muka baka kenan ko SHAREEF?" Sai ta girgiza kanta tana jin zuciyarta na zafi musamman yanda ta ga yana kukan bilhaƙƙi da gaskiyar sa, sai ta daka masa tsawa tana furta, "zaka rufe mana baki ko kuwa? Uban wa kake yi wa kuka a nan?"

"Momy wlh bani nayi mata ciki ba, yarinyar nan sharri take min, yarinyar da na tsana..." Sai kuma yayi shiru yana haɗiye yawu tare da duƙar da kansa ya ci gaba da zubar da hawaye zuciyarsa kamar zata fashe

Momy koma wa tayi ta zauna tana kaɗa kafafu cike da tsananin takaici da haushin sa, ta rasa ma me zata ce don baƙin ciki, wai ga shi ƙiri-ƙiri abu ya bayyana yana ƙaryata su, ji take yi tamkar ta fashe da kuka; idanunta tuni sun kaɗa sun yi jazur

Fahimtar hakan yasa Dady ya dube ta yace, "Kinga Deeja, ki dena irin wannan fushin kina bari ranki yana ɓaci a kan abu ƙalilan, kin san dai kina da hawan jini bai kamata kina yin abun da zai tayar miki dashi ba."

Kamar jira take yi sai ga hawaye sun soma zubo mata, sai ta rufe fuskarta da tafukan hannunta tana jan shashsheƙa, kana kuma ta buɗe lokaci guda tana kallon wurin da SHAREEF yake, tare da nuna sa da yatsa tace, "Alhaji SHAREEF yake so ya nuna mana zai gagare mu, a kan abun da bai fi ƙarfin shi yayi mana ba, ashe akwai ranan da SHAREEF zai iya bijire mana? Ashe yana mana kallon da bamu kai ba bamu isa dashi ba?..."

"Khadijah na ce ki yi shiru ko, yanzu wannan hawayen da kike zubar masa ba ki san tamkar baki bane a gare sa, ba na so ki share hawayen ki nace." Yayi maganar cikin ɗaure fuska babu wasa a tare da shi,
"Kaima ka dena kukan nan na gaji da jin sa, kayi min shiru yanzun nan." Ya daka masa tsawa

Sanin halin Dadyn nasu bai iya fushi ba, shiyasa dukka suka bi umarnin sa,
Yayinda Falon ya ɗauki shiru kamar babu kowa

SHAREEF ya kasa tashi bare ya bar wurin sabida yanda jikinsa ke faman rawa tamkar zai haɗiye zuciya ya mutu don baƙin ciki da ƙuncin da ya cinkushe masa maƙogwaro. A kanta; a kanta komai yake faruwa, ita ce sila na son ruguza masa farin cikin sa, a kanta Iyayensa suna jifan sa da muggan kalamai, a kanta Mahaifiyarsa take zubar mishi da hawaye; wanda bai taɓa ganin hakan ta kasance ba, taya ya zai ƙaunace ta? Ba ya jin zai iya yafe mata har abada

Hango Maryamu da Dady yayi shiyasa yayi shiru bai yi maganar da yake son furta wa ba; yayinda yake kallonta cike da tsantsan mamaki gami da al'ajabi, har datse baki yayi wurin ƙoƙarin sa na furta sunan ta

Hakan ne yasa da sauri Momy ta juya itama tana kallon inda yake kallo, itama mamakin ne ya kusa kashe ta tayi saurin tashi a kan ƙafafunta

Sakamakon ganin Maryamun da suka yi cikin ta ya kumbura; tamkar na mai cikin wata bakwai, ita kanta hankalinta a tashe yake shiyasa ta fito a sukwane tana ƙoƙarin kiran sunan su; but harshenta ya karye ta kasa sarrafa shi, idanunta sun kaɗa sun yi jazur; sai kawai ta zube a wurin babu ko numfashi a tare da ita

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un..! Maryam." Momy ta kira sunan ta hankali a tashe ta nufi wurin ta

Haka shima Dady jiki na ɓari ya take mata baya suka nufi inda ta zube

Shi SHAREEF tunda yayi musu duba ɗaya, ya ɗauke kansa ya miƙe yana jin jiri na barazanar ka dashi, haka ya riƙe kansa da ke tsananin sara mishi kamar zai cire, hanyar ɗakin sa ya nufa batare da ya bi ta kansu ko ya damu da ganin halin da yarinyar take ciki ba; cuz Allah -Allah yake yi ya bar wurin ma sabida tsananin baƙin ciki da tsanarta da ke taso masa, burin sa kawai ya gansa a ɗakin sa ko zai samu salama daga azabar da yake ciki

Su Momy tashin hankali bai sa sun kula da SHAREEF ba, halin da Maryamun take ciki ya ɗimauta su tare da saka musu wasi-wasin ganin yanda cikin nata ya kumbura yayi ƙato

Dady ne yayi ƙarfin halin furta, "matsa in ɗauke ta mu kaita saman kujera, da alamu akwai matsala; kina ganin cikin da nake gani a jikinta?"

Momy tace, "nima abun da nake gani kenan, tabbas akwai abun da ke faruwa Alhaji, yakamata mu kira Malam ya duba ta, sabida ka san ina zargin dama tun farko tana da mutanen ɓoye."

Ɗaukar ta yayi ya kaita saman dogon kujera ya shimfiɗa ta, har yanzu ba ta motsi tamkar gawa. Sai ya dauko wayansa yayi dealing Malamin da ke bata rubutu tana sha

A sa'ilin Sadiq ya shigo gidan ya tarar da su a wannan halin, hankalin sa shima a tashe yake kallon yanda cikin Maryamun ya kumbura, a rikice ya dubi Momy yana tambayarta, "what's going on?"

Kasa ba shi amsa tayi; sai neman wuri tayi ta zauna tana kallonsa idanunta jawur but ta ƙi ce masa komai

While Dady kuma da ke wayan; bayan ya gama ya kalli Sadiq da sauri yace masa, "Sadiq maza ajiye Jakar; ka tafi gidan Malam Abdu ka ɗauko sa yanzu yana jiran ka."

"To Dady." Ya amsa mishi yana ajiye Jakar kamar yanda ya ba shi umarni, ya fita da hanzari

Su kuma suka zauna zugum-zugum kowannen su yana cike da al'ajabin wannan al'amari, sun kasa ma ƙwaƙƙwaran motsi bare su suyi wata magana a tsakanin su, sai kallon Maryamun suke yi sun zuba mata ido sun yi jigum da tunanin abun da zai biyo baya.
***

        
_____After Malam Abdu ya zo, bayan ya zauna yake kallon Maryamu, kallo ɗaya da yayi mata ya gane tabbas tana fama da mutanen ɓoye ne, amma bai ce komai ba sai da ya tambayi Dady duk abun da ke faruwa

Nan ya sanar masa tun daga result da Likitan ya basu, har kawo yanzu daga fitowar ta suka ga cikin ta a haka, da kuma zargin da suke yi a kan ɗansu ne yayi mata cikin tunda haka tace Maryamun

Sai da ya saki ɓoyayyiyar ajiyar zuciya ya sake kallon inda Maryamun ke kwance tamkar gawa, sai yace, "alal haƙiƙa abun da nake gani a nan Jinnul Ashiq ne suka shafi yarinyar nan, muddin suka kasance suna saduwa da ita dole zasu riƙa zuwa mata da siffofin mutanen da ta sani ne, wasu yana faruwar musu a mafarki ne, wasu kuma yana faruwar musu kamar zahiri, to idan har ba a dauki mataki ba abun zai ci gaba da tafiya, daga ƙarshe zasu hana kowacce Mace jin daɗin Mijinta muddin tana da aure, zasu cire mata sha'awar Miji sai wannan mafarkin da take yi shi kaɗai ne zai riƙa mata dad'i, wasu ma kafin su yi aure; daga zaran manemi ya zo wurin yarinyar, zasu yi ƙoƙarin koransa, daga nan ne fa zaka ga wasu Matan sun kasa auruwa sabida suna tare da wannan matsalar, babbar cuta kenan, ina ganin wannan ba wata matsala bace, duk da ban taɓa ganin irin nata zahiri ba. Sau da dama suna haihuwa da bil'adama amma a zahiri ba a ganin Yaran; su kaɗai suke ganin cikin sannan Yaran ma su kaɗai suka san dasu, amma kuma abun mamakin ita a zahiri abun ke faruwa, tunda ga ciki nan a fili."

Sosai bayanin Malam Abdu ya sake ɗaga musu hankali, gaba ɗaya sun yi shiru damuwa ce fal a kan fuskokinsu; yayinda zuciyoyin su ke cikin tashin hankali mara misaltuwa

Bayan ya gama musu bayanin ne; sai Dady yace, "don Allah Malam a san yanda za a yi a taimaki yarinyar nan, muna cikin tashin hankali matuƙa."

"Babu komai wlh, komai ka ga mafarin sa akwai ƙarshen sa, bare aljanu ne dole ayar Allah zai yi tasiri a kansu, don haka ku kwantar da hankalin ku, insha Allahu bi'iznillah yarinyar zata samu waraka, zan yi duk yanda zan yi wajen raba ta da su."
Nan ya saka aka kawo mishi ruwa a cup, ya soma addu'o'i tsawon lokaci bai dena ba, ya jima yana yi wanda ya ɗauke shi tsawon awanni kafin ya basu ruwan yace, "a zuba a gora a ajiye, kullum a riƙa shafa mata a cikin da saman kanta sau biyu a rana, insha Allahu ko me ke akwai da yardan Allah zamu ga sauƙin lamarin, idan ma akwai wata matsalar zan sake dawowa in Allah ya yarda, Allah ya bata lafiya."

"Amin ya Allah." Dukkan su suka amsa

Sai kuma ya sake cewa, "su samo littafi ya faɗa musu wasu addu'o'in da zata riƙa yi kullum da dare, idan baza ta iya ba ana karanta mata kowanne dare."

_Aya ta ɗaya zuwa goma cikin suratul Kahf.. sai kuma ƙarshen Suratul mu'uminun... Aya 54 zuwa ta 56 cikin suratul A'araf, sannan ta karanta wannan addu'ar kamar haka; Allahumma inni a'uzu bika min sú'i ahlami, wa'astajiruka min talaubish shaiɗan fil yaqzati wal'manàmi..._

Daga bisani Dady yayi masa godiya sosai, sai ya tashi ya raka sa bayan ya kira Sadiq yace, "ya zo ya mayar da shi gida."

Suna fita Momy ta ɗibi ruwan ta soma shafa mata a cikin nata, sannan ta cire ɗankwalin kanta shima nan ta shafa mata, but ko gezau Maryamu bata yi ba, a tunanin ta zata ga ta farka,
Shi yasa ta zauna shiru tana kallonta yayinda take ƙara jin tausayin ta,
Bayan Dady ya shigo take kallonsa da faɗin, "Alhaji hankalina ya kasa kwanciya, har yanzu bata motsa ba kuma na shafa mata ruwan."

"Deeja mu jira mu ga abun da hali zai yi, tunda Malam ya faɗa mana abun da ke damun ta; kuma kika ga ga abun da ya bayar, muyi mata abun da yace kawai, ciwo faraɗ ɗaya yake shiga; sauƙi sai a hankali, Allah zai bata lafiya."

Ta amsa mishi da Amin hankalinta na a kan Maryamun

"Yanzu abun da ya dace, sai ta koma ɗakin ki da zama don bazai yiwu mu bar ta a ɗaki ita kaɗai ba, sai ki riƙa taimaka mata addu'o'in ke ma kina mata, insha Allahu komai zai wuce."

"Allah yasa." Tayi maganar tana jan numfashi

A taƙaice dai haka suka kwana a wannan ranan cikin damuwa da zullumi, Maryamu bata farfaɗo ba tana nan a yanda take, abun duniya ya dame su matuƙa, amma sun tsaya su ga ikon Allah zuwa safiya

A washe garin ma da ta farka; jikin babu sauƙi gaskiya a yanda suka gani, tunda ko um bare um um ba ta cewa, tana kwance sai yanda aka yi da ita, shiyasa Momy ta dage da yin mata addu'o'i sosai tana shafa mata, wasu kuma ta bata, har yanzu dai jikin babu dad'i, ga zafin jiki kamar garwashin wuta, ƙarshe ma in ta rufe ido ta dinga barci ba ta farkawa sai ta jima tana barcin

Sai da Malam ya sake dawowa ya duba ta; yace, "su ci gaba babu wata matsala, a hankali zata samu sauƙi, da alamu Aljannun ba ƙananu bane; bayyanar su zai yi wuya, sun rigada sun jima a jikinta."
Ya daɗe yana mata karatu don ma ya tabbatar ya gani ko zasu bayyana; but sun ƙi bayyana, sai kuka da take yi tana ihu kamar ana yanka ta,
Har ya gaji ya dena karatun ya basu wasu addu'o'in yace, "a ci gaba da mata."

Duk wannan bidirin SHAREEF yana ganin abun da ke faruwa amma bai taɓa magana ba bare ta ba shi tausayi, don har yanzu ganin baƙin ta yake yi; tunda har ta iya masa sharri to kaɗan ma ta gani, bai taɓa jin ɓurɓushin tausayin ta ba, tuni ya koma aikin sa don ma kar ya ci gaba da zama a gidan yana ganin abun takaici, tunda yanzu Momyn ma fushi take yi dashi har yanzu ta ƙi saukowa, ko gaisuwar sa sai ta ga damar amsa mishi, Dady ne kawai bai canza mishi ba. Abun yana damun SHAREEF, shiyasa the more yana ƙara jin tsanar Maryamu a ransa ne, sanadiyyar ta mahaifiyarsa ta ɗauki tsawon wannan lokacin tana fushi dashi; babu magana mai daɗi a tsakanin su, har yanzu kuma yana nan a kan bakan shi don ya rigada ya saka a ransa bazai taɓa zama da
End Ads