x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 1 - SHAREEF SEXY BOY BOOK 1

  • 1 words
  • 3000 words
  • Out of 152447 words

Category: Romance Story +18

Views 364

25 Jul 2025
Start ads
After Image Ads

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[04/01, 11:59 am] OumƊahirah نفيسة: 🌱🌱🌱🌱🌱

      *SHAREEF*
             _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱


_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

       *P.W.A✍️*










__________
*BOOK1*
_______________*FREE PAGE1to2*
             Malam Sama'ila Abashe; Mutum ne mazaunin Zaria cikin anguwan Ƙofan kibo, sana'ar sa shi ne jan babban mota, yana bin babban Motan ɗan gote. Shi yasa kodayaushe ba wai ya cika zama bane, idan ya tafi wurin sana'ar sa ya kan yi fiye da watanni uku before ya dawo. Ya jima Allah bai sa yayi aure ba; don sai da yakai aƙalla shekaru arba'in sannan Allah ya ba shi Matarsa wacce ya aure ta a gida, bazawara ce kuma yar uwansa ne, tunda tayi aure bata taɓa haihuwa ba har Mijin ya rasu, bayan fitowan ta shi kuma yace, "yana sonta zai aure ta."

Kowa a dangi yayi murna tunda bai taɓa zancen aure ba sai a wannan karon, ko an kawo mishi Mace ba ya auren ta sai ya gudu zuwa Legos idan aka matsa mishi, a haka dai yake shashantar da zancen har ga shi da lokacin yin sa yayi, dama aka ce aure lokaci ne, baza ka taɓa yi ba idan har ba lokacin ka ne ya zo ba. Ga shi sai a wannan karon Malam Sama'ila ya samu Samira ya aura

Sun yi aure cikin rufin asiri tunda Allah yana buɗa mishi sosai, baya ga jan Motan yana sana'o'i na siye da siyarwa a can inda suke zaune. Yanzu haka ya gina sabon gidan sa a nan Ƙofan Kibo sun tare da Matarsa. Suna zaune lafiya babu wani CeCe-kuce a tsakanin su, suna mutunta junansu matuƙa tare da taimakon juna, domin tunda aka yi auren Samira take ɗan saye da sayarwa na kayan miya. Shima tun lokacin da yayi auren ya rage daɗewa a can garin, ya kan yi wata ɗaya ko fiye sannan ya dawo, zaman su son Barka kowa yana sha'awar su

Abun da suka soma fuskanta shi ne rashin haihuwa, tunda tun sanda aka yi auren yau kimanin shekaru biyu kenan Samira bata haihu ba, ga shi Allah ya zuba mishi son ya'ya tunda yayi auren nan. ya kan ce, "yana son ganin ƴaƴansa tunda yanzu lokacin sa ya soma tafiya, ya fara manyanta ga shi bai yi aure ba sai Yanzu."

Yanda yake damuwa shiyasa itama Samiran ta soma damuwa, tunda ta san cewa daga ita ne matsalar kasancewar tayi wani auren bata haihu ba. Malam Sama'ila bai fito fili ya gaya mata wata magana mara daɗi da zai tayar mata da hankali ba, amma a yanda take ganin shi da kuma yanda yake ƙaunar yara, bai da zance sai maganar haihuwa, ga yawan damuwa a kan fuskarsa shiyasa ta gane halin da yake ciki, kuma ta san tabbas ya damu da ya ga ƴaƴan sa. Shi yasa a wata rana ta zaunar da shi tayi masa maganar ƙarin aure, tace, "ita a ganin ta tunda ba ta haihuwa bai kamata ya zauna haka nan ba, ya ƙara aure domin ya ga ƴaƴansa, ita ta yarda ta amince ya auro ko wace ce."

Da farko bai amince da maganar nata ba, har an shafe kusan rabin shekara da tayi mishi maganar. Ganin ta matsa da zancen dole ya amince yace mata, "shikenan zai nemo."

Su ma iyayensa sun ba shi goyan baya tunda hakan shi ne maslaha, bazai zauna babu ya'ya ba dole ya nemi wata, duk da wannan ƴar uwansa ne amma ba an yi don a wulaƙanta ta bane, bare suna matuƙar ƙaunarta kasancewar ta mai hankali da natsuwa, akwai son jama'a da  faram-faram.



               Da yin maganar bai fi wata uku ba ya samu Mata a nan A.B.U Samaru, sai dai ita budurwa ce kuma yarinya ce sosai, Allah ya haɗa su a can Kano lokacin ta je hutun makaranta wajen ƴan uwan Babanta. Dayake kuma tana son shi shiyasa nan da nan ta ba shi dama suka soma soyayya, basu jima ba ya tura gidan su tunda shi ya ƙosa ya ƙara auren

Sai dai iyayenta sun ce, "sai dai ya jira har ta ƙarisa karatun ta tunda bai fi wata biyar ba."

Kuma ya amince, shiyasa ya nemi a saka ranan auren zuwa lokacin. Aka saka ranan auren ya ci gaba da neman ta

A hankali - a hankali biki ya zo tunda komai aka saka mishi lokaci zuwa yake yi. Aka sha biki Amarya Bilkisu ta tare

Allah da ikon sa kuma sai suka fara zaman lafiya da Samira sosai, tamkar Ƙanwa da Yaya tunda Samiran tana da hankali matuƙa, bata ɗauki Bilkisu a matsayin kishiya ba sai Ƙanwarta kasancewar ta girme mata, ta riƙe ta da amana sun zauna lafiya. Haka itama Bilkisun tana girmama ta kamar mahaifiyarta, komai ita take mata ba ta barin ta tayi komai, idan ka shigo gidan za ka yi tunanin uwa da ƴa ce tsaban biyayya da girmama juna

Kowa yana cewa, "Sama'ila yayi dacen Mata." Tunda kowa sha'awar su yake yi. Duk yanda Mutane suka so su shiga tsakanin su abun ya faskara tunda soyayyar junansu a jinin su yake

Allah da ikonsa da shigan Bilkisu ta samu ciki, sai dai kasancewar ba mai laulayi bane shiyasa basu gane ba sai da yayi kusan watanni biyar. Sun yi murna matuƙa tunda har sun cire rai a tunanin su shima Sama'ila yana da matsalar ne. Nan aka je asibiti da ita aka duba ta komai Lafiya, daga nan ta ci gaba da zuwa asibitin tana awo

Daga lokacin kuma Samira ta amshi komai na gidan ita take yi, ta hana ta komai tace, "baza ta sake yin aiki ba sai ta haihu."

Amma Bilkisu ta ƙi yarda tace, "tunda cikin ba mai wahalar wa bane Ita dai ta barta ta riƙa yi, shima ƙarin lafiya ne ga cikinta tunda motsa jiki zata yi."

Shi yasa Samira ta ƙyale ta tana yin wasu abubuwan, amma ba masu wahala ba

Cikin ikon Allah lokacin haihuwa ta haifi ɗanta namiji sak irin Babansa kamar an tsaka kara. Zo ku ga murna a wurin familyn nan, domin kowa yayi murnar zuwan Yaron nan duniya, tamkar ba a taɓa haihuwa ba a dangin su saboda ƙauna

Sai dai kuma Allah yayi nufin Malam Sama'ila bazai ga girman Yaron sa ba, yanda yayi murnan zuwan Yaron nan ko abinci ba ya iya ci tsaban bai da lokacin kansa sai na yaron, wuni yana hannunsa tunda aka haife shi. Ana gobe suna aka kira shi a kan an yi mishi lodi. Farko yace, "bazai je ba saboda gobe ne sunan ɗansa." Amma Matansa suka dage sai ya je tunda idan bai je ba zai iya samun matsala, ƙarshe ya rasa Motan ma, shi kansa ya san da haka, but tsaban ƙaunar ɗan shi ne yasa ba ya son ya jirga ko nan da can. Shi yasa da suka matsa mishi sai yace, "to shikenan tunda kun matsa zan je, amma bazan wuce sati ɗaya ba in sha Allahu zan dawo. Ga Yarona nan kafin in tafi zan bada kuɗin rago, zamu yi magana da Yaya Shehu komai na sunan zan ba shi, Yaro na raɗa mishi Ahmad Allah ya raya shi."

"Amin Amin." Suka amsa mishi cikin farin ciki. daga nan suka sake sallama dashi sannan ya bar gidan bayan ya haɗa ƴar Jakar shi

To tafiyar kenan wanda basu kai can inda zasu je ba; Allah yayi mishi cika wa sakamakon mummunan hatsarin da suka yi, ko gawan su ba a samu ba sai toka

A sanda labari ya riski Matan sa sai suka yanke jiki suka faɗi a nan take. Aka yi da su asibitin Ƙauran Wali domin basu taimakon gaggawa. A can jini ya ɓalle wa Samira ashe itama cikin take dashi, wanda babu wanda ya sani sai Allan da ya ɓoye kayan sa, ko ita bata san cewa tana da juna biyu ba ashe har ya kai wata Bakwai. A take a nan ta soma naƙuda cikin wahala ta haifi ɗiyarta Mace

Lallai Allah gagara misali ne, mai raya wa kuma mai kashe wa, ga shi ya ɗauke Uba ita kuma ƴa ta zo. A sanda ya amsa sannan yayi musu kyauta

Hakika babu wanda bai ji mutuwar Malam Sama'ila ba, su kansu Matan shi an rasa kansu domin ba kaɗan ba mutuwar tayi muguwar ratsa su, musamman ma Samira; tunda ita sai da tayi kusan kwana goma a asibitin tana fama da kanta, haihuwar ta zo mata da matsala sosai, ga kuma rashin Mijinta wanda yasa ta damu ta kasa kwantar da hankalinta, tayi jinya sosai tunda hawan jini ne ya kama ta. Daga baya aka sallame ta

Already an sanya wa yarinyar suna Hafsah duk da babu wanda aka yi suna. Daga Ahmad har Hafsan, mutuwar Mahaifin su yasa aka jingine sunan, sai dai an yi kokari an yanka musu rago. A haka har aka yi arba'in na mutuwar sannan suka yi takaban su

Bayan sun gama. Bilkisu ta ƙi komawa gida kamar yanda iyayenta suka so ta tafi. A cewar ta, "zata zauna da Yaya Samira ba ta son rabuwar su." Amma yanda iyayenta suka hura mata wuta a kan dole sai ta komo gida; shiyasa ba don ta so ba tabar gidan. Sai dai sun sha kuka kamar baza su rabu ba, shaƙuwar su yasa sun ji ciwon rabuwa ba kaɗan ba

Koda Bilkisu ta tafi hakan bai sa sun watsar da zumuncin su ba, akai-akai suna ziyartan juna har lokacin da iyayen Bilkisu suka sama mata gurbin karatu a can Kano, zata koma wurin yan uwan Babanta sai ta ci gaba da karatun a can, sun so su amshi Ahmad ita ta tafi ita kaɗai, amma furr ta ƙi yarda, haka ta tafi dashi bayan ta je ta yi wa su Samira sallama

To sanadiyar tafiyanta kenan, tunda a can ta samu Miji tayi auren ta, ko rufa shekara bata yi ba Allah ya kawo mata Miji. Haka nan ta yaye yaron ta koma gidan Mijinta, kuma dashi ta tafi tunda sai da suka yi yarjejeniya da Mijin; da ɗanta zata tafi

Su ma ƴan uwan Malam Sama'ila basu taɓa yunƙurin karɓan Yaron ba, sun bar mata shi duk sanda ta tashi kawo shi don kanta sai ta kawo shi

Ita kuma Samira bata sake aure ba illa ci gaba da tayi da kula da ƴarta, ta koma yin sana'a kala-kala domin taimakon kanta da ƴarta. Duk da ta samu waɗanda suka ce zasu aure ta but ta ƙi, domin kwata-kwata a yanzu ba ta buƙatar wani auren, gani take yi kamar idan ta kuma yi Mijin zai sake tafiya ya barta, aure biyu kenan tana rasa su, baza ta iya ba a wannan lokacin. Haka nan ta ci gaba da rayuwarta duk da ba wai zumuncin su ya taɓarɓare bane da Bilkisu. Duk sanda ta zo Zaria wurin iyayenta tana ƙoƙarin ziyartan ta

Samira ta ci gaba da kula da Hafsah tunda kasancewar yarinyar bakwanyi ne tana matuƙar tausaya mata. Ga soyayyarta da Allah ya dasa mata, tana sonta sosai duk abun da take so shi take mata. A haka har tayi karatun ta ta gama ta shiga makarantar nursing. Allah da ikon sa tana da shekaru goma sha tara a wannan lokacin ta samu Miji

Sai dai fa Mijin asalin sa ɗan ƙauye ne mazaunin garin Kugu. Amma yana aiki a nan cikin Zaria. Allah ya haɗa soyayyarsu shiyasa ta manne mishi kamar chewing gum

Duk yadda Samira ta so ta raba su tare da nuna mata illar auren sa, tunda a ganin ta tana yar birni kuma tana karatun ta mai zai sa ta koma ƙauye? Ta taso a cikin gata zata ƙare a wahala

Amma sai Hafsah ta dire a kan dole sai shi. Kuma tace, "ai yayi mata alkawarin a nan zasu zauna, bazai kaita can ba."

Shi yasa sai Samira ta barta tunda ita ta zaɓa haka, amma ta so ta hana kasancewar hankalinta bai kwanta ba, ba ta son ƴarta tilo ɗaya wacce take matuƙar kauna ta ƙare a wahala

An saka ranan auren nan da wata shidda, yayin da Hafsan ta ci gaba da karatun ta tunda a lokacin saura shekaru biyu ta ƙare

Tun ana saura kwana biyu Bilkisu ta zo tare da Ahmad da Ƙannin sa biyu Mata da ta haifa, shima Ahmad ɗin ya girma ya zama ɗan Saurayi, yanzu yana karatu ne a can BUK yana aji na biyu, dayake duk sa'annin juna ne da Hafsan tunda kwana shidda ya bata, shiyasa suke wasa sosai da ita, ta ɗauke shi tamkar Abokin ta domin wani lokacin har rigima suke yi idan tace, "baza ta kira shi da Yaya ba, wai ai shekarun su ɗaya bai girme ta ba."

Ƙanninsa su yi ta musu dariya suna kallon draman su, idan ka zauna da su dole su ba ka sha'awa, kallum cikin rigima suke yi suna musu ga junan su, wata rana har sai Inna Samira ta tsawatar musu tana yi wa Hafsan faɗa a kan, "koda awa ɗaya ya riga ta zuwa duniya ya girme ta, dole ta girmama shi."

Ita kuma tayi ta kumbura baki tana fushe-fushe a kan bata yarda ba, dayake akwai ta da rigima kasancewar yanda Inna Samira ta raine ta cikin gata da sangarta

To an sha biki har Hafsah ta tare a gidanta a nan ɗan Magaji; inda Mijinta Haruna ya kama haya. Gida yayi kyau Masha Allah duk da ba ita kaɗai bane a gidan, su uku ne kuma dukka Amare ne, ɗaya tana da ɗanta ɗaya, ɗayan kuma bata haihu ba, ga shi Hafsan ta samu kaya ba kaɗan ba, komai an yi mata na ƴar gata ne

Bayan bikin; su Ahmad suka koma Samaru gidan Kakannin shi, daga can ne suka wuce Kano

Rayuwa ta miƙa, ga shi har Hafsah ta gama karatun ta amma Allah bai bata haihuwa ba, duk da dama an ce ana gadon uwa na rashin haihuwa, idan Mahaifiya itama tayi jinkirin haihuwa ƴaƴanta ma suna gado. To ga shi Hafsah a yanzu tana neman shekaru na uku da aure Allah bai sa ta haihu ba

Kuma a wannan lokacin ne ta soma fuskantar matsala tunda iyayen Haruna sun matsa mishi sai ya ƙara aure, sannan kuma sai ya dawo da Hafsan ƙauye itama ya haɗa su da Matar. Dayake ya siyi fili a can har ya soma gini, shiyasa suka ce mishi, "dole sai ya dawo da ita nan, idan bata dawo kusa da su ba taya zata san ƴan uwa?"

Duk yanda ya so ya fahimtar da su a kan Hafsah ƴar birni ce bata saba da irin rayuwar can ba, amma sun kasa fahimta, sun matsa mishi sosai dole yayi abun da suke so

Dayake itama Hafsan ba baƙuwar zafi bace kuma tana son Mijinta, shiyasa ta amince ta bi shi, yana gama ginin ta koma, a lokacin kuma har an saka mishi rana da wata ƴar uwan shi

Gidan sa yayi matuƙar kyau domin duk ƙauyen babu mai kalan gidan sa, dogon gini irin na ƴan birni yayi kuma da bulon sumunti, sannan ko'ina ya sha filasta ga pentin zamani, kana doso ƙauyen da gidan za ka soma cin karo tunda ya fita daban ne, ya haska ƙauyen sosai, kowacce da sasanta yayi musu ciki bibbiyu, sai shima nashi da kuma safayan daki, sai kuma wani ɗakin na kaji tunda yana kiwon kaji

Gab da bikin kuma Hafsan ta soma laulayin ciki, cikin mai wahala ne ga tsurfa; amma haka nan ta jure tana
End Ads