x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 21 - NA KASA JUREWA book 1

  • 60001 words
  • 63000 words
  • Out of 86738 words

Category: Love Stories

Views 143

09 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
da kuka a tare, tsohon ya ɗaga musu hannu kana yace "godewa Allah ya kamata kuyi, bai kamata kuna kuka ba, ya ƙwalawa yarinyarsa kira wacce bata wuce sa'ar Najma ba, sannan ya ƙwalawa yaronsa wanda Majeed ma zai girme masa kamar da shekara ɗaya, yace "a basu ruwan wanka da abinci, shi namjin ya bawa Majeed kaya, ita kuma macen ta bawa Najma kaya, suka amsa da cewa "to"...
KANO
ana gobe birthday party ɗin Laurat, Aysha ta gayawa anty Tasneem da Umaimah, bata hanata zuwa ba, hasali ma har tambayarta tayi mai zata kai wa ƙawar Tata a matsayin gift, Aysha tayi shiruuu, sboda bata sam mai ya dace ta kai mata ba, anty Tasneem tace "gobe idan Allah ya kaimu sai in baki abinda zaki kai mata, "Umaimah zakije koh?" Aysha ta tambayeta,
"Eh man zuwa sosai ma"
Umaimah ta bata amsa, wunin ranar dai sunata tsara irin shigar da zasuyi, kai kace sune masu yin birthday ɗin,  yau kusan kwananta uku bata kunna wayarta ba, Umaimah tayi tayi akan ta kunna saboda kar Zayden yayita tunanin ko bata cikin ƙoshin lafiya amma fur taƙi sai yau, kamar jira yake yi, ta kunna wayar, aiko sai ga kiransa tare da text message, kiran nasa ta ɗaga, cikin sanyaya murya, "amincin Allah ya tabbata ga masoyiyata abin alfaharina, ina fatan dai kwana biyu lafiya?"
"Uhm lafiya lau"
"Mai yasa wayarki bata shiga,"
"Haka kawai"
"Kinason ki azabtar dani ne?"
Ta fashe masa da kuka mai sauti, da sauri ya kalli wayar dake hannunsa kana ya kara a kunnensa kafin yace "Please beauty ki gayamin meke faruwa?"
"Zayd ina sonka, bani da damar da zan iya furta maka hakan"
Ta katse kiran tare da ajiye wayar, dariya ta farayi ga hawaye na, zuba, ta share hawayen, tare da kallon gefenta taga babu kowa, hamdala tayi kana ta tashi ta shiga toilet ta ɗauro alwalah kana ta shimfiɗa sallahya sannan ta kabbara sallahar magriba, tana cikin yin Sallah sai ga Umaimah ta shigo, da alamu daga can parlorn ta ɗauro alwalah, itama ta kabbara sallah, bayan sun idar sunyi addu'oinsu, Aysha ta kalli Umaimah, kafin tace "kinsan me?" Umaimah ta girgiza kai, Aysha tace "wlhi har tunanin ranar da zan koma gidan Hajiya nakeyi, babbar damuwata yah Ma'aruf, bashi da mutunci ko kaɗan"
Umaimah tace "uhm na taɓa ganinsa sau ɗaya a wata hira da akayi dashi a TV, wlhi bana fata in ganshi a zahiri, saboda Guy ɗin akwai kwarjini sosai, ga shi Ubangiji ya haɗa masa komai duka, ance ɗan adam tara yake bai cika goma ba, nikam a ganina wannan bawan Allahan ya cika ɗari ma, ga kyau ga kuɗi ga izza wow amma fa tsoronsa nakeji" Aysha tayi murmishi kana tace "wato Umaimah, babbar damuwata komawa gidan, kamar dai yadda na gaya miki, dalilin da yasa na fara tunani, hamm uncle Junaid ya kusa dawowa kinga anty Tasneem bazata barmu a gidannan ba, i swear" Umaimah tace "faɗi ki ƙara barinma kekam da zaki sace zuciyar duk wani lafiyayyen namijin da yayi tozali dake" Aysha ta zaro idanu tare da cewa "wlhi sharri dai babu kyau"
Umaimah tace "wlhi gaskiya nake gaya miki lokaci ɗaya kika wani cika, ƙila baki ga hips ɗinki bane ko?  One Month nazo gidannan lokacin ma ƙirgen dangin da kika farayi ƙanana ne, ga shi yanzu har ana saka bra, uwa uba 3 weeks ago kika fara period, hmm ai dole ki fara tunanin makomarki, amma ya maganar makarantar ki fa?" Uhm Umaimah, alhmdulilah insha Allah na koma Abuja zan ci gaba, amma nafison mai haɗe da islamiyya" Umaimah tace "ai karatun addini yanada kyau sosai, haɗuwarmu zatayi wuya sai dai a waya, wlhi zan gargaɗeki karki kuskura ki nunawa wani wayarnan, idan ba haka ba, wlh sai kin shiga tashin hankali" Aysha tace "hauka nakeyi Umaimah?"
Aysha ta faɗa tana riƙe baki,
Sunsha hira a daren, bayan an kira sallahar isha'i sunyi suka kwanta, wayar Umaimah ta fara ringing, tana dubawa taga Zayden, ta zaro idanu, tare da cewa "Aysha ga masoyinki ya kira, tayi kamar bazata karɓi wayar ba, ta miƙa hannu ta karba tare da karawa a kunnenta, "aslmu alaikum"
Tayi sallama,
"Wlkslm" Zayden ya amsa, daga jin muryarsa ma ta nuna yanayin damuwar da yake ciki,
Kafin yace "beauty dan Allah ina son in roƙeƙi wata alfarma, sannan inason ki gayamin iya gaskiyarki saboda bana son ƙarya.."
In Cold voice tace "ina jinka"
"Aysha kina sona, tsakaninki da Allah?"
"Tayi shiru, kafin tace "eh sosai ma"
Yace "good"
Ya sake cewa "Aysha bana son idan muna magana ki dinga katse min kira"
Cikin sanyin murya tace "bazan sake ba"
A karo na uku ya sake cewa "yanzu meye yake damunki?"
Ta marairaice murya tare da cewa "babu komai"
"Yaushe zamu haɗu"
Kai tsaye tace masa "ko gobe"
Yace "a ina zamu haɗu?"
Ta jujjuya idanu kafin tace "zan kiraka, ƙawata ce zatayi birthday"
Yace "okay, Allah ya kaimu"
Tunda ya katse wayar Aysha, tunani iri-iri ya dameshi, sakamakon sonta da yake neman zautar dashi, duk inda ya zauna sai ya yi maganarta har cikin danginsa da abokansa, shi kasansa ya kasa misalta son da yake yi mata, wanda bai taɓa yiwa wata mace a faɗin duniya ba"
Itama a nata ɓangaren haka ne, soyayyar Zayd ta fara nisa a zuciyarta.
Har Umaimah tayi barci tana rungume da wayarta...
Washe gari
Tun bayan da sukayi sallahar asbha suka fara aikace-aikace, daga nan sukayi wanka, already dama babu school sboda malamar su anyi wa wata Malama cs headmastern su shima yana Hospital,
A gurguje sukayi breakfast sukuma masu aikin sukayi moping,
Ƙarfe 9:am abinci ya kammalu aka jere a dinning, sai da suka shirya tsaf, cikin Abaya baƙaƙe, sunyi matuƙar kyau, saboda abayar ta amsa sunanta, duba da ƙyaleƙyalen dake jikinta, duk wanda ya kallesu tabbas sai ya sake kallo, saboda har wani walwali takeyi sukayi rolling veil ɗin a kansu, ba wani abinci mai yawa sukaci ba, tsabar ɗoki da murna, anty Tasneem ta kawowa Aysha wata haɗaɗɗiyar sarƙa mai zobe, da turare mai tsada harda su ribom masu kyau, Masha Allah sunyi kyau sosai, Aysha tayi godiya tare da cewa "anty bakice munyi kyau ba"
Anty Tasneem tace "wlhi kunyi kyau sosai, sukayi hoto,
Tare da yi mata sallama, kasancewar ko wacce ta fito da hand bag ɗinta, anty Tasneem ta miƙawa Umaimah 10k tace ko zasuyi siyi wani abun, sukayi mata godiya kana suka wuce.
Kai tsaye parking space suka nufa, sukayi wa driver kwatancen anguwar da zai kaisu, suka shiga backside yayiwa motar key bayan an buɗe masa get.
Cikin ikon Allah suka iso anguwarsu Laurat har ƙofar gida ya kaisu, suka gaya masa time ɗin da zai dawo ya ɗauke su, ya wuce.
Nocking sukayi a get na gidan, mai gadi ya leƙo tare da cewa "sannunku daga ina?"
Umaimah tace "nan ne gidansu Laurat?"
Da sauri mai gadi ya gyaɗa kai gami da cewa "eh nan ne, amma daga ina kuke, kuyi hakuri wannan tambayar da nakeyi muku tana ɗaya daga cikin sharuɗan shiga wannan gidan"
Aysha tace "babu komai, ta buɗe hand bag ɗinta kana ta ciro wata ƴar takarda sannan ta miƙa wa Umaimah, tace ta kira mata lambar, ringing ɗaya Laurat ta ɗaga tare da cewa waye?" Aysha tace "gamu a ƙofar gidanku"
Cike da murna Laurat ta katse kiran tare da fitowa harabar gidan tana yiwa mai gadi magana akan ya buɗe musu get, bayan ya buɗe musu suka shigo, wow, hmm masu karatu gidan fa Masha Allah komai yayi, hatta motoci biyar ɗin dake jere a gurin ajiyar motoci duk na yayi ne masu tsadar gaske, Laurat tana sanye da gown irin ƴar kanti, kanta yasha gyara sai sheƙi yake yi Masha Allah, daga nan tayi musu iso zuwa cikin gidan, babu kowa a gidan, saboda an ɗaga birthday ɗin, sakamakon Dad ɗin ta yace ta bari sai next week, Aysha kuma bata sani ba shiyasa suka zo, kai tsaye ɗakinta ta kaisu, ɗakine babba kai kace ɗakin wata macen, Masha Allah ɗakin yayi kyau, bayan sun shiga suka zauna a wasu ƙawatattun kujeru, Laurat ta fita zuwa kitchen, ta kawo musu sakwara da miyar egusi, da kunun gyaɗa mai ɗumi wanda ya ji coconut da milk,
Bayan ta ajiye musu a saman table ta koma ta zauna, kafin suka fara gaisawa, nan take gaya musu ai an ɗaga birthday ɗin, Aysha ta ciro kayan da Anty Tasneem ta bata ta miƙa mata, sosai Laurat tayi farinciki da wannan tsaraba, saboda a halin yanzu sun shaƙu da Aysha sosai,
Basu wani ci abincin sosai ba, Laurat ta ƙurawa Aysha idanu, A'isha dai da ta gaji da kallon da Laurat keyi mata tace "ke ya dai lafiya?"
Laurat ta sauya mood zuwa na damuwa, kafin tace "Ƙawar Aysha Please sunanki fa?" Umaimah tayi murmishi kafin tace "sunana Umaimah, ni ƴar uwarta ce" Laurat tace "alhmdulilah"
"Dan Allah Umaimah ki taimakeni akan manufata Please ku fahimceni dan Allah"
Sosai ta jefasu cikin alhini duk da basu ji me take son cewa ba,
Laurat ta sakko ƙasa tare da durƙusa guwaiwoyinta ƙasa, ta haɗe hannayenta kafin tace "dan Allah Aysha kiyimin wata alfarma dan Allah"
Aysha tace "Laurat wace irin alfarma ce hakan, da har kika durƙusa min?"
Laurat ta shiga gallery na wayarta ta nuno wani kyakkyawan hoto, wanda wani matashi ne a jikin hoton, shi ɗin ba fari bane, baƙi ne, sannan baƙinsa ba mai muni bane, yanada gashin baki mai kyau, sannan ya gyare sumar kansa, ta nunawa Umaimah, kafin tace kinsan wannan?"
Umaimah ta gyaɗa kai, tare da cewa "wannan ai yayi ambassador a ƙasar waje, kuma har yanzu ana damawa dashi dan na gaban goshi ne, ga kuɗi kamar zai kasheshi" dukkansu basu san me take nufi ba, tace "kuyimin alƙawarin duk abinda nace zaku amince" a tunaninsu wata maganar ko neman shawara takeyi, cikin haɗin baki suka amsa da cewa "zamu amince"
"Laurat tace "Aysha dan Allah ki auri Dad ɗina, shine a jikin hotonnan, ni kaɗai nake zaune a gidannan sai masu aiki, sannan shi bai cika zama a Nigeria ba, sannan yana dawowa Nigeria baya cin abincin waje ko na masu aiki nice nakeyi masa, tun bayan rasuwar mahaifiyata, tana aihuwata ta rasu, wlhi tallahi Aysha baki da matsala da Dad, ƴan uwansa sunyi masa maganar aure har sun gaji dan Allah ki taimakeni"
Laurat ta ƙarshe maganar tana, sake cewa "karki manta keda Umaimah kunyi min alƙawari, sannan Ubangiji yana girmama alƙawari"
Kuka take yi sosai, yayinda Aysha ta daskare a gurin, Umaimah kam ta kasa koda motsa bakinta ne, tsabar firgici, saboda basuyi tunani ko tsammanin jin waɗannan zafafan kalaman daga bakin Laurat ba, ta sake fashewa da kuka tana cewa "Please nasan zaki iya kinada hankali nutsuwa tausayi da duk wani hali na gari da namiji ya kamata ya samu gurin mace, Please say something...!

Tofa, 2days nayi talauci, rashin data yasa banyi muku posting ba, kuyi hakuri dan Allah.

Mom Islam ce 08141799224

*NA KASA JUREWA*
💋💋💋
💋💋
💋
          _Mom Islam_

Page 59-60

Bayan ta gyara bedroom ɗin nata, ta koma ɗakin Alhji Abdullahi, yana kwance kamar inda ta barshi ɗazu, ya miƙe samɓal sai ta ga ya ƙara yi mata tsayi sosai, a hankali ta isa gareshi tare da kai tafin hannunta gurin hancinsa, yanayin da jikinta ya bata, sam ta kasa gasgata hakan, ta sake kai hannu a karo na biyu, a tsorace tace "baya numfashi?" ta fashe da kuka, saboda bata yarda da abinda zuciyarta ke gaya mata ba, da sauri ta koma ɗakinta, kana ta ɗauki wayarta ta danna number anty Asabe, bata ma san anty Asabe ta kirawo ba, murya babu daɗin saurare tace "Salima ya akayi?"
Cikin Muryar kuka Hajiya Salima tace "Anty Asabe dan Allah kizo, dan Allah" takai ƙarshen maganar tana sakin kuka mai sauti,
Daga can ɓangaren anty Asabe sauri ta farayi, adu'ar da takeyi bai wuce ta ji ance nata Alhaji Abdullahi ya mutu ba, a fili tace "baya motsi meye amfaninsa" ta fito harabar gidan sboda dama ita kaɗai ce a gidan sai yaron ƙanwarta da ta rasu ta bari tun yana jariri ga shi yanzu ya zama saurayi a halin yanzu shekarunsa 27yrs a duniya,
"Driver yi sauri kazo ka kaini gidan yayana, tai maganar cikin yanayi na nuna damuwa kai kace har a zuciya, bayan ta shiga mota driver ya tada mota suka fice, kasancewar mai gadi ya buɗe get tun kafin shigarta mota.
Driver na gudu tana yi masa masifa akan ya ƙara gudu ita kam taga yana driving sai kace wani mace, daga ƙarshe ma cewa tayi ya fito a motar ya dawo backside ta yarda ita zatayi driving, abin ya matuƙar bashi mamaki matuƙa, saboda driving ɗin ma bata iya ba, shi yake koya mata, masifarta ta hanata koya,
Ikon Allah ne ya kawosu gidan Alhaji, gida ya cika maƙil da mutane, saboda Hajiya Salima ta sanarwa da maƙota, sai koke-koke akeyi, tun da taga ƙofar gidan an cika, tai saurin fitowa daga mota ba tare da ta gama tsayawa ba, wata irin kururuwa takeyi marar daɗin ji, har ta isa ɗakin da alhajin yake, Hajiya Salima da maƙotansu da ƴan uwanta wanda suke kusa, mama dai har yanzu bata iso ba, sosai take ta gunjin kuka babu kauƙautawa, mutane sai bata haƙuri sukeyi, cikin Muryar kuka tace "Allah sarki Yaseen da Yusra, ko a wane hali suke ciki oho,
Hajiya Salima kam idanunta sun kumbura sosai, tsabar kuka, da jimamin yaranta, ta rasa su, daga shi har ƴaƴansa, sosai takejin rayuwar duniyar ma ta fitar mata a kai,
Bayan anyi masa wanka kana aka yi masa sutura, daga nan aka kaisa gidansa na gaskiya.
Alhmdllh Alhaji Abdullahi ya samu yabo daga bakunan al'umma, babu mai faɗar wani mugun abu sai alkairansa, yayi tashen arziƙi wanda har yanzu ma yana kai, sai kuma yabar duniya, ya gina manya manyan masallatai da makarantun islamiyya duk kyauta, kana yana yawan kaiwa gidan marayu ziyara duk lokacin da yake free, hakan yasa ya samu babbar shaida anan duniya.
Ana kaisa aka fara hada-hadar ɗora abinci, anty Asabe kam kai tsaye ɗakinsa ta wuce, ganin key a ƙofar ɗakin yasa ta kulle ƙofar ba tare da sanin kowa ba, a tunaninta Hajiya Salima ta iya zuwa ta kwashe dukiya ta barta a banza..
KEFFI
yau ta kasance sunday, washe garin biki kenan, sam hankalinta ya gaza kwanciya, gani takeyi kamar Hajiya Zaliha zata iya dawowa, duk da alhajin yana gida, zaune take a saman gado, tana sanye da shadda fara sol anyi mata stone work ɗinkin Abuja Bubu, tayi ɗauri mai kyau wanda ya daɗa ƙawata kwalliyar tata, Masha Allah.
Danne-danne takeyi a wayarta, bata tunanin kiran iyayenta, saboda sune suka yi sanadiyar rusa mata farinciki, tunda akayi bikin bata kirasu ba, sboda ta ajiye simcard ɗin ta a ƙasa, a hankali Alhajin ya murɗa handle na ƙofar kana yai sallama tare da ƙarasowa cikin shiga ta alfarma, yana sanye da shadda milk color sleek sai sheƙi takeyi, a hannu ya riƙo babbar rigar tasa, ta amsa sallamar tare da sunkuyar da kanta, "Habibty gaskiya kinyi kyau" yai maganar yana ƙarasowa inda take, bata ɗago kanta ba, bare ta nuna ta ji abinda ya faɗa, zamansa a kusa da ita ne yasa ta ɗago fararen idanuwanta tare da ɗora su a nata, yai amfani da hakan wajen rungumeta, cikin Muryar tarairaya yace "Habibty nasan kina jin yunwa, idan har drinks ɗin da suke gidannan basuyi miki ba, ki tashi muje restaurant muci abinci"
Tabbas zaman kaɗaici ya dameta, duk da alhajin yana wuni a gida, amma bata wani sakewa suyi hira, ita har yanzu bataji tana sonsa ba, sai dai ta gano yana tsananin sonta sosai, tana son ta koyawa zuciyarta sonsa ya zatayi?"
Amsar ta maƙale mata a ƙasan maƙoshinta,
Rungumeta yayi sosai, kana ya ɗan sunƙuyo da fuskarsa gurin tata fuskar kafin yace "Habibty mai kikace game da fitar?"
"Uhm to"
Saudart ta amsa masa, saboda bata da zaɓi,
Ta zame a jikinsa tare da buɗe drowa ta ɗauki mayafi, ta ɗauko sabon takalminta da Hand bag, da wayarta, wacce babu simcard a ciki, kana ta fito parlor, har yanzu yana mamakin Saudart, duk irin soyayyar da yake nuna mata har yanzu ta kasa fahimtarsa, mai yasa take yi masa haka?" murmishi kawai yayi, kana ya fita a bedroom ɗin nata, kai tsaye ya wuce bedroom ɗinsa, car key da ATM ya ɗauka, kana ya sanya takalmi cover shoe sannan ya fito parlor, tana zaune a ɗaya daga cikin kujerun da suka ƙawata parlorn, tayi nisa a tunani sosai, "Habibty tashi mu tafi.." jin bata ce komai ba, sannan bata motsa ba, yasa shi ɗan risinawa a gabanta bai kai ƙasa ba, yace "Habibty nace tashi mu tafi"
Firgit ta miƙe saboda tayi zurfi cikin tunanin nata, drivernsu na ganin fitowarsu ya fara shirin shiga mota, alhajin ya dakatar dashi tare da cewa "kayi zamanka yanzu zamu dawo"
Driver yayi musu Allah ya tsare, bayan an buɗe musu get securities ɗin suka buɗewa Alhji Murfin mota gurin zaman driver, already Alhji ya buɗe wa Saudart kusa dashi, kai tsaye yayiwa motar key suka bar anguwar,
Driving yakeyi time to time yana kallon fuskar Saudart, cikin rashin sa'a go slow ya haɗu, wata ƙawar Salma ta hango Saudart dake zaune cikin motar Alhji, abin ya bawa ƙawar Salma mamaki, dan bata san yayi aure ba, sbda har hannunsa ya ɗora a saman Saudart, kana ya zuba mata idanu, da sauri ƙawar Salman ta danna number Salma, ringing ɗaya ta ɗaga, tare da cewa "Aminiya ya akayi ne?"
"Ke na rantse da Allah idanuna sun ganemin wani abu, Salma Dad ɗinki tare da wata kyakkyawar budurwa har yana kissing ɗinta a mota gashi go slow ya haɗamu, nikam basu gama isata kallo ba" Salma ta miƙe a zabure, kana ta kalli mahaifiyarta, kafin tace "momy wlhi tallahi Dady ya gama damu, ashe ma yawo yakeyi da amaryar tasa, yanzu fa ƙawata ta kirani" Salma tayi maganar tana fashewa da kuka, tare da ɗora hannu a kai,
Hajiya Zaliha tace "shikenan, wlhi shikenan, mun kaɗe, daga mu har ganyenmu, Hajiya Zaliha tace "barin kira Hadiza inji ya akayi da maganar zuwa gurin malamin da tace zatace "
Salma ta dauki wayar Hajiya Zaliha ta kira lambar anty Hadiza, sai da tayi ringing sau uku ana uku Kafin ta ɗaga "Hajiya ina hanyar zuwa gidanki, yanzu"
Hajiya Zaliha tace "Allah ya kawo ki ina jiranki akwai wata, bura ubar sabuwa"
Hajiya Hadiza tace "shafamin ya akayi?"
End Ads