x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 29 - NAYEL THE RETURN OF EXILED PRINCE

  • 84001 words
  • 87000 words
  • Out of 89550 words

Category: Love Stories

Views 392

14 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
da kayan barcin white color , ya daura hannu saman forehead ya lumshe idanu

a hankali ta karaso bakin gadon ta zauna , ta kai hannu a hankali saman face din sa

cikin nitsuwa ya janye face din sa , ya juya mata baya baki daya
( ๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚ na ga alamun yau su Honey fushi a ke yi )

sai da ya juya mata baya sannan ya ce " me ki ke yi a nan ? , koma wajen sister din ki , ni ki kyale ni barci na ke ji "

Hayewa saman gadon ta yi , ta kwanta gabansa su na kallon juna
yanzu ma a hankali ya sake juyawa ya ba ta baya

rungumo shi kawai ta yi ta baya , cikin sanyin murya ta ce mishi " Honey , please kar ka yi fushi "

" ni ba fushi na ke ba , ba ke ce ki ka kyale ni ba yau baki daya kin manta da ni , ko nema ta ba ki yi ba bare ki san wane hali na ke ciki , amma ba komai , gobe na ke komawa UK "

cike da shagwaba ta ce mishi " I'm sorry Honey , please kar ka tafi ka bar ni , kuma ni ban manta da kai ba , sai da na shigo bedroom din ka na kawo maka lunch kawai na ga ba ka nan , shi ne na yi tunanin ko ka fita "

" Hmmmm , ke dama kullum kin san yadda za ki yi ki kare kanki " ya fada ya na juyowa su na fuskantar juna

ta na ganin ya juyo ta saki wani kyawatacen murmushi ta ida shigewa jikinsa
hannu ya kai ya janyo duvet ya rufe su har zuwa kirji , sannan ya kashe lamps din dakin ya kunna bedside lamps , ya zagayo da hannayansa a bayanta ya rungume ta shi ma
( ๐Ÿคฃ๐Ÿคฃ๐Ÿƒโ™€๏ธ๐Ÿƒโ™€๏ธ na ga alamun yau ba za a yi game ba , to bari na tafi abuna , to bari na dan takaice labarin )


โ˜† AFTER SOME DAYS โ˜†



Haka dai rayuwa ta ci gaba cikin wannan gidan , wajen wata guda yanzu har da kwanaki bayan rasuwar MALIKAT INAS ,
a cikin kwanan nan abubuwa dayawa sun faru , bangaran Prince da Aleesherh , ba su da labarin abun da ke faruwa cikin Daular dan kullum su na part din su manne da juna , cikin kwanan nan har daukar ta ya yi su ka tafi Yemen , ta ga Familynta , ba karamin farinciki ta yi ba , sai da su ka yi kwana biyu a Yemen sannan ya dauke ta su ka tafi Dubaรฏ yin shopping , shi ma sai da su ka yi kwana biyu a cen sannan su ka dawo Saudiya , ba karamar kula ta ke sha ba wajen Prince har ta kara haske ta yi wata yar k'iba
Junior da Princess kuwa , sun fara investigation a kan Faaz , kuma gidan marayu na farko da su ka je shi ne na Ekhaa , amma wani abu , duk yadda su ka so yi musu kwatancen Faaz su ka rufe ido su ka ce ba su ma taba samun yaro me sunan Faaz ba , nan Junior ya tabbatar tabbas maganarta gaskiya ne , duk da haka ba su hakura ba su ka ci gaba da binciken sauran gidan marayun Masarautar ko sun samo wani abu , sai da su ka bincike kab gidan marayun Masarautar ba su samo komai ba , sai a na karshe ne su ka samu wasu information , information din da su ka samu ya tabbatar wa da Junior Faaz tabbas turo shi a ka yi dan ya cutar da su
bangaran Faaz kuwa , tun lokacin da ya je Prison wajen Izayn bai sake wani motsi ba , dan gudun kar a kama shi , musaman da Izayn ya ce kar ya sake dawowa wajensa , specially ma yanzu da ya san Aleenah ta saka mishi ido , dole ya kiyaye takunsa wajen aiwatar da aikinsa na gaba
yanzu dai Familyn shiru ba abun da ke Faruwa , sai shirye shiryen tafiya Makkah da Malik da Diya su ke yi na watan azumi nan da two weeks




โ˜† MISALIN KARFE 9 NA DARE โ˜†



โ–ชPRINCE ๐Ÿ‘‘๐Ÿ”ฅ



zaune ya ke a parlour , da ga shi sai short , da laptop saman Thigh ษ—insa ya na aiki
ya na zaune a haka Aleesherh ta shigo parlourn ta na sanye da kayan barcinta , hannunta rike da wani tray cike da fruits da snacks

kai tsaye ta karaso wajensa ta zauna a kassa saman carpet , ta ajiye tray din gabanta ta fara ci

a hankali ya dawo da kallonsa gare ta , sai cin fruits ta ke cikin nitsuwa bayan yanzu su ka kammala diner kamar cikinta ba ya cika

janye laptop din sa ya yi ya ajiye gefe ya sauko kassa ya zauna gefenta ya kai hannu ya janye tray din ya na fadin " wai ke ba ki gajiya ? yanzu fa mu ka yi diner ? "

marairaice mishi face ta yi ta na fadin " please Honey , ka ban abuna , wlh yunwa na ke ji , ji na ke kamar ban ci komai ba tun safe wlh "

" dubi don Allah har kin fara yin k'iba , kullum sai ci ki ke yi , wai yaushe ki ka fara wannan uban cin ne ? ni dai a sanina ba komai ki ke sakawa a jikinki ba "

" ni dai yanzu ka ban Fruits di na na sha " ta fada cikin shagwaba ta na turo dan bakinta

bai ce mata komai ba ya mike tsaye ya dauki tray din ya nufi dining table ya ajiye shi
sannan ya dawo wajen ta , ya sa hannayansa biyu ya dauke ta cak kamar baby ya nufi corridor da ita

da sauri ta ce mishi " ni sauke ni ba in da zan je , ka sauke ni "

" shut up ! yaushe ki ka koyo rigima haka wai ? wlh har kin kara nauyi " ya fada ya na shiga bedroom din shi da ita

kai tsaye saman gadonsa ya kwantar da ita , sai turo dan bakinta ta ke yi kamar ya ce zai yi mata kiss

ya na sauke ta ko ta yi sauri ta juya mishi baya , ta janyo duvet ta rufe jikinta har kai

murmushi mai dan sauti ya yi ya na kallon ta , ya rasa ya a ka yi kwanan nan ta koyo rigima , amma ko ba komai ya na jin dadin yar rigimar nan da ta ke yi mishi specially idan dare ya yi sai ta yi zaune ta na zuba mishi shagwaba kamar baby

bai ce mata komai ba ya juya ya fice bedroom din , kai tsaye parlour ya koma ya dauki laptop ษ—insa sannan ya dauki tray din fruits din ta da ya ajiye saman dining table ya koma bedroom ษ—insa

ko da ya koma ya ajiye komai saman bedside drawer , ya hau saman gadon ya na fadin " tashi ki sha kayanki "

shiru ta yi ko motsi ba ta yi ba
a hankali ya kai hannu saman shoulder din ta ya juyo ta
nan ya ga Ashe har barci ya fara yin gaba da ita , da alamun ita kanta ta gaji

wani dan karamin murmushin gefen fuska ya yi kafin ya kwanta ya kashe lamps din dakin ya kunna bedside lamps , ya zagayo da hannayansa a bayanta ya rungume ta a jikinsa ya na sauke ajiyar zuciya , ya lumshe idanunsa duk da ba barcin ya ke ji ba




โ–ชJUNIOR ๐Ÿ‘‘



zaune su ke a garden shi da Diya , yau ya na son zama da Daddynsa sun yi wajen kwana biyu ba su ga juna ba , kullum Diya ya na fada , shi kuma ya fita wajen aikinsa

su na zaune su na hira har da dariya kamar wasu abokai
a haka Malik ya iso wajen ya na sallama

a tare su ka amsa mishi sallamarsa kafin Diya ya ce " lafiya na ga ba ka yi barci ba har yanzu "

karasowa gefensa Malik ya yi ya zauna ya na fadin " ganin ku na yi ku na dariya shi ne na taho na ji hirar me a ke yi haka "

har Diya ya bude baki zai yi magana Junior ya riga shi cewa " uncle dama ina son mu yi wata magana "
ya fada dan ya san in har Diya ya bude baki to tabbas sai ya bar wajen dan ko zaman da su ke yi tsokanar shi ya ke wai ya lura ya yi haske kwana biyu kamar sabon ango

cikin nitsuwa Malik ya ce mishi " wace magana kuma ? na ga ai Nailah ta koma part din ka ko ba haka ba ? "

wani dan karamin tsaki Junior ya ja ya na kauda kai kafin ya ce " uncle ni ba wannan maganar ba , a kan Faaz ne yaron da ke wajen momy RIANNA , na ji ta ce wai ta na son ta yi adopting shi , ko ta bar maganar ? "

" ta ce mu bari har ya samu sauki , ka san kwanan nan ba shi da lafiya har Asibiti ya kwanta , shi ne ta ce a bari har hankalinta ya konta sai a yi abun da ya dace "

" amma uncle kun san gidan marayun da ya gudo ? "

" ba ta fada min ba har yanzu "

dan jinkirtawa Junior ya yi kafin ya ce " gidan marayun Ekhaa , uncle a iya sani na gidan marayun Ekhaa ko bai zo na daya ba ya zo na biyu cikin kassar Saudiya , saboda su na da tsari sosai , su na kuma kula da marayu musaman manyan mutane da ministers ke ba da gudun mawa wajen kula da yaran , na takaice maka a cikin gidan marayun akwai karamar school ta koyar da yaran da su ka kai 8 years , ku na tunanin za su bar karamin yaro kamar Faaz ya gudo da ga gidan marayun ba tare da sun saka an fara cigiyar shi ba ? wajen four months ya na tare da mu amma shiru babu ta in da na ji a na cigiyar yaron da ya gudo da ga gidan marayu "


" me ka ke nufi ? ba da ga gidan marayun Ekhaa ya gudo ba ? " fadin Diya

cikin nitsuwa ya ce " Daddy sai da na je gidan marayun dan na tabbatar in da ga cen ya ke amma su ka ce min duk yaransu su na nan tun last year har zuwa yanzu ba wanda ya bar gidan marayun ko da sunan adopting , hakan ya sa kawai na ci gaba da binciken sauran gidan marayu kar a je mistake ne a ka samu ba da ga gidan marayun Ekhaa ya fito ba , Daddy baki dayan gidan marayun masarautar Saudiya sai da na bincika amma ban samu abun da na ke so ba , har pic din Faaz na dinga nuna musu amma su ka ce ba su taba ganin shi ba ma , akwai wani tsohon gidan marayun da ke cen fitar masarautar , ba kowa ne ya San da shi ba asali ma yaran da ke ciki ba su wuce 10 ba , bayan na gwada musu pic din Faaz su ka ce min Eh sun taba samun yaron da ke saman pic din , amma a lokacin sunan shi Abdallah , kuma ya yi wajen two years da rasuwa "


a tare Malik da Diya su ka ce " what ? rasuwa fa ka ce ? "

gyada musu kai ya yi ya na fadin " Yes , ya rasu , Daddy , Uncle , Princess ta jima ta na ce min hankalinta bai kwanta da yaron nan ba , kamar ya na da wata muguwar manufa , amma na kassa yarda da ita saboda a gani na yaro ne ba abun da zai iya yi , amma yanzu ina da tabbacin akwai wani abu a kassa "

ya na gama rufe bakinsa su ka jiyo Muryar Prince ya na fadin " ni kaina tun lokacin da na shigo masarautar nan na gan shi zuciyata ta kassa sakewa "

a tare duk su ka juya su na kallon wajen da su ka jiyo Muryarsa
dama ya jima a tsaye a nan ba su da labari , ya kassa barci ne shi ya sa ya fito , tun lokacin da Junior ya fara magana ya ke tsaye a wajen amma ba su lura da shi ba

a hankali ya tako ya zauna gefen Junior , ya na kallon Malik da Diya
cikin nitsuwa ya ce musu " ni kaina yaron nan bai kwanta min ba , amma momy RIANNA ta na son shi sosai , idonta ya rufe a kan shi , duk abun da za mu fada mata ba ba za ta yarda ba "

" yanzu me ku ke tunani a kai ? " fadin Diya

" mu fara sanin abun da ya kawo shi masarautar , abun da ya ke shirin yi , in ma cutar da mu ya ke son yi " fadin Prince

" haka ne Daddy , a ka je da hannunshi cikin rasuwar Ammie ? "

shiru Malik da Diya su ka yi ba su ce mishi komai ba , musaman Malik shi kadai ya San abun da ya ke tunani

ya yi nisa duniyar tunaninsa ya ga kawai Prince ya mike tsaye ya bar wajen ya nufi part din shi

a haka shi ma Junior ya mike ya na fadin " sai da safe Daddy , sai da safe uncle "

a tare Malik da Diya su ka amsa mishi , sannan ya fara takawa ya nufi part din Diya ya shiga bangaran su

shi dai Malik duk jikinsa ya yi sanyi ya ma rasa abun da zai ce
in har da sa hannu Faaz cikin rasuwar MALIKAT INAS to da hannunshi zai kashe shi kafin ya kai ga wanda ya aiko shi

yanzu tambayar da ta tsaya mishi a kai ita ce , wa zai aiko Faaz dan cutar da su ? wanene makiyinsa cikin masarautar ? shi dai ya san a halin yanzu ba wanda zai ce ga shi makiyansa , sai dai na Diya , amma kowa ya na da shaidar Diya bai da wani dogon hadi da MALIKAT INAS , to wanene ? gaskiya dole ya san abun

shi ma dole ya fara bincike a kan Faaz dan in har maganar Junior ta tabbata, ya na niyar cutar da su ya fara rasa ahalinsa kenan

ya yi nisa duniyar tunaninsa ya jiyo Muryar Diya ya na fadin " ya kamata ka je ka kwanta , dare ya yi "

gyada mishi kai ya yi kafin ya mike tsaye a hankali ya na fadin " gobe za ka je fada ne ? "

" gobe Friday fa , ina ga gaskiya zan yi hutu week-end , na fara gajiya "

murmushi mai dan sauti Malik ya yi kafin ya sa kafa ya bar wajen ya nufi part din su
da kallo Diya ya raka su har sai da ya yi nisa sannan shi ma ya tashi tsaye , ya na fadin " hakan na nufin duk su na da tantama a kaina ? dole na janye hankulansu da ga kaina har momy ta fada min shirin mu na gaba "
da kallo Diya ya raka su har sai da ya yi nisa sannan shi ma ya tashi tsaye , ya na fadin " hakan na nufin duk su na da tantama a kaina ? dole na janye hankulansu da ga kaina har momy ta fada min shirin mu na gaba "
ya na gama fadar haka kawai na ga ya koma Faaz lokaci guda
a hankali ya juya ya nufi part din MALIKAT INAS ya koma


( ๐Ÿ˜จ๐Ÿ˜จ๐Ÿ˜ง Hakan na nufin tun farko da Faaz ne su ke hira ba su da labari ? yanzu ina Diya na gaskiya ya yi ? kar a je ya cutar da shi ๐Ÿ˜ฟ )

( to ni na ce mi ? yanzu bari mu jira mu ga me Faaz ya ke shirin aikatawa , duk yadda a ka yi ba al'heri ba ne , a yanzu ahalin Malik za su fuskanci wani sabon hatsari , ga Prince kuma ya ce yaga Nayab , a ka je da gaske shi ne amma ya zo musu a matsayin mugu ? )
Yau dai na gama free pages ษ—ina Book 1 , me son cigaba mu haษ—u a book 2
Me bukatar yin magana da ni , zai iya taษ“o ni ta wannan number +22798999753

*WANNAN LITTAFIN NA BIYA NE , WANDA YA SHIRYA BIYA ZAI IYA TABO WANNAN NUMBER +22795577612 , โ‚ฆ500 NE KUDIN SHIGA PAID GROUP ฦŠIN*
*HAR ZUWA RANAR FRIDAY ZAI KASANCE โ‚ฆ 300*



โคโš˜ ๐๐€๐˜๐„๐‹โš˜โค
________________
แด›สœแด‡ ส€แด‡แด›แดœส€ษด แดา“ แด‡xษชสŸแด‡แด… แด˜ส€ษชษดแด„แด‡


THE MIDDLE ๐Ÿ•Š๐Ÿ‘‘โค



๐Ÿ•Š๐Ÿ’ž ( ๐™ฐ ๐™ท๐™ด๐™ฐ๐š๐šƒ ๐šƒ๐™พ๐š„๐™ฒ๐™ท๐™ธ๐™ฝ๐™ถ ๐™ป๐™พ๐š…๐™ด ๐š‚๐šƒ๐™พ๐š๐šˆ , ๐š๐™พ๐™ผ๐™ฐ๐™ฝ๐šƒ๐™ธ๐™ฒ , ๐™ธ๐™ฝ๐™น๐š„๐š‚๐šƒ๐™ธ๐™ฒ๐™ด & ๐™ณ๐™ด๐š‚๐šƒ๐™ธ๐™ฝ๐šˆ) ๐Ÿ’ž๐Ÿ•Š






โค๐Ÿ‘‘ ๐‘ด๐‘จ๐‘ณ๐‘ณ๐‘จ๐‘ฒ๐‘ฐ๐‘ต.๐‘จ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น๐‘จ๐‘ฏ ๐‘จ๐‘ฉ๐‘ซ๐‘ถ๐‘ผ๐‘ณ๐‘จ๐’€๐‘ฐ๐Ÿ‘‘โค
( ๐‘จ.๐‘ฒ.๐‘จ ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น๐‘จ๐‘ฏ ) โค๐Ÿ•Š


_______________________________________________


[ PAGE ___ 01 ๐Ÿ•Š๐Ÿ‘‘โค ]


da kallo Diya ya raka su har sai da ya yi nisa sannan shi ma ya tashi tsaye , ya na fadin " hakan na nufin duk su na da tantama a kaina ? dole na janye hankulansu da ga kaina har momy ta fada min shirin mu na gaba "
ya na gama fadar haka kawai na ga ya koma Faaz lokaci guda

( ๐Ÿ˜จ๐Ÿ˜จ๐Ÿ˜ง Hakan na nufin tun farko da Faaz ne su ke hira ba su da labari ? yanzu ina Diya na gaskiya ya yi ? kar a je ya cutar da shi ๐Ÿ˜ฟ )



โ˜† WASHE
End Ads