An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
๐ IN DAI KIN SAN BA KI KARANTA EXILED PRINCE BA , BOOKS 1 , 2 , 3 & 4 , TO KAR MA YI KI YI KOKARIN KARANTAWA DAN BA ZA NI GANE KOMAI BA ๐
WANNAN KARAN NA ZO MUKU DA SABON SALON SOYAYYA KAMAR KULLUM ๐โโค
BA ZAN CIKA KU DA SURUTU BA , SAI MUN SHIGA CIKIN LABARIN ZA KU GANE , WANNAN KARAN ZAI TASHI KWAKWOLWAR KU KAMAR BOMB ๐ฅ๐ฅ๐ฅ
๐คญ๐คญ ๐คญ๐คญ
TAP THIS LINK TO JOIN MY CHANEL
https://whatsapp.com/channel/0029Vaudu1uGpLHRdHh76P0s
_______________________________________________
PAGE___1 ๐๐โค
FOUR YEARS BEFORE
DAULAR SAUDIYA ๐๐ฅ
har ya kai bakin kofar mama ta ce mishi " tsaya don Allah ina son na yi magana da kai , auta yanzu na dawo " ta kai karshen ta na sakin Inaya
ta mike ta bi bayan Malik su ka fita ita kuma Inaya ta koma ta konta
sai da su ka yi dan nisa da dakin sannan su ka tsaya mama ta ce mishi " na sani Triplets ne ta haifa , ban ga laifin ka ba dan ka boye mata dan kar ta cutu , amma ina jin wani abu wanda ba zan iya fada maka ba "
cikin rudu ya ce mata " ta ya a ka yi ku ka san uku ne bayan ni da doctor da nurse biyu ne kawai mu ka san triplets ta haifa , ko ita na yi mamakin yadda a ka yi ta san Triplets ne "
" Muryar shi ta jiyo , haka ni ma na jiyo Muryar shi ta haka ne na gane su uku ne ta haifa , but zan so ka koma wajen doctor ka tambaye ta ina babyn ka ya ke in ba ta gan shi ba za ta iya samun sukuni ba , haka za ta yi ta jin Muryar shi "
wani dogon nunfashi ya ja ya na saukewa a hankali kafin ya ce " ki yi hakuri mama , ba zan iya ba , na san in ta ji labarin shi ba za ta iya jurewa ba , shi ya sa na boye wannan maganar , ke ma ina rokon ki don Allah kar ki fada mata "
" amma ya ka ke so ta yi Muryar shi da ta ke ji ? "
" zan san yadda zan yi " ya na gama fadar haka bai jira amsar ta ba ya raba ta geffen ta ya wuce
a hankali ta juya ta bi shi da kallo na dan lokaci kafin ta juya ta sauke wata yar karamar ajiyar zuciya sannan ta koma dakin Inaya
ko da ta koma ce mata ta yi " auta jira ni yanzu na dawo "
ita dai Inaya da to kawai ta ke amsa mata
haka mama ta sa kafa ta fito bedroom din , kai tsaye office din doctor din da ta karbi haihuwar Inaya ta nufa kamar ko ta san hanya
da sallama a bakinta ta shigo , ta na gaishe da doctor
da fara'a doctor ta amsa mata cikin girmamawa dan ba wanda bai San mama ba cikin masarautar nan
" Doctor , babyn da Malik ya ce ku bizine shi na ke son adawowa yarinyata da kayanta "
nan take murmushin da ke saman face din doctor ya bace ta ce " ki yi hakuri ranki shi dade , amma mun riga mun bizine shi , akwai nurse din da su ka fita da shi ta hanyar sirri , na san yanzu haka su na kan hanyar dawowa "
" innallillahi wa'ina illaihi raji'un , a ina su ka bizine shi ? " mama ta fada dan karfi
" a makabartar da ke fitar masarautar , Malik ya ce kar wanda ya san da maganar nan shi ya sa mu ka kai shi cen "
wani dan karamin tsaki mama ta ja kafin ta fice da sauri ,
ba dakin Inaya ta koma ba , kai tsaye word room din ta fito kamar za ta tashi sama sai sauri sauri ta ke yi
kai tsaye part Diya ta nufa , dan ta san shi kadai ne yanzu zai iya yarda da maganarta , kuma ya taimaka mata
da sallama a bakinta ta shigo part din , nan ta tardo Nesrine zaune ta na rike da Junior ta na ba shi nono , Diya na konce saman dayar sofa ya zuba musu ido sai murmushi ya ke saki , kamar ya meda su cikin cikinsa ya ke ji
a tare duk su ka dago kai su ka amsawa mama sallamarta
da sauri Diya ya mike zaune ya na fadin " sannu da zuwa mama "
wani dan murmushi ta saki kafin ta ce " yawwa sannu , Nesi ina fatan ki na kula da shi yadda ya dace , ko sai na taimaka miki ? "
girgiza mata kai Nesi ta yi ta na fadin " no mama , duba ki gani ma "
" mama , ku zauna mana ku na tsaye " Diya ya fada ya na mikewa tsaye zai ba su waje
da sauri ta ce " a'a Diya , wajen ka na zo , ina son mu yi magana "
bai kawo komai a ransa ba ya ce " bismillah "
" no , taho muje dai " ta fada ta na juyawa ta fice
nan ma bai kawo komai a ransa ba ya bi bayanta su ka fito ya na xe ma Nesrine yanzu ya dawo
da to kawai ta amsa mishi ta ci gaba da shayar da babynta
a harabar part din su ka ci karo da Abdoul ya fito da ga cikin part din sa , ya na ganin mama ya saki wani dan karamin murmushi ya karaso wajen
ko ta kansa mama ba ta bi ba ta ce ma Diya " Diya ina bukatar taimakon ka , cemetery din da fitar masarautar nan za ka kai ni "
da sauri Abdoul ya ce " cemetery kuma mama ? me za ki yi a cen ? "
kafin mama ta ba shi amsa Diya ya rigata cewa " saboda a cen su ka bizine dayan babyn Auta , ni ma jiyo lokacin da Malik ke cewa nurse su boye maganar nan , shi ya sa na yi shiru ban ce mishi komai ba , amma ni ma na san baby triplets ne ta SAMU "
" please Diya , mu je ina ji a jikina kamar yaron nan bai mutu ba , in ma ya mutum ina son auta ta gan shi in ba haka ba Aswad ba za ta kyale Malik ba , babynta ne ajikin na biyun "
" shikenan mu je " Diya ya fada ya na yin gaba
da sauri mama ta bi bayan shi su ka bar wajen , Abdoul dai ya zama dan kallo dan sam bai gane maganar me su ke yi ba
ko da su mama su ka fito kai tsaye cikin motar Diya su ka shiga , su ka bar masarautar da mugun gudu a kan idon Malik dan ya na ganin duk abun da ke faruwa tun shigar mama part din Diya
zaune ta ke tsakiyar parlourn irin zaman nan na cin tuwo , ta na sanye da wasu bakaken kaya na takaba , idanunta sun yi jazir , ta yi kuka har hawaye sun kassa fitowa
ta na zaune a haka Manisha ta shigo parlourn ta na sallama ta na rike da tray cike da fruits , ta karaso gaban Hafsat ta ajiye ta na fadin " ki ci wani abu mana , ko dan babies din da ke cikinki " ta fada cike da so
cikin bacin rai Hafsat ta sa hannu ta buge tray din nan take fruits din su ka watse cikin parlourn
wani dan karamin tsaki Manisha ta ja ta koma saman sofa ta zauna , sannan ta ce " ki godewa Allah ma da Malik ya ce a sake ki , bai sa an cire miki kai ba , bisa abun da ku ka yi wa yar uwarsa "
da sauri Hafsat ta juyo ta wurga mata wani mugun kallo da jajayen idanun nan nata
" Ni kuma abun da su ka yi min fa ? ya kashe min mahaifina , yanzu ya dawo ya kashe min mijina "
" Hafsat, ba ki yi dacen miji ma mahaifi ba ne , na san kawai dan ki dauki fansar kashe mahaifinki da Malik ke ya yi ki ka auri Aymane , abun da su ka shuka ne kawai su ka girba , mahaifinki ba mutumin kirki ba ne , ina sane da hakan na yarda na aure shi , ko kashe Marigayi Malik Hicham da ya yi kokarin yi ina sane , saboda na san mugun kishinsa da mahaifinki ya ke , in ba ki manta ba kafin Malik ya tafi Makkah , na samu rauni a hannuna wajen yankar fruits , aikin mahaifinki ne , babu ko tausayi ya sa wuka ya yanke min hannu saboda na yi kokarin dakatar da shi , shi da so ya yi ya samo jijiyata na mutu amma Allah bai yi ba , da bai samu nassara ba ne na ja baki na na hi shiru , haka Aymane ki na sane da abun da ya ke aikatawa , amma ki ka rufe ido ki ka goya mishi baya , yanzu wa gari ya waya ? "
" no , karya ki ke min , kawai ki na son kare shi saboda yaron yar uwarki ne "
" ke Hafsat , rashin mutuncin naki har ni za ki yi wa ? ni za ki cewa karya na ke " Manisha ta fada ta na dan zaro idanu
da karfi Hafsat ta ce " na fada , na fada , duk karya ku ke min , mijina ba abun da ya aikata , ni ce shaida tare da shi na ke kwana na ke tashi , ban taba ganin shi ya sha jini ba , kawai ku na son yi mishi kasafi ne saboda azabar da na yi wa RIANNA , wlh ba zan taba bari ba Nawfel ya ji dadin rayuwarsa tun da ya hana ni jin dadin tawa rayuwar "
wata yar karamar dariya Manisha ta yi ta na tapi , sannan ta ce " me za ki yi ? , ko ki na tunanin za ki iya yin wani abu a kansa ne ? "
wani dan karamin murmushi ta saki , kafin ta daura hannunta saman cikinta , ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " ni ba zan yi komai ba , amma dan da zan haifa ya yi wani abu a kai , in har jinina ne kuma jinin Aymane , na tabbata ba zai taba barin wanda ya raba shi da mahaifinsa ya yi rayuwa cikin farinciki ba , sai ya daukar min fansar da ni na kassa dauka , sai na ruguza wannan masarautar ta Saudiya , in har ban yi haka ba to ban cika diyar Mohammed ba "
a razane Manisha ta ce " ke Hafsat ki na da hankali kuwa ? kin san ab...... "
ba ta karasa maganarta ba kawai ta ga Hafsat ta bace bat , babu ita babu mai kama da ita
tsananin tsoro Manisha ba ta yi wani motsi ba ta sulale sumamiya a wajen
( ๐ค๐ค๐ค๐ค to fa , a na dara ga dare ya yi , sihirin Aymane ne ya dawo jikin Hafsat , ko ta babyn da ke cikinta ne ta ke sihirin , ๐ค๐ค๐ค )
TO NI NA YI GABA , MAY BE KAFIN NA DAWO , TA DAWO ITA MA ๐๐
Tsaye mama da Diya su ke bakin kofar Cemetery din masarautar , babu kowa da ga su sai Allah tsakiyar rana , sai bin wajen da kallo su ke , yi , yadda ka san sahara haka ya ke
" mama , ai wannan samo shi kamar neman alura cikin ciyawa ne , ba za mu iya neman sa ba " fadin Diya cikin raunin murya
" kai ba za ka iya ba , amma macijinka za iya samo wajen da su ka bizine shi , in har Aswad na jikinsa to zai iya samo Nayab " ta fada ba tare da ta kalle shi ba
wata irin muguwar faduwa gabansa ya yi , har sai da ya ga wasu dan taurari , a dubu dari ya juyo ya na kallon mama ya na zaro idanu
a hankali ta juyo ta kalle shi , ta saki wani dan karamin murmushin geffen fuska ta ce " ko ka yi tunanin za ka iya boye min ? ina sane da duk abun da ke faruwa a zagaye da ni , ko da abun a boye ya ke ina iya gani , tun ba yau ba na san da wannan maganar , kawai na yi shiru ne , yanzu ka fitar da macijinka ba mu da isashen lokaci "
gyada mata kai ya yi a hankali kafin ya juya ya lumshe idanunshi , ya fara motsa lips din sa a hankali
farat daya kawai ya koma macijinsa , a hankali ya konta kassa , ya fara tafiya , ya na zagaye kabaririkan da je wajen ,
sai da ya iso tsakiyar cemetery din sannan ya tsaya , ya mike ya juya ya kalli mama , alamun ya samo wajen
gyada mishi kai mama ta yi kafin idanunta su sauya su koma farare kal , bat ta bace , sai ga ta tsaye geffen macijin nan , ta na fitowa idanunta su ka dawo dai'dai ta na kallon wajen ta ce " tono ramin mu gani "
ba musu ya sa wutsiyarsa , ya fara ginar wajen , a haka har su ka fara hango wani warin veil
wata yar karamar ajiyar zuciya mama ta sauke kafin ta Zube saman guyiwowinta a wajen , ta fara gina da hannayanta
janye wutsiyar sa ya yi , ya birkice ya koma mutum , sannan ya shi ma ya tsuguna ya fara gina da hannayansa
sai da su ka fito da babyn su ka kontar da shi a kassa
da sauri mama ta sa hannu ta warware tissu din
ba shiri ta mike tsaye ta na karanto kalmar shahada
a rude ta ke kallo Diya ta ce " Diya , ina Nayab ya yi ? " ta fada dan ba doll ce a nade cikin tissu din
" mama ni ma jan sani ba , amma duk yadda a ka yi an nade Nayab cikin tissu din nan , sai in dai da ga baya su ka fitar da shi "