" kan bazawara mai tallen fura da nono mune karuwan,
kazamin banza kai inba kaddara bama ka isa mu sayi abunka banza kawai mai yawo da germs ajiki,
dube kafa yohh tohh ko karuwancin zanyi ai mai lasisi zanyi,
wallahi nafin kar wulakan cecce irinka marar abunyi,
kwarton banza mai kallon 'ya'yan mutane asararre kwasheshshe kawai"
"ko made mai zaku ce wallahi kurwata tafi karfin ku sai de kuyi gaba,
sai kuzo kuyi ta hana bayin Allah bacci kuna mawa mutane kwalele ku barinsu zakuyi su taba ba"
Islam tace " da tun fari abinda ka fada kenan sai kace muna maka kwalele ai daya fi mutunci,
asararre kazamin kan layi wa zai baka ka taba sai de kajea can kasan gadan kasamu kaza mai irinka kuyi ta faman tabe taben naku"
cikinshin ta murda buta ya dauka yace " kuma wallahi saura ko daya ku dauka ku gani"
yana magana ya shiga banadakin dake gun na sabil,
wani irin kutukin bakin ciki ne ke addabar mu dan sam bamu huce ba,
wani dabara ne ya fado wa Islam ta dan murmusa
tace "kina tuna nin abinda nakeyi kuwa,"
nuna mata dibinon nayi da ido na kuma nuna mata yaran dake wajen wanda basu gama tafiya ba sai kuma wanda suke wucewa,
murmushi na sake wanda tun safe banyi ba na daga siririn murya na,
na fara sadaka , sadaka, sadaka ,
Queen Mahirah
GUDU SAURI SAURI,ππΆ
KU MASTO KUJI NI DA KUNNEN π BASIRA,
πNA KUSA DENA POSTING FREE PAGES GROUPS ,
GAME BUKATAN SON CIGABA DA GANIN POSTING YAYI GAGGAWAN SHIGA GROUP LINK NA SAMA ANAN ZAKA SAMU POST AKAI, AKAI
KO YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER A WHATSAPP 09168962485.
π§THE TWO LIGHTβ¨ {RIKICIN GIDAN SARAUTAπ°}π§
Story and written by
Queen Mahirah
ADAPTED EXPERT WRITER πποΈ
BOOK 1
?Friday, ?February ?23, ?2024
10:22:13 AM
GUDU SAURI SAURI,ππΆ
KU MASTO KUJI NI DA KUNNEN π BASIRA,
πNA KUSA DENA POSTING FREE PAGES A GROUPS ,
GAME BUKATAN SON CIGABA DA GANIN POSTING YAYI GAGGAWAN SHIGA GROUP LINK NA SAMA ANAN ZAKA SAMU POST AKAI,AKAI
KO YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER A WHATSAPP 09168962485.
π§23π§
Cikin siririyar muryata na fara cewa
sadaka, sadaka,
aiko dama kamar jira suke a kirasu suka yo kanmu da gudu,
batare da wani shakka ko storo ba muka sadakar da wannan dibino da kwakwaan a yara,
bamu bar ko daya ba kai hatta amalanken nashi ma mun sadakar,
muna gamawa sai ga Auwal da mota ya zo ba bata lokaci muka shiga ya kama hanyan gida damu,
a mota ba abunda mukeyi sai kwasar dariya da kwatanta yadda wannan mutumin zaiyi idan ya tarar da tabar gazan da mukayi masa,
har muka iso gida tun daga bakin gate muka hango dandazon sojoji har aka bude mana gate muka shiga wani dummmm heart dina ya bayar,
gaba daya na nemi wannan farincikin na rasa lokaci guda wani kunci ke dawaainiya da zuciyata da bansan name ba,
Islam tace " tohhh ikon Allah mai yake faruwa a gidan yau, "
Auwal driver ne ya amsa mata da cewa baki akayi,"
ba wanda ya tan ka masa muka fito daga motan muka nufi cikin gida,
wani irin karkarwa jikina keyi da bansan na mai nene ba ga wani bugu da heart nawa keyi,
haka muka yi ta tafiya har muka iso bakin farlon mu nice nayi saurin shiga,
aiko ba shiriii na ci karo da wani abu kamar dutse,
hakan yasa nayi baya tamkar zan fadi amma cikin ikon Allah naji ban fadi ba,
jinayi ina reto don tuni veil da turban di na ko wanne yayi hanyan sa,
yalwaceccen gashi nane ya bazu shigo ya tallafoni da kyau sai ya zaman to kamar a film din indiya yadda jarumi ke tare jaruma inzata fadi,
ahankali na bude idona inda mukayi 4 eyes dashi wani mugun stinkewa heart nawa yayi ware idona nayi,
na cigaba da kallon idonsa wanda shima anasa bangaren haka ne,
duk da irin bugu da heart dinsa keyi da abubuwa masu wuyan fassarawa da yake ganowa a idona baisa ya dena kallona ba mun kame kamar statue,
Islam da abin yazo mata abazata ta sake baki tana kallon ikon Allah,
ganin kallon bazai mata wani amfani bane yasata ciro wayanta ta fara haskasu da camera tana musu video'
wani irin kara na saka lokaci daya,
wanda yayi nasaran birkita mishi brain abinka da mutumin da baison hayaniya,
aiko nan ya sakeni na fadi yasa hanu ya toshe kunnan sa,
cikin azaba na fashe da kuka dan ba karamin buguwa nayi ba,
su Innani suka fito jin wannan ihun tana tambayn ba'asi don ko ba'a fada mata ba tasan shalelenta ne ke wannan kukan,
"waye ya taba uwassa yau agidan nan waye ya taba munke shalelena yau naci ubanshi daidai gwargwado"
cakkk ta staya ganin Fahreen staye ya rufe kunnan sa da hanu biyu niko ina zaune akasa nayi zaman cin tuwo ina ta rera kuka ,
Islam ko tana ta faman video da wayanta kirar i phone 15pro,
baki ta sake tana kallon ikon Allah,
Fudhal ya karasa inda Fahreen yake ya ce" lfy Tweeny mai ya sameka,?"
shiko Fareed inda nake ya karasa ya tsuguna yace
" subahanallahi mai ya faru dake?
mai yasa meki?
ince dai bai miki komai ba ?"
stegege nayi na staya kallonsa da mamaki wanda ya bayyana karara a fuskana,
sai binshi nakeyi da kallo ina ta misitsika ido nayi wuri wuri dasu kamar wacce aka kama tana satan kaya,
kara kusanto ni yayi yana tambayan lafiya,
aiko ba shiri nakara sa wani kukan na fasa ihuu ina kiran sunan Innani,
ta karaso da sauri, ta dafa kafadana tana cewa " gani shalelena mai ya sameki,"
rungumeta nayi da sauri bakina yana rawa nace Innani sanyi,
sanyi nakeji Innani zan mutu wayyo Allah Jaddi wayyoh Hamma Faruq,
wayyohh Ilham dina da Sauban dina momy, ummi, Abie, wayyohh Allah na Myreen,
zan mutu Innani kaina zai fasahe wayyohh Innani ban karasa maganan danakeyi ba idona ya fara juyawa na kafe na sandare na dena mosti gaba daya ,
cikin tashin hankali Innani ta fashe da kuka,
ta ce dan kwal ubanki kibar wannan danne danne da wayan kije ki kira mun Sheik yana dakinsa yanzu ya tafi,"
cikin tasahin hankali Islam ta tafi kiran Jaddi,
Fudhal ko dakyar ya kama Fahreen ya mai dashi cikin falon don so yayi ya rikice gaba daya sai fisge fisge yakeyi,
nikuwaa Fareed ne ya sunkuce ni ya shiga falo dani,
ko sakan biyu bamu kai ba saiga Islam da Jaddi sun shigo falon hannunsa dauke da wani gora wanda yake dauke da ruwan zam zam da addu'a aciki,
yana shigowa ya rasa gun wa zai fara zuwa,
mika roban yayi a Islam yace taje ta shafa masa sannan ta kama mishi kai ba musu ta karba don tasan mai yake nufi,
babu abinda basu iya ba dan yana koya musu abubuwa sosai,
karba tayi ta wuce inda Fahreen yake Fudhal ya rungumeshi sosai ajikinsa,
tana zuwa ta zauna agefensa ta bude goran tashfa masa a fuska yunkurowa yayi kamar mai yin dambe,
amma Fudhal ya rike sa batare da storo ba ta kama kansa ta shiga tofa masa addu'a wani irin gumi ne ke stattafowa daga jikinsa yunkurin kokuwa yake tayi da ita wani wawan stawa ta daka masa
" zaki staya ne ko saina ci ubanki muna fuka "
da ido π Fudhal yake ta binta ganin yadda halittanta ya canja lokaci daya,
in baiyi karya ba har wani huci yaga tanayi hayaki na fitowa daga bakinta da hancinta wani abu ya hadiya,
abun mamaki gani yayi Fahreen ya dena shure shuren ya nustu,
kuma bugu da kari yaji ta ambaci mace kuma de yasan su duka maza ne sai ita ce mace to mai haka yake nufi ?
wikil wikil π ya fara yi da idonsa,
cikin kan kanin lokaci ya sake wani dogon ajiyan zuciya,
yayi shiruu dago da rinanun idonta tayi tace
" gyara masa kwanciyar sa," ba musu yayi abinda tace,
abangaren Jaddi kuwa ya karaso inda nake Innani sai kuka takeyi niko na kafe na bushe kamar gawa,
karasawa yayi ya zauna agefena shide Fareed yana ganin ikon Rabbi,
ahanakali ya fara tofa mun addu'a wani irin mika nayi can nafara fisge fisge sai kuma na nustu,
mikar dani yayi ya zaunar, kafaun yace bayan skekara 20 yau Allah ya kaddara haduwan mu,
dago kan ka ka kalleni sannan ka kayi gaggawar war ware abinda ka kulla ka cire ajiyan da kayi ajikinta tun kafun mu kwashi yan kallo da kai,"
kauda kaina nayi gefe ina dan harare harare,
murmushi Chief yayi yace Islam kawo min goran ba musu ta kawo masa,
karaf idona{ ko ince idonsa tunda ayanzu bani bace zan iya cewa aljanin jikina ke magana},
ya fadi akan goran,
aikuwa ya mike mai kyau ya gyara zaman sa ya kalli Chief yace " kafadi mai kake so zanyi,
amma banda wannan ruwan,"
yayi magana cikin wani murya mai razanar wa ,
wanda yasa kowa nacikin falon mai da hankalinsa kaina don abun mamaki ne ace karamar yarinya tana irin wannan maganan cikin muryan gardawa,
murmushi Chiefa ya kara sakewa yace " bazan kuma mai maita kaina ba nasan kaji mai nace tun farko"
"kade fadi wani abun daban amma banda wannan don gaskiya bazan iya ba an riga anbiyaa ni kudi akan aikin nan,
ni bazan iya saba alkawari ba,"
" bude murfin goran Chief yayi ya wasta masa ruwan wani irin razananen kara ya sake,
ya kara wasta masa, ganin zai illata sa ne yasa shi fara ja baya yana jijjiga kai yace
"naji kayi hakuri zanyi koma mai kake so"
murmushi Chief yayi ya shafa farar gemunsa yace
" kamar yadda na fada ma afari zan kara mai mai ta kaina, kacire mata ajiyan da kayi ajikinta,"
cikin azaba yace" zan cire amma ba duka ne nawa ba abinda nasa mata stanan shi ne kawai"
Chief yace bangane mai kake nufi ba"
cikin azaba yace
" labarin dogon labari ne kuma a sarkake yake abun ya samo asali ne tun kafin su fito duniya akayi abubuwa akansu wanda ba mutum daya bane,
war ware abun zai yi wiya ayanzu har sai ta koma cikin masarautar su kafun komai zai ware,
amma kaga wannan yaron yayi magana yana nuna Fahreen dake kwance,
itace maganin jinyarsa ita din garkuwa ce agaresa saukin sa yana cikin taraiyar su,
kasancewarsu a guri daya zai samar mashi da kwancaiyar hankali,"
shiruu chief yayi yana nazarin magan ganun sa jijjiga kai kawai yayi yace
" naji amma inaso kasan ba wai na dauki wannan zancen naka bane sabida sauki yana wajen Allah,
sannan duk abinda ya faru da wani to tabbas da sanin Allah ba wani wanda ya isa ya cutar da wani ba tare da Allah ya yadda ba,
da kuka raba su kuka kuma koresu daga cikin ahalinsu da tunanin kun salwantar da rayuwarsu,
shin hakan yayiwu ne gashi sun cigaba da rayuwa,
wannan ba ikon Allah bane ko haka ya isa ya sa ku risina ku tabbatar da cewa in Allah ya kaddara faruwar abu ba wanda ya isa ya dakatar,
kun nesantasu da juna na stawon shekara 20 gashi cikin kankanin lokaci basirar ku ta shafe kunyi abinda kuka hada su batare da kunsan kunyi hakan ba,
inaso kusani ba yadda kuka iya da wayannan yaran sai de ku gansu ku barsu su din hadin Allah ne kuma halittar sa ne,
kamar yadda kuke gudu to hakan ne zai faru hasken da kuke storon zai haaska duhun da kuka mamaye masarautar dashi yana nan kuma yana tahowa da sannu kamai zai ware,
inaso kaduba yaran nan gaba daya katabbatar ka cire ajiyan da aka aiko ka kayi musu"
cikin muryarsa marar dadi yace " kayadda dani banyi ajiya ajikin ko wa acikin su ba,
bani na musu ajiya ba suma nasu masatalan daban ne wata daban ne tasa aka musu ba ni ba ba wacce tasa ni wannan aikin bane nasu daban ne,
kuma ta fimu karfi sosai ita mastafiya ce ita da kanta take aiki da wani kungiya a kasar Eagypht ni kuma daga kasar India nake ni dan can ne,"
jijjiga kai Chief yayi yana mamakin wannan lamarin yace
" shikenan kayi aikin ka kawai ka barni dasu sauran,"
wani irin mika nayi na koma na kwanta wufff bacci mai nauyi yayi awun gaba dani,
dogon numfasahi Chief ya sauke yace Fareed taimaka kadan mika mun ita daki tasamu tayi bacci,
gyada kansa yayi ya mike cos he is totally speechless,
daukana yayi kamaar wata baby Innani da tayi jugum ta masa jagora ya kaini daki ya kwantar dani,
karewa fuska na kallo yayi na yan sakanni yana kokarin fahinmtar wani abu game da fuskan,
gani yake tamkar yasan wani mai irin wannan fuskan to amma a ina dogon numfashi yaja ya fito daga dakin,
"sannu dan albarka na gode ko zaku iya tallafawa dan uwan naku ku kaishi ya kwanta shima don ya huta kafun anjima zan zo sai muyi magana ,"
gyada masa kai kawai sukayi suka dan bibbigi Fahreen ya tashi suka tallafa mishi suka kaishi dakinsa suka kwantar dashi kafun kowa ya zauna ya fara karanta wasikar jaki,
kamar haka ,wacece wanan yarinyan ?
sannan wani masarauta yake magana akai ?
mai ne ne alakanta da Fahreen ?
kuma wani ajiya yake magana akai ?
wa kuma yayi ajiyan kuma ta yaya ?
DOMIN SAMUN WANNAN AMSA SAI KU CIGABA DA BIYONI DON WASAN YANZU AKA FARA YANZU LABARIN ZAI SOMA
Story and written by
Queen Mahirah
ADAPTED EXPERT WRITER πποΈ
BOOK 1
?Monday, ?February ?26, ?2024
02:30:18 PM
GUDU SAURI SAURI,????
KU MASTO KUJI NI DA KUNNEN ?? BASIRA,
??NA KUSA DENA POSTING FREE PAGES GROUPS ,
GAME BUKATAN SON CIGABA DA GANIN POSTING YAYI GAGGAWAN SHIGA GROUP LINK NA SAMA ANAN ZAKA SAMU POST AKAI AKAI,
KO YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 09168962485.
2οΈβ£4οΈβ£
NIGERIA { RUGAR HARDO BELLO}
Suna zaune jigum jigum ba wanda yake cewa kala,
hasalima kowa da abinda yake tunani da sakawa a ranshi har aka kira sallan azahar ba wanda ya mosta acikinsu,
zuwan Chief ne ya mikar dasu alwala sukayi bayan tada Fahreen da sukayi shima yayi alwalan ya musu jagora har zuwa tankamemen masallacin dake kofar gidan,
hadadde mai tashin kamshi da sanyi A/c zaka ranste a villa mosque kake stabar yadda gurin ya staru da kayan alatu da more rayuwa,
daga Fudhal har Fareed duka sake baki sukayi suna mamakin wassu abubuwa game da wannan Rugar daya ke kamar aljannan duniya,
bayan sun idar da sallah ne suka kama hanyan komawa gida inda suka samu an ajiye musu abincin rana,
suna shiga suka samu guri suka zauna,
kamar kullum MG Fahreen ya samu guri ya zauna ya kishingida a jikin laulausan kujeran falon ba abinda yakeyi sai salatin annabi da ya zame masa ruwan sha da kuma ci,
don tunda ya fara wannan jinyan ya dena komai sai bautawa ubangijinsa dama ba gwanin surutu bane sai ya lumshe idonshi yayi ta istigfari da hailala ko salatin annabi,
tohh yauma hka yayi ya lumshe idonsa,
Chief yace "bissimillah kuci abinci sai muyi maganan daya kamata"
," Fudhal da kamar dama jira yakeyi yace " no need for mu fara cin abinci kawai let go straight to the point,
cos baza ma mu iya cin abincin ba muna da tambayoyi da dama da zasu hana mu jin dadin abincin infact bamu da ma appertite,"
murmushi Chief yayi yace " shikenan, yanxu mai kuke so ku sani "
Fudhal ya dan muskuta ya gyara zaman sa yace
" yauwa firstly muna son sanin mai yake damun Fahreen??
sannan bamu gane mai kake magana akaai ba game da ajiya dake jikinmu,??
sannan wannan yarinyan wacece ita,??
kuma mai yasa garinnan ya zama haka,??
a iya sanina ruga ai karamin guri ne wanda fulani ke rayuwa kuma babu gini sai bukka da tarin shanukai,
but anan da ban ban ci ko mai yasa hakan,"
gyada kai Chief yayi murmushi yace
" malam Yarima iirin tambayoyi haka da wanne zan fara"
Fareed yace " Jaddi ba sai ka takura kan ka ba kawai ka fada mana abinda ya kamata mu sani,
kabar wannan marar hakurin dama hka yake yana da gajen hakuri,"
yana magana ne yayin da yake aunawa Fudahal harara don yaji haushin tambayoyin nashi,
murmushi Chief ya saake yace
" da farko de inaso ku gode wa Allah don yayi muku baiwa mai tarin yawa wanda baku san dashi ba,
sannan game da rashin lafiyan dan uwanku wannan daga Allah ne,
amma a komai akwai sanadin faruwarsa,
tohh zan iya cewa sanadin faruwar rashin lafiyansa ba komai bane sai sharrin makiya da kuma magauta hadi da miyagu,