x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 17 - THE TWO LIGHT RIKICIN GIDAN SARAUTA

  • 48001 words
  • 51000 words
  • Out of 97531 words

Category: Love Stories

Views 539

20 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
kyakyawa ga wani tashin kamshi da nakeyi .

Farlo na fito anan na samu Islam na jirana itam cikin nata shigar mai daukan hankali mikewa tayi tace

" muje kar muyi latti"

kai kawai na gyada mata don sam yau ban tashi da son yin magana ba,

tare muka fito harabar gidan muka wuce side din Jaddi don musu sallama shi da Innani.

da sallama muka shiga farlon muka yi sa'a mun samesu a farlo,

Innani tace a'a shalelena har kun fito" ban iya cewa komai ba sai Islam ne ta gyada mata kai,

Jaddi yace " Allah kare ya kuma dawo daku lafiya"

da Amin Islam ta amsa niko a kasan makoshina na amsa,

bayan dogon addu'a da Innani ta surfo mana kamr yadda ta saba muka kama hanya.

mun fito muka samu Auwal har ya fito da mota,

ta bangare daban kuwa sai gyara guest room akeyi duk da dama agyare yake,

haka kawai na stinci kaina da stinkewan zuciya da bansan name ba.

school ya kaimu kamar yadda ya saba muka shiga tun daga gate din school din muke kwasan gaisuwa ta dalibai da wassu malamai da ma'aikata har muka isa staff room,

bance kala ko gaisuwan ma sama sama nake amsawa,

koda muka je staff din ma ban kula kowa ba,

haka ko da na shiga class yau ba walwala su kansu daliban sun sha jinin jikinsu da ganin yanayi na duk sai suka subure.

Innani ne ta zubawa Chief ido na yan sakanni kafun tace "Sheik,"

yace na'am "Nana,"

wani dogon numfashin ta kara saukewa kafun tace " niko ka kula da yanayin Noor yau gaba daya ta subure,

ni wallahi gaba daya a storace nake da wannan lamarin kana ganin baza a samu mastala ba,

anya baza mu kware ta da yawa ba, ni inaga kamar mu mai da can Iraq din ta cigaba da zama zaifi,"

murmushi Jaddi ya sake yace " ba yadda muka iya da abinda Allah ya kaddara,

ko bangon duniya zamu kai Noorul Huda bazai hana ta shiga wannan yanayin ba sabida kaddaran tace,

ba'a ja da ikon Allah namu addu'a da fatan alakairi,

sannan kasancewar da zasuyi a tare shine kadai hanyar war ware wannan mastalan,

in ba haka ba daga shi har ita ba wanda rayauwar zata mawa dadi."

dogon numfashi Innani taja tace to "Allah zaba mana abinda yafi alkairi,"

Amin shine abinda Jaddi yace.

Wasu hadaddin mota ne na bugawa jarida sukayi parking akofar gidan Chief Imam,

motoci ne na alfarma wanda sai wane da wane ke hawanta mota biyar,

hudu daga cikinsu bakake ne daya ne kadai fari wanda yake a stakiya,

ajikin ko wani plate na motan an rubuta COMMANDORE AJ sannan ko wanne da tambarin masarauta ajiki,

ban gama ankarewa ba saida naga dan dazon soldiers sun fito sun yi kawanya a motan stakiyan,

suna cikin haka aka bude musu gate din gidan tare da basu izinin su shiga nan kuwa wannnan farar motan ta danna kanta cikin gidan bata staya a ko ina ba sai a parking space,

nan yayi parking sojojin ne suka dawo cikin gidan suka kara yiwa wannan motan rumfa suka bude cab din motan na both hannun hagu da dama cike da takama da mazan taka suka fito su biyu daga motan,

suna sanye cikin half jamfa daya fari daya kuma sky blue,

ya matukar amsar su ya fidda zallan mazantakarsu da kwarjininsu hadi da haiba,

Captain Fudhal ne ya taimakawa Major General Fahreen ya fito daga motan,

Masha'allah yana sanye cikin dakakkiyar yadi black colour wanda ya fidda zallan kyansa da kamalansa,

fuskarsa tayi fayau da ita sai lumlumshe ido yakeyi kamar mai jin bacci,

Fudhal ne ya kama hannunsa suka fara tafiya kafun Commandore Fareed ya jera musu,

suna tafiya cike da izza da mazantaka hakika Allah yayi halitta anan domin inka gansu sai ka kara ganinsu haka baza kaso ka dauke idonka daga kansu ba ko ba'a fada ba mahaifiyarsu ba karamin kokari tayi ba,

haka ka zalika ba karamin baiwa Allah ya mata ba na haifan wayannan zaratan samarin masu murdadden halinta,

haittansu kadai abin birkitar wa ga makiyinsu,

dakatawa sukayi da tafiyan don hango Chief da suka yi dama Auwal ke musu jagora zuwa maasaukinsu,

kallo daya ya musu ya jijjiga kai ya hango tarin mastaloli da suke dauke dashi wanda a zaahiri ba kowa ke iya gani ba sai wanda Allah ya kaddara,

wato wanda Allah ya masa baiwaa, ko su kansu basu san dashi ba .

fuska dauke da fara'a ya karasa inda suke,

yace"sannun ku daa zuwa bissmillah,"

jagora ya musu har part din da aka tana da musu ya kuma bude suka shigo wani dogon numfasahi suka ja gaba dayansu,

wani ni'imanceccen kamhi suka shaka mai kwantar da hankali dasa nustuwa ga waani sanyi mai rasta jiki,

"bismillah"

shine abinda chief ya fada ganin su staya daga bakin falon basu iso ba,

shigowa sukayi suka samu guri a kasa suka zauna ganin ya zauna akan kujera,

ba komai ne ya su yin haka ba sai dan ganinn kwarjininsa da kamalan sa ga wani hasken imani da yakeyi,


murmushi yayi yace "ya kuka zauna daga kasa,

ku tashi ku hau sama kasan da sanyi inkuma ni na sauka tohh,"

sunso yimasa gardama amma kimarsa da girman zatinsa da suke hangowa ya hanasu yin hakan hadi da last statement nasa yasa su hawa kan lumstatan kujerun na alfarma,

suka zauna sannan suka mika masa gaisuwa cike da kamala ya amsa musu cikin yaren fullanci yana murmushi yace

"ko baku iya ba"

murmushi dukkansu suka sake kafun ya kuma cewa

"nan ne masaukin ku ga dakuna wanda kwa zai iya amfani dashi,

zaku iya shiga ku duba in bai yi muku ba sai acanja muku,

Fareed sarkin saukin kai da fara'a ne yace

" nan ma yayi ba sai ancanja ba mun gode da kulawarka gare mu"

murmshi Chief yayi yace "gyada kai yace Masha'Allah yanzu sai ku shiga ku huta ko kafun anjima sai muyi magana"

ya kammala maganan yayin da yake mikewa staye da niyan basu guri don su sha iska.


kowa dakin da ya masa ya shiga cike da kwanciyar hankali suka wasta ruwa sannan suka shirya cikin kaya mara nauyi,

kamar sun hada baki duka suka jallabiya farare tas,

suka fito falo suna fitowa suka samu an jera musu abinci reras akan centre table dake falon ba musu suka karasa inda abincin yake don dama ko breakfast basuyi ba,

suna zuwa Fareed ya fara bude flasks din wani kamshi ne ya daki hancinshi har san d ya lumshe idonsa,

bakomai ne acikin flask din ba sai hadaddiyar kaza data sha dafin stofi,

dan Innani da kanta ta dafa musu dayan ya bude doya ne da kwai sai tashin kayan kamshin yake da tafarnuwa,

daya kuma wani dan bowl ne fruit salat ne aciki da kuma hadaddiyar tea a tea flask ga kuma dibino shima acikin nasa ma'ajiyar,

gyada kai Fareed yayi yana jin jina musu jikinshi har rawa yakeyi wajen daukan plate yayi serving kanshi,

Fudhal da shi kanshi tun dazu hadiyar yawu yakeyi ya buga stuka abinka da mai hancini

"mistchhhww dube shi sai wani rawar jiki yakeyi kamar bai taba cin abinci ba"

ko kula shi baiyi ba ya zuba abincinsa yadda zai isheshe shi ya kuma dauka plate ya zuba wa Fahreen ma ya mika masa bai masa musu ba ya karba,

Fudhal ne ya sauka gaban abincin don zuba nashi,

" awwww wai dama zaka ci "

ko kula shi baiyi ba sai kara hade fuska da yakara yi,


murmushin da take halittan sa ne ya sake yace

aikin kawai mutum sai dan banzan burga,

ai na zaci kai da kataba cin abincin baza kaci wannan dinba dan renin sense,,"

ko kula shi baiyi ba ya fara bawa cikinsa hakkinsa.

"kai Allah de yayi albarka a matar gidan nan ni dole ma na shiga na mata godiya kamar tasan dama yunwa nakeji wallahi,

kuka ne kaawai banyi ba da zamu zo kuka wani daga wa mutane hankali wai muyi sauri kamar zamu bar duniyan,"

yana maganan yana turo baki yana bata fuska,

idan ka kare masa kallo zaka hango zallan shagwaba dake tattare dashi,

"Fudhal yace tun da gidan na kanin ubanka ne sai ka shiga kamata godiyaa,

dan shishsigin stiya sai shegen son cusa kai a inda ba'a gayyace ka ba da son asan da kai"

" murmushi ya sake yace to Alhamdulillah dalilin shishigin da cusa kan nawa aka sanni a gurare da dama wanda wani katon gardi baije ba,

kuma ba'a san dashi ba yayi karasa maganan nashi yana auna mishi harara"

" nuna kanshi yayi yace nine katon"


" dubawa zakayi dan renin wayo kawai "

sallaman da Chief yayi ne ya kastar dashi daga abinda yake niyan fada,

amsawa suka yi ya shigo ya zauna fuskansa dauke da murmushi,

yace "saannunku da bakunta da fatan ban takura muku ba,"

caraff Fareed yayi ya cafke zancen da cewa,

"ko kadan wallahi Jaddi dama muma yanzu muke cewa zamu shiga muyi wa matar gidan godiya"

Fudhal dake gefe sai aikin auna mishi harara yakeyi shiko yayi kirmisisi kamar ma baisan yanayi ba,

murmushi Chief yayi cike da jin dadi don bai stamman ci haka daga garesu ba yace

" ayyahh ai ai sai kunje ba itama zata zo ku da kuke da marar lafiya,"

"aaa ba'a yi haka ba ai mu ya kamata muje mu duba ta mu mata godiya don ba karamin taimakon mu tayi ba"

murmushi Chief ya kara sakewa yace tohh muje"

ya mike don musu jagora ya fito waje,

Fudhal sai aunawa ishi harara yayi don ba karamin kular dashi yayi ba,

murmushi ya sakea yace

" kadan ma kagani dani kake wasa wataran ma sai na ka kayi wanke wanke agidan,

nan anan zaka gane ni cikakken dan shishigi ne,"

wani wawan cafka ya kai masa ya kwace ya fice kamar zai kone dan bakin ciki,

Fahreen ne ya mike wanda tamkar baya gurin tun dazu sai de yana jinsu stabar miskilanci ne ya hanashi magana,

hannunshi Fudhal ya kama suka fito tare suka hango Fareed da Chief har sunyi nisa sai hira sukeyi kamar wanda sukayi shekara 30,

da haduwa haka suka bi bayansu har suka iso cikin balcony na gidan directly part din su Mahnoor yayi dasu don da shi ake amfani"

a falo sukayi sallama suka samu Innani sai bala'i take ta zazzagawa Barira kamar zata cinye ta danya tana ganinsu ta fara washe baki ,

" maraba lale sannunku da zuwa"

shigowa sukayi suka syugana har kasa suka gaisheta ta,

amsa da sunyi niyan zama a kasa ta hanasu suka zauna a sama kan kujera,

" Masha'Allah yau larabawa muka samu a gidan namu ai badan kunyi hausa naji ba da bazan yadda ku ba larabawa bane,

da har ina kokarin kankaro nawa guntun larabcin ashe ma kuna jin hausa"

murmushi duka sukayi amma banda Fahreen da ya saadda kanshi kasa wani mugun bugu zuciyarsa keyi da bai san dalilin taba,

Fareed yace " ayyahh kice da mun wahalar dake ai mu muna jin hausa dan acikinta ma muka taashi,

dama ma mun shigo ne mu muki godiya Mama mu ga abinci mun gode Allah saka da alkairi ba karamin taimakon mu kikayi ba "

murmushi Innani tayi cike da jin dadi tace "laaa ba komai ai bakonka annabinka,

kuma Innani zaka ringa cemun haka jikanun nawa suke ce mun shikuma Jaddi suke kiransa dashi"

" shike nan Innani kinga mun samu sabin kakanni dama mun bar namu a gida sai ku maye mana gurbinsu'"

washe baki Innani tayi tace " aiko ina maraba daku dama kaga kuwa jikanun nawa murdaddu ne kamar sauran yan uwan naka dama dama ma acikinsu Mahnoor ce"

mugun razane ya dago da snake eyes dinsa ya zuba mata su jin abinda ta fada,

ta tabo inda ke masa ciwo ta fame masa ciwon da ya dade yana fama dashi na stawon shekara 20,

jin ta ambaci wannan suna duk da yasan mamallakiyar sunan bata duniyan ayanzu sai de har gobe tana ransa baya kuma fatan cireta daga ransa har abada,

Fareed yace " ayyah wai itama jikar kice"

" ehh ai su shida ne amma biyu ne kawai suke kasar nan,

sauran suna can kasar Iraq su da iyayen su amma in anyi hutun karshen shekara suna zuwa"

"shikenan kinga yanzu mun zama tara gani ga Fudhal ga kuma Fahreen "

"murmushi tayi tace masha'Allah kuma kamar jikanuna suma haka suke kamar larabawa "

"aiko zanso ingansu insamu kanne ko sun fini"

dan ware ido tayi tace "sun isa sufa shekaransu 20 nema kuma mata ne ka girme su nesa ba kusa ba "

" shikenan kinga na samu kanne sai in hadasu da nawa kanwar duk dama bata kaisu ba ita shekarunta 19 ne,

amma ai ba mastala ina zasu dauke ni a yayansu "

"murmushi tayi tace da Mahnoor dai baka da mastala amma Khadijatul Islam sai ahankali,

don halinsu daya da wannan ta nuna fudhal kullum fuska a hade kamar shanu 🐂ba fara'a sai de ayi ta danne dannen waya Noor ce de yar gari"

kunshe dariyarsa🤣 yayi jin abinda ta fada akan Fudhal wanda ya kara hade fuska kamar gobara ta kama makera 😡

" ai ba damuwa Innani zan iya da ita tunda na iya zama da wayannan dodannin,

kin san fa su sai ahankali shi wannan baya son magana ya nuna Fahreen,

wataran sai ya wuni ya kwana bai kula kowa ba "

gyada kai tayi tace "mishkili kenan yafi mahaukaci ban haushi"

"shiko wannan ba abunda ya iya sai hancini da hade rai waishi kar a rena shi"

ya fadi haka yana nuna Fudhal da yayi kicin kicin,😡 da fuska yanaji yakeji kamar yayi gula a bakin Fareed,

Innani tace " Allah mai halitta dukan ku de kamar jika nuna suma kusan haka halayyarsu yake kowa da nasahi salon tabaran da raashin mutunci,

shi Sheik fetel halinsu yazo daya da wannan ta nuna Fahreen shiko wannan haalinsu daya da Islam,

kaiko kamar kara aka staga stakaninka da Mahnoor,

haka nan take sai stokala da neman magana kamar yar bera ta shiga nan ta shiga can,

yanzu nema girma ya shigo lamarinta sai ka taba ta take kula ka,

amma yanzu a zaman mun nan da anyi karar ta akalla zai kai so 3 ko 5,

ita ko Islam ta iya jibgar ya'yan mutane wai ita bata son reni in raashin mutuncin ta ya mosta kamar ta ci babu,

sai de ita bata shiga sabgar mutane shiyasa ba'a fiye kawo karanta ba,

amma inka kuskura ka shiga nata sabgar zaka san Allah daya ne, don ta iya shuka stiya iri iri,"

gyada kai yayi yace" kai ashe jikanun naki manyan kaya ne"

" wai ahaka ma shi babban yayan nasu baya baya barinsu,

yana koda su abinka da soja na sojojin yake musu,

zan iya ce maka su renon soja ne dan basun yake ajikin su in suka yi laifi"

" ikon Allah shi kuma mai ne ne sunansa"

" shi sunansa Umar Faruq wai anace dashi wai Majooo generel ne ko maiye abun nasu sai su turawa"

wani karamin daria Fareed ya sake jin yadda ta wani kwaba turancin yace " kina mufin Major General "

" san musu ne ma ni sai de su turawan ni baturiyta bace "


dan murmushi ya sake yace "MG Umar faruq ba shine sunan nashi "

gyada kai tayi tace " laa shakka fiiii haka ne tabbas haka nai suke fada masa"

gyada kai yayi yace kamar nasanshi

washe baki Innani tayi tace" ehh zaka iya saninshi ai ba abun mamaki bane duk da de ba'a nan kasar yake aiki ba acan Iraq din yake aiki"

" ayyah ina jikanun naki "


" ai sun tafi makaranta wai suna sarbis ko mai ne ne kadai tambayi Sheik shi ya sani "

murmushi ya sake don stabb ya gane mai take nufi don bayau ya saba mu'amala da stofi irinsu ba,

yasan mutane da yawa shiyasa ya iya mu'amalantar kowa sabida yana bin muum ayanda yake ne,

" ai nasan sun kusa dawowa ma yanzu suna hanya don lokaci yayi"


tsaye muke a bakin makaranata muna jiran Auwal yaazo don yau baiazo da wuri ba wani mai kwakwa da dabino Islam ta hango

tace "pls muje insiya Sis inaso"

bancae mata komai ba muka kama hanya muka je inda yake,

muka masa sallama sai da mamakin mu bai amsa ba kallo daya ya mana ya kauda kansa Islam tace

" malam sallama fa mukeyi ta fada haka a dakile "

mai dibino yace " banga daman amsawa ba lashe money kawai haka kawai na amsa ku lashe mu dan jarin da nake adanawa,

sanda fa na sai gonan gadon Innata na samu wannan jarin"

hade fuska Islam tayi tace " to ni na tambaye ka ne yadda ka samu kudin jarinka,

kuma uban mai muka maka dakake kiran mu lashe money"

"ohh rashi kunya zaku mun dama kukan anyi muku tambari ai kan haka,

ansanku da rashin kunya ako ina asarar ru kawai masu jan alhakin mutane"

cikin stiwa da hasala nace lalle kura tayi sanyi tunda har dan zomo ke jan kunnenta

Islam ta cafki maganan tace "ai bama sanyi tayi ba kasa tayi duba wannan karamin alhakin a mu yake wa maganam banza,

" ohh tantiranci zaku nuna mun to ni da kuke gani kasungumin tantiri ne don har kwana nayi a kasan gada a lagos"

mtswwwww muka hada baki wajen jan wani dogon stuka

" kai naka stiyan kadan ne and so what ma dan ka kwana a kasan gada a lagos,

wannan ma ai gayyar kazanta ne cewa zakayi kai kasungumin tantirin kazami ne ba tantiri ba"

"baku sanni bane lashe money kawai irinku nawa suka llata min jarii,

yan iska masun farin fuska sai kuyi ta far farawa mutane ido kuna rabasu da hakkin su"

Islam tace "no wonder yanzu na gane ashe banda tantirancin kazantar naka har da na iskanci,

to dan Allah kai ya akayi sense naka ya baka mu sa'annunka ne ,

kaga munyi kama da class dinka see you stupid idiot,

da gani ko fatihar sallar nan ma dakyar inka iya kai da kasamu zamu siya abunka ai gaba ta kai ka"

cike da shaka yace" ke de kika sani ehhhehh nafi karfinku kurwata ahir
End Ads