x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 4 - ROYALTY YAN SARAUTA

  • 9001 words
  • 12000 words
  • Out of 85109 words

Category: Love Stories

Views 1692

20 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
Da wannan d'an hijab din zakije school are you out of your sense "?.

Wani kala tai da fuskarta tana kallon shi innalillahi yanzu tsakani da Allah mene laifin wannan hijab d'in dama talhat ai haka yake nata ma yana da girma akan na wasu...........
"what are you looking😕"?.

Taji ya sake jefo Mata tambaya d'ora hannu tai aka gaskiya ya Ahmed bazai ta'ba barin ta tai 'kiba a gidan nan ba yanzu meye aibun wannan hijab d'in dan kawai tayi kuskure a magana ya nad'eta shiyasa yake mata irin wannan tambayar......................

"Baby".

"Na'am yaya".

"Kina son ganin fushi na ko"?.

"A'a yaya".

"To amma meyasa duk abinda kikasan bana so ke kuma shi kikeyi ban hanaku saka irin wadannan hijab d'in ba"?.

"Ka hana mu dan Allah kayi hakuri yaya bazan sake saka irinsa ba bari na sauyo wani yanxu" ta fad'a tana juyawa zata koma part d'insu a bisa tsautsayi ta buga 'kafar ta jikin qofa qara ta saki tana dur'kusawa a gun cike da azaba ta dafe gurin data bugun kafin ta d'ago tana kallon Ahmad taga shima ita yake kallo jin saukar muryar sa tai yace.

"What"?.

Fad'in hakan yasa taji idonta ya cika da hawaye maida hankalin sa yai kan qafar ganin yadda take matsa yatsan data bige yasa yasan taji ciwo ne matsawa yai kusa da ita domin ya duba mata amma saita d'an matsa daga gareshi a razane gira ya d'auke yana cewa.

"Oh is like you don't need my help right"?.

Batai magana ba prince Hamid dake tsaye a d'an nisa dasu shine ya matso yana cewa "eh bata buqatar taimakon naka malam zaka iya fecewa dama ai bakai niyyar ka taimaka mata d'in ba bayan silarka ne ta buge".

Ta'be baki Ahmad yai jin abinda prince Hamid d'in yace yana gyara tsaiwarsa ganin ya kusa karasowa yasa Ahmad ya kama qafar babyn ya matsa ta da kyau qara tai tana kuka kafin ya jinjina kai yana ficewa d'aga murya prince Hamid yai yana cewa "kaji kunya dai wallahi Ahmad kaji jiki babu 'yan dubiya haba ayi mutum muguntarsa tafi qarfinsa kai gani kake hakan ado ne ko humm d'an rainin hankalin yaro zan had'aka da Abba tunda shi ya isa dakai yayi maka magana abun ya isa haka" ya karasa maganar yana d'agota daga dur'kushen da take yace "kinga baby rabu dashi kiyi ha'kuri kinji Ahmad baida hankali kina hattara dashi karki ri'ka shiga safgarsa tunda baki laifi bama zaluntarki yake balle ki masa wani abu ya samu mafaka muje na mayar dake part d'in Mami ko gurin Momy zakije ki ha'kura da zuwa makarantar yau naga kamar qafan na miki ciwo sosai ko"?.

Kai baby ta girgiza tana d'an yarfa hannu tace "a'a ya Hamid ina son zuwa school yau akwai wani programs da za'ayi kuma harda ni a ciki sannan muna da test na biology zamu shiga qarfe sha d'aya da rabi dole naje zan iya zuwa ka rakani gun driver ya kaini" Kai ya d'aga mata yana cewa "ok baby karki damu muje da kaina zan kaiki tashi mu tafi kada kiyi late" mi'kewa tai daidai tana d'an d'ingisa qafar suka fita khairat ce bata da lacture sai qarfe hud'u na yamma dan haka batasan wainar da ake toyawa ba tana bedroom tana hutawa abinta har cikin school prince Hamid ya kaita tare da shopping na kayan cinye cinye daya saya mata tayi ta masa godiya dan tasan abinda Ahmad bazai ba kenan wai yau ace rana ce ta fito ya rakota makaranta yana lallashinta harda yi mata sayayya hum'um ranar da anyi ruwan sama mai qanqara tasan abu d'aya ne ko zai kawota saiya gwangwaje ta bazai kawota a banza ba baya aikin kawai.

Suna zaune tare da qawarta Ayrah bayan tafiyar prince Hamid fitowarsu kenan daga gurin da akai programs d'in kafin a shiga musu test duk da lokaci ya kusa saura 'yan mintuna kallonta Ayrah tai tana cewa.

"Zuhra Ashraf Sharfaddeen ya akai ne yau waye gayen daya kawo ki school ai na ganshi ko brother d'in kine naso zuwa gurin amma da naga ba driver daya saba kawo ki bane shiyasa na fasa na juyo nayi tunanin ko kin ganni amma sai naji baki magana ba shiyasa ma na tambaye ki"? Murmushi baby tai tana cewa "meyasa kika tambayi waye shi"?.

"Babu kawai dai na tambaya ne" cikin tsokana baby ta girgiza kai tana cewa "um um fa Ayrah fad'i gaskiyar ki naji".

Hade rai Ayrah tai tana cewa "um um me"? Ta fad'a tana kallon babyn ganin dariya take mata yasa ta zaro ido waje tana rufe baki tace "ke Ashraf Sharfa karfa kimin fassara ba wani abu nake nufi ba dan na tambaye ki".

"Oh to kuma nima ai bakiji nace wani abu ba ko na daiyi mamaki ne da naga kin dage kina tambaya a kansa".

"Ok kenan ba'a tambayar waye shi ko nayi laifi kenan"?.

"A'a no dan kawai kin tambaya saiya zama abun laifi to ba kowa bane yaya nane sunansa Abdul-hamid".

"Wow dama kina da yaya saurayi haka"?.

"Eh man gashi kin gani kuma aiba iya shi kad'ai bane su uku ne".

"Umm 'kwarai Ashraf Sharfa" kawai shine abinda Ayrah tace tai shiru kamar me tunani sai kuma ta sake kallon Babyn tana cewa "amma shi wanda ya kawoki uwa d'aya uba d'aya kuke dashi"? Kai ta girgiza tace "a'a shi d'an gidan Abba Aliyuddeen Sharfaddeen ne dashi da 'kaninsa ya Ahmad sai kuma Aunty Khairat ni kuma kinga Yaya na baya gida yaje Singapore karatu sunansa Shadad saini da qanina Sultan Sharfaddeen sunan kakan mu yaci".

Kai Ayrah ta jinjina tana sake kallon Baby tace "to amma Baby da alama wannan yayan naki daya kawo ki school baida jin kai kamar zaiyi kirki ba irin mutanen nan ne masu shariya ba ko"?.

"Eh tabbas wannan haka yake Ayrah Yaya Hamid akwai sauqin hali shiyasa nafi sakewa dashi ba irin su ya Ahmad ba wanda ko barci suke kazo wucewa sai kana sand'a saboda tsoron karya farka su ganka humm boss me zamani kenan dama gashi soja shiyasa zafin ran yai yawa amma ya Hamid so silent ne baida hayaniya ko kad'an".

"Gaskiya ne Baby haka nake son mutum ya kasance me faran faran ba wanda kullum fuska tana murtuke a d'aure kamar ta shanu ba".

"Ko kema kina da bros me matsa miki lamba ne kamar mu Ayrah"? Kaita girgiza tana cewa "a'a bani dashi nice babba a gurin Daddy na saidai takura Yaya Aiman wani lokacin shima idan yana gidan baya barin mutum ya sake saidai yasaka a gaba kayi ta karatu kamar zaka had'iyi dictionary kafin rasuwar umman mu amma yanzu da Daddy yayi aure gata yake nuna min sosai baya bari na shiga damuwa saidai idan bai sani ba shine yake kula dani".

"To shi kuma waye kince kece babba"?.

"Eh nice babba Yaya Aiman d'an gidan 'kanin Daddy mune tun daga yaye ya'ki komawa gidansu yake zaune a gidan mu gurin Umma na har gobe ba sosai ma yake zuwa asalin gidan mahaifin saba sai yayi kwana biyu uku baije ba".

"Ok ayya Allah sarki Ayrah dama mahaifiyarki ta rasu"? Kaita d'aga a sanyaye tace "ta rasu shekaru uku da suka wuce" kai Baby take girgizawa cikin tausayawa tace "Allah sarki Ayrah sannu Allah yayi mata rahma".

"Amin Baby nagode tashi muje kinga an fara shiga maybe lokaci yayi ni saitin agogo na ya goce" ta fad'a tana kallon agogon dake d'aure a hannunta mi'kewa Baby tai tana cewa "ok ni nawa a saice yake idan muka fito saiki gyara nakin muyi sauri wannan lecturer ba kirki ya cika ba shima" wucewa sukai aiko suna shiga ya fara tare kofa yana cewa.

"Baku masu taku ba wa zakuyi wa iyayi ni malamin kune ba saurayin ku ba dan haka saiku tsaya idan na rubuta musu sunyi rabi kwa shiga" ya fad'a tare da shigewa ajin yaja kofar ya rufe 'yan matan dake waje sai ta'be baki suke suna kad'a kai domin babu wanda ransa ya 6aci akan abinda lecturer yace dan dama mafi yawansu ba karatu suke ba shashanci kawai suke da samari a makaranta ayo wankan 'kure maki azo makaranta dan a burge samari da malamai koda ace ya barsu ba test d'in zasuyi ba shiyasa ma ya hanasu shiga saboda karsu hana sauran masu niyya su shiga class su dagula musu lissafi,, saida suka gama suka fito sannan yasa suma suka shiga su zana iya su.

Su Baby kam gurin da suka tashi nan suka koma Ayrah ta gyara agogonta suka cigaba da hirarsu har lokacin tashi yayi da yake gajeriyar rana ce Ayrah bata tafi ba saboda taji cewa prince Hamid ne zai dawo d'aukar Baby so take taje su gaisa suna tsaye suna zancen su da dariya mota tai parking da mamaki Baby take kallon motar wannan ba motar prince Hamid bace Kuma ba da ita driver yake zuwa d'aukarta ba to waye kodai Aiman yayan Ayrah ne yazo d'aukarta......................

Katse tunanin da take tayi ganin an bud'e kofar da sauri ta d'ago tana kallo taga waye kallon farko fuskar Ahmad ta gani wani irin zaro ido waje tai tana d'an jada baya kad'an ta murje idonta ta sake bud'ewa sai kuma taga prince Hamid ne mamaki ne ya kamata duk da dama suna fusgar kama amma dai yanxu itafa fuskar Ahmad ta gani 'kiri-'kiri kodan tasa tsoron sa a ranta ne?...............

"Baby mene ya firgita ki"? Taji muryar prince Hamid da sauri ta dawo daga tunanin da take tana kallon sa ta girgiza kai tana ri'ke hannun Ayrah tare da yin murmushi tace "babu komai Yaya Hamid kawai kallon farko naga ka fito da fuskar Yaya Ahmad ne saida na sake runtse ido na bud'e kuma sai naga fuskarka wallahi Yaya Hamid bakaji yadda zuciyata ta buga ba na d'auka da gaske ya Ahmad d'in ne yazo d'aukata inaga da kafin muje gida sai zazza'bi ya rufe ni".

Murmushi ya sakarwa zancen nata yana d'an girgiza kai yace "haba Baby tsoron da kikewa Ahmad ya wuce misali mene abun zazza'bi dan kawai yazo d'aukarki"?.

"Uhm ya Hamid dole nayi zazza'bi nasan haka kawai ya Ahmad bazai zo d'aukata ba saidai idan dama akwai abinda ya shirya".

"Abun daya shirya kuma? Babu wani abu Baby kawai fa kece kika rud'a kanki dashi tun farko da baki nuna jin tsoron saba da babu abinda zai faru Baby bakisan mene Ahmad yake ji a kanki ba da irin kallon da yake miki da ace zaki fahimce ni dana fad'a miki wani abu dazai baki mamaki wanda ke har gobe baki sani ba amma shikenan dai muje ko" ya fad'a yana nuna mata mota juyawa tai tana kallon Ayrah wacce ke kallon yadda suke magana a sake cike da burgewa murmushi Baby tai mata tana cewa.

"Ayrah kizo man ku gaisa ga yayan nawa Yaya abdul-Hamid ya dawo" ta fad'a tana kallon prince Hamid wanda ya kalli Ayrah taci gaba "Ayrah ga Yaya abdul-Hamid ku gaisa" kai Ayrah ta jinjina tana d'an sake fuska tace "ina yini"?.

"Lafiya kalau ya karatu"?.

"Alhamdulillah" ta fad'a tana kallon Baby wacce tace "Ayrah ki shigo ya fara kaiki gida idan ya sau'ke ki sai mu wuce ko"? Kai Ayrah ta girgiza da sauri jin abinda take fad'a ta sani matukar wani yaga sanda aka sauke ta a cikin su Abidah ko Nadiya wani ya ganta ta shiga uku sharri zasu 'kulla mata a gurin Daddy musamman da yanzu ba goyon bayanta yake ba ya watsar da ita.....................

"Ayrah muje man".

Baby ta fad'a tana ri'ko hannunta tana janta sake girgiza kai Ayrah tai tare da kankaro murmushin dole tace "a'a Baby nagode karki damu sai ranar Monday insha Allahu" ta fad'a tana sake kokarin daidaita fuskarta dan kada su fahimci komai had'e rai Baby tai tana cewa "ai dama ba ro'ka kikai ba amma a tunani na Ayrah bai kamata dan kawai nace ki shigo muyi dropping d'inki zaki 'ki ba yarda ta dake tafi haka ko"? Shiru Ayrah tai jiki a sanyaye bataso ace sun gane tsoron 'yan gidansu take saboda haka kawai ta ha'kura badan taso ba sai domin karta bar musu kokwanton meyasa ta'ki yarda su kaita gida tun daga nesan gidan tace su sau'keta tsayawa prince Hamid yayi ta sauka tayi musu godiya sosai kuwa domin taji dad'in yadda suka nuna mata kulawa da murmushi akan fuskarta ta bud'e gate d'in ta shiga saidai lokaci guda taji farin cikin nata ya koma ciki sakamakon ganin motar Nadiya data Abidah a parking space kenan suna gida harsun dawo innalillahi wa inna ilaihi raji'un ji take kamar ta juya inama tana da inda zataje da wallahi tabar gidan nan har abada saidai ya zatai da rayuwarta tunda nan ne gidan mahaifin ta haka zataita ha'kuri har karshen wahalar ta yazo tunda karfofi sun zo sun cika musu gida sun fita sakewa da gadara.................

Tana shiga parlor ta gansu a zaune kowacce ta d'ora kafa d'aya kan d'aya da waya a hannunta tana shafawa shigarta da sallama yasa suka d'ago suna binta da wani irin ba'kin kallo babu wacce ta amsa mata sai tsawa da Nadiya ta daka Mata tana cewa "ke sokuwa zomin nan" a tsorace Ayrah ta juyo tana kallonta lokaci guda jikinta yad'au rawa ganin ta kasa takowa ta dawo Abidah ta ta'be baki tana cewa "ai baki da isar da zata dawo miki saidai ki tashi kije ki jawo jaka kalli man ki gani tafi 'karfin zuwa haka ne amsar tsaiwarta" ta karasa maganar tana sakarwa Ayrah harara kai Nadiya ta jinjina tana cewa "tabd'ijan aiko yau zataga hauka nice zan tashi naje na jawota saboda Ina so tai min aiki? Hum'um wallahi bazan je inda take ba saita dawo nan har gaba na naci uwarta" dariya Abidah tai tana cewa "ai shikenan bari muga yadda wannan comedyn zai kasance kince itace zata tako tazo miki ita kuma taja ta dake tace bazata zoba mukam yan kallo ne" ta fad'a tana sake gyara zama cizon yatsa Nadiya tai tana sake daka mata sabuwar tsawa tace.

"Zaki zo min nan ko saina ci uwar data haifi uwarki matsiyaciya tinkiya baki gane yaren da nake miki ba saina tashi a kanki"?.

Cikin jin takaici da d'acin maganar da Nadiya ta fad'a a kanta Ayrah ta juyo tana dawowa tare da dur'kusawa domin wannan sawar Hajiya Khubura ce tasa indai sukai kiranta tazo ta tsaya musu a tsaye su mata shegen duka tana dur'kusawa Nadiya mi'ke tana danna kanta a 'kasa ta dun'kule hannunta ta tuma mata dundu mai karfi a bayanta tana hankata har saida ta wuntsila kanta ya bugi center table na glass dake tsakiyar parlon da 'kafa Nadiya ta sake taketa tana cewa.

"Mi'ke min tsaye bagidajiya wannan ba komai na miki ba cikin ukubar dazan d'and'ana miki tashi ki wuce part d'in mu ki wanke mana hijab dinmu na islamiyya da nikaf kuma wallahi idan basu fita ba sai naci ubanki" ta karasa maganar tana mikar da ita tashi Ayrah tai damuwa da ba'kin ciki ya gama rufeta da'kyar ta juya tana shiga part d'in nasu aje wayar hannunta Abidah tai tana mi'kewa tace.

"Bari nabi bayanta kar tayi Mana sata kinsan 'yar 6arayi ce" Nadiya ma dake tsaye bin bayanta tai tana cewa "toni kuma nayi zaman me nima biyo ki zanyi naga aikin dana sakata zatai ne ko kuma tafi 'karfi'' shiga sukai suka tararta a cikin toilet ta d'aure hijab din'ta tana wankewa Kai Nadiya ta jinjina tana juyawa ta bud'e fridge d'in dakinsu ta d'auko karamin bokiti fal da ruwa da alama yana da matukar sanyi domin bokitin har ra6a yake kuma saboda ita suka cikashi da ruwa su saka a fridge yayi sanyi juyawa tai tana shiga toilet d'in cike da mugunta ta d'aga batare da Ayrah ta sani ba sai jin saukar sassanyan ruwa tai a jikinta 'kara ta saki cikin firgici jikinta yana kakkarwa ta d'ago tana kallon Nadiya data saka yatsanta saman lips dinta alamar tai mata tsitt batasan jin koda tari kafin tace.

"Ci gaba da abinda kikeyi ko na fasa miki baki" Ayrah batace komai ba ta du'ka taci gaba da wanki yayin da Abidah ma ta d'ebo wasu ruwan a jakar faro tana zuwa tace "da wannan ruwan zaki wanke mana an fad'a miki mu matsiyata ne irinki da zamuyi wanki da ruwan fanfo ki dau'ki wannan kiyi mana shi kuma kiyi sauri kizo ki d'ora mana abinci wallahi na baki minti goma idan baki fito ba sai mun fasa miki jiki zaki gani kuma karki fito muna daidai dake" tana fad'in haka ta juya hawaye Ayrah ta goge tana jin yadda sanyi yake ratsa mata ga6o6i tana wankin hawaye na d'iga a cikin ruwan harta gama ta fita garden ta shanya musu sannan ta dawo ta d'ora musu girki data gama tana ajewa a dinning zata wuce part d'inta Abidah tai wuf tace.

"Gidan ubanwa zakije dama mun sallame kine"?.

Tsayawa Ayrah tai bata iya koda motsa le6enta ba saboda wani irin zazza'bi da taji yana shirin kamata dawowa tai Abidah dake binta da kallon banza a wula'kance tace "ki wuce bedroom d'in mu ki gyara mana shi tas har 'kar'kashin gado ki sharo shi sosai sannan ki had'a min ruwan wanka" numfashi me zafi Ayrah ta fitar muryarta na kakkarwa saboda sanyin AC dake 'kara taso mata da zazza'bin da'kyar tace "bani da lafiya bazan iya gyarawa ba saidai anjima" zaro ido Abidah tai tana cewa "ina ruwana da zazza'bin ki zaki wuce ki gyara mana ko saina d'auke ki da mari" tana rufe baki taji an bud'o kofa ganin wanda ya shigo ga wani irin kallon 6acin rai da yake binsu dashi yasa da gudu suka mi'ke a gigice suka shige part d'in Hajiya Khubura ajiyar zuciya Ayrah ta sauke tare da fad'in alhamdulillah daidai Aiman ya karaso ta kalleta ganin yadda take rawar d'ari yace.

"Baki da lafiya ne"? Kaita d'aga muryarta na rawa tace "eh zazza'bi nake ji".

"Dama baki da lafiya kuma baki fad'a min ba me ya ji'ka miki jiki haka"? Ya fad'a yana kallon yadda hijab din'ta yake ji'ke ko bata fad'a ba yasan su Abidah ne sukai mata haka "Ina tambayarki kinyu min shiru"?.

"Abidah ce ta watsa min ruwa" ta fad'a hawaye yana zubo mata kaiya jinjina yana kallon kofar part din Hajiya Khubura da suka shiga yace "ok kinga kiyi
End Ads