TASHI ZAMU ZO MUSHA BUSA RANAR AUREN NAN MAMA🤣.
Nice zanyo gudunmawar ruwan da za'a yayyafawa Maryam idan ta suma🙊 kufa FANS me zaku kawo mata kodan idan kukayi Mata sannu ma ya wadatar😂.............✍️YUSRAH MUSA ABUBAKAR CE.
Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë mai tambarin yma dutse Jigawa state.
See you tomorrow morning be with me at always my lover's tnks for ur supports we will meet again ina sonku masoya godiya sosai sosai godiya da jinjina gareku thanks you so much I really appreciate it Yusrah ce.
17~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Shakirnah.
Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿
@YUSRAHMS CE.
Page 33 & 34.
Bayan sati d'aya Amaan yana gurin aikinsa Ashraf yaje ya sameshi domin su karasa maganar da suka fara yayi sa'a kuwa a lokacin baya aiki yana free zama yayi suna gaisawa cikin sakin fuska ya kalleshi yana cewa "ya ake ciki ne banker ko kud'i ka kawo min yau nima naje na huta da shan shurba"? Dariya Ashraf yai yana cewa "eh abinda yafi kud'i na kawo maka maganar mu nazo mu karasa akan Maryam yaya kukai da ita ko baka fad'a mata ba"?.
"No na fad'awa Mama kaje ne"? Kaiya girgiza yana cewa "banje ba ai baka bani amannar naje d'in ba sannan bansan ka fad'a matan ba idan ka amince ko ayau zan iya zuwa muyi maganar da ita".
"Ok karka damu Ashraf duk lokacin da kake free kaje ku gaisa ka fad'a mata komai saboda zatafi fahimtarka akan nina sameta na fad'a mata tunda bansan me yake ranka ba shiyasa gara kaje zuwa dakai yafi sa'ko ko"?.
Kai Ashraf ya jinjina yana cewa "Eh tabbas gaskiya ne haka ne amma kasan inada matsala na rasa meke damuna haka kawai ina jin tsoron tarar mace nace mata ina sonta ne sai naji wani irin kwarjininta ya kamani" murmushi Amaan yai yana cewa "tab aiko zaka Sha wahala a gurin mace da zarar ta gane kana jin tsoronta shikenan ta samu kofar da zata ri'ka juyaka kamar waina ka daina fad'a ma kar sujika kawai yanxu idan ka shirya koda yaushe ne kaje ku gaisa" kaiya jinjina yana mi'ka masa hannu suka sake gaisawa yana cewa "ok nagode sosai Amaan insha Allahu zanyi kokari naga naje mun had'u zan tafi ka gaida min Mama kafin na samu na 6ulla"?.
"Ok insha Allahu zata ji".
Shiru Amaan yai bayan tafiyar Ashraf yasan da akwai ya'ki yau indai ya koma gida ya fad'awa Mama shiyasa a take ya yankewa kansa shawara kawai gara yayi shiru idan Ashraf d'in yaje shikenan ai dai sunsan ba shine ya kawo Shiba balle Mama tai fushi dashi yarda yayi da shawarar abinda zuciyarsa ta yanke masa domin hakan ne mafita tunda ya lura Mama ko kad'an batai na'am da maganar Ashraf yana son Maryam ba ya rasa meye dalili amma yasa a ransa zai bincika ya gani.
Watan Nadiya guda cur a asibiti sannan aka bata sallama ta dawo gida badan ta warke ba Hajiya Khubura ce to gaji da zaman can din ganin abu ya'ki ci ya'ki cinyewa ana magani kamar ba'a yi 'kafa kullum a kumbure ba sau'ki kuma iya kokarinsu likitocin sunyi sun rasa inda matsalar take a hakan tana iya tad'an dafe wani sanda da suka bata tana tafiya dashi amma ita kad'ai dai bazata iya ba saidai idan ri'keta za'ai kullum tana zaune guri d'aya tunda tafiya wahala take mata ba ranar da zata fito ta fad'i batai kuka ta tsinewa mahaifiyar Sabit ba dashi kansa Sabit d'in daya yaudareta saboda yana so ya aureta ya'ki ya fad'a mata asalin mahaifiyar sa Ashe duk matar da take zarya ba uwarsa bace uwar kud'i ce siyanta yayi yanzu tana kallo babu yadda ta iya da Ayrah saidai ta zuba ido idan Abidah tana yi mata masifa da zagi amma banda ita domin ba wannan ne a gabanta ba damuwarta ta warke kawai shine a ranta.
Yauma tana zaune a parlor ita kad'ai babu kowa sai iya khaleel shi kuwa ba'a cikin parlon yake ba yana can gefe kan dinning ya saka bluetooth a kunne sai kad'a kai yake kamar 'kadangare yana murza yatsunsa alamar kid'an yana shigarsa fitowa Ayrah tai a shirye zata tafi school da littafi a hannunta sauri take ma dan taso makara ganinta yasa Nadiya cewa "ke d'auko min ruwa a fridge d'in bedroom d'in mu ki kawo min yanzu karki 6ata min lokaci" kallonta Ayrah tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta aje book din nata tana shiga part d'in ta d'auko mata ta dawo mi'ka mata tai bata kar'ba ba sai wata harara data sakar mata tana cewa.
"Oh bazaki aje ba dole saina kar'ba 'yar isa"? Ajewa Ayrah tai tana shirin d'aukar littafinta cikin tsawa Nadiya tace "ke jaka ki mi'ko min cup mana da uban me zansha ruwan kika aje min zaki tafi wato yanxu rainin ki kika tattare ya dawo kaina saboda kinga ba iya tashi zanyi cikin sauri ba balle na kamaki ko"? Wani irin kallon Ayrah ta aiko mata fuska a d'aure tace "saiki nemi jakar ta mi'ko miki kofi kisha ruwa amma badai niba domin ni mutum ce idan baki sani ba ki sani Ayrah Abdul-Kharim nake da kike maganar dan naga kina zaune guri d'aya ne nake miki haka ina ruwana da zamanki dama nina zaunar dake balle ki huce a kaina tashi kiyi yawonki man waye ya hanaki ina tunanin nan a gidan mijin mahaifiyar ki kike ba'a gidan yari ba balle kice baki da 'yanci sai yadda akai dake ai daman kwad'ayi mabud'in wahala tunda kika bi son zuciya kina tare da nadama Dana sani yanzu kika fara gani sai a gaba ma domin hakkina bazai ta'ba barinku kuji dad'i ba kuma zaki gani" tana fadin haka tai gaba takaici da ba'kin ciki ne suka rufe Nadiya ji take inama ace tana da damar tashi lafiyarta kalau yau babu abinda zai hana ta karyawa Ayrah 'kafa ta fasa mata baki cikin 'karaji tace.
"Ke dan kan uwarki dawo min nan idan ki isa"? Batare da Ayrah ta juyo mata tace "na isa harna wuce inda kike tunani amma baki da matsayin da kika isa na dawo miki idan kin matsu dani ki taso kizo ki sameni ina daidai dake" sabon ba'kin ciki ne ya sake kama Nadiya ganin yadda Ayran take tsaye tana jiran taje inda take d'in kuma ta juya mata baya ba ita take kallo ba kamar zatai hauka tace.
"Wallahi tallahi bashi kikaci kin d'aukowa kanki masifa da bala'i kin d'ebo ya'ki Allah ya bani lafiya na warke zama saiya gagare ki tsabar dukan fitar hankali dazan nad'a miki a gidan nan ni dake ne" baki Ayrah ta ta'be tana cewa "karyar banza kenan na saba jin irin haka a bakin ki sau tari kuma babu wata tsiyar da kike yi sai kuri dama Abidah ce take ganin damata Kuma itama tunda na goge mata baki a jikin bango take shakkata kodan ke baki sani ba amma yanzu kin sani saura ke yadda na fitar da jini a bakinta kema wadannan ru6a66un hakoran naki sai sun fitar dashi ki jira dawowa ta" Nadiya tana kallon Ayrah ta fita ranta in yayi dubu ya 6aci tana zaune Ayrah ke fad'a mata haka yarinyar da suke cin ubanta take tsoron su amma yau itace take fad'a mata maganganu masu razanarwa da nuna alamar ta fara d'aukar fansa...................
Jin 'karar bud'e kofa yasa ta mayar da hankalinta gurin ganin Hajiya Khubura ta fito cikin shiri alamar anguwa zata fita ta kalleta idonta yana kawo hawaye cikin takaici tace "wallahi Umma indai na warke saina kashe Ayrah a gidan nan saita ga ukuba da bala'i zatasan wace ni" dakatawa a kanta Hajiya Khubura tai tana kallon 'kafar tata cike da fargaba tace "metai miki ko 'kafar taki ta taka"? Kaita girgiza tana cewa "ba gara ta taka min 'kafa ba akan irin munanan kalaman data fad'a min wai yaushe kukai sake yarinyar nan ta Raina mutune har take cewa ta gurjewa Abidah baki saura ni".
"Au haka tace"?.
"Haka tace min harda wani wai minbi kwad'ayi da son zuciyar na auri wanda iyayensa basa kaunata sunci ubana na dawo gida kema ba 'kyale ki take ba yanzu baki da wata martaba da Zaki saka ta abu tayi balle ni banza wacce kashin me gadi ma yafini daraja a gidan nan yanzu" zaro ido Hajiya Khubura tai tana cewa "Wai du Ayran ce me fad'in wannan maganar"?.
"Itace man yanxun nan ta fita zata tafi school kinga ruwa nan akan nace ta d'auko min kofi nasha bakiji irin zagin cin mutumcin data ri'ka min ba wai ai tasan babu abinda na isa nayi mata ina zaune a daskare guri d'aya kamar bishiya Allah yasa karna warke Allah yasa 'kafar ta ru6e haka tace min" Nadiya ta karasa maganar tana sakin kukan 'karya cizon yatsa Hajiya Khubura tai tana jinjina kai tace.
"Aidai addu'a tai Allah yasa karki warke ko? Humm yau kuwa zan gwada mata rashin imani bari ta dawo wallahi saina saka Abidah tai mata dukan mutuwa ta 6alla mata tata 'kafar itama ta zauna guri d'ayan sannan mu hanata abinci yunwa ta kashe mitsiyaciya bari naje anguwa na dawo wannan case d'in har gaban Alhaji sai yaje yaja mata kunne karta kuskura ta sake miki fatan kafarki ta ru6e idan kuwa bai kulaba zaiga hauka ganin idonsa wallahi sai mun kasheta a gidan nan" ta karasa maganar tana huci saboda yadda ranta yake turiri ta kalli Nadiya wacce ta zubawa kafar ta ido tace "bari na dawo Nadiya ki kula sannan karki damu da abinda ta fad'a indai tsautsayi ya dawo da ita gidan nan da kaina zan jawo miki ita har kusa dake na zauneta kiyi mata tsinannan dukan da zata kasa tashi bari Allah ya dawo dani lafiya itama ta dawo" ta fad'a tana wucewa ta fita duk abinda suke cewa khaleel yana zaune yana sauraron su baice musu 'kala ba har Hajiya Khubura ta fita saida ya gama abinda yake zai mi'ke ya kalli Nadiya yana cewa.
"Ke dan ubanki idan Umma ta dawo ki fad'a mata sa'ko na idan tsautsayi yasa ta kawo miki Ayrah kuka daketa na rantse da Allah wannan shegiyar 'kafar taki saina mayar Miki da ciwonta d'anye saina take ta da takalmi na mutsustsu ke ta yadda bazata sake moruwa ba saidai a yanke dama ba 'karyar da kikawa Ayran kenan ba alhali bata fad'a humn zan wakilce ta naci ubanki keda Abidan Allah yasa ku daketa na gani" yana fad'in haka shima ya fita daga gidan aka barta ita kad'ai domin Abidah ma tana school gashi Hajiya Khuburan ma ta fice kuka kawai Nadiya ta kamayi saboda ba'kin cikin hanata taci uban Ayrah da yayi tasan tunda yace haka indai tsautsayi yasa ta daketa ba karamin aikinsa bane ya take mata kafar ya dawo mata da d'anyen aiki tasan ba hankali ya cika ba ga6o ne indai ya fad'i magana ka yarda gaskiya ya fad'a maka bai cika ya fad'i 'karya dan barazana ba...................
***Tunda Ashraf sukai magana da Amaan akan zaizo gurin Maryam bai ta'ba zuwa ba saboda tsoron a yadda zata kar'beshi tunda yasan halinta 'yar rainin hankali ce yana so ya gwada zuwan ya kasa abun na matukar damunsa karshe dole ya samu abokinsa ya fad'a masa matsalar sa shine ya 'karfafa masa gwiwa ya bashi shawarwarin ta yadda zaije mata da yadda zai fara ya tsike ya nuna jarumta kar yayi wani abu da zata gane yana jin shakkar tararta da maganar soyayya yarda yayi da shawarar ya kuma saka a zuciyarsa zaije ya gwada sa'arsa fatansa ta amince masa indai yaga ta amince saboda gudun matsala abun bazai dau'ki dogon lokaci ba za'ai bikinsu kawai hakan shine mafita dayin maganar tasu yakai kusan kwana goma baije inda take ba duk da yace zaije sai daga baya har Mama da Maryam sun manta da wani Ashraf yace zaizo yana sonta kamar a mafarki rana tsaka sai gashi yayi musu dirar mikiya ba sanarwa ba zaton zuwansa ganinsa yasa ran Mama 6aci da'kyar ta amshi gaisuwarsa saboda wani irin damuwa da fargaba daya lullu'be ta domin yau Abban su Maryam d'in yana gida kuma yaga Ashraf d'in harsun gaisa ma saidai baisan me yazo yiba ya d'auka kawai yazo a gaisa ne ta Nan Mama taji d'an dama-dama shiyasa da taga Abban bai fahimci komai ba tayi saurin tashi jiki na rawa ta tafi part d'in su Maryam a lokacin tana zaune tasa waya a gabanta tana kallon photon Ahmad🤔 taga mama ta shiga d'agowa tai da murmushi saboda nishad'in da take ji a wannan lokacin ta kalli Mama ganinta a hautsine yasa tace.
"Lafiya Mama"?.
Kaita girgiza mata tana waige-waige kamar mara gaskiya tai kasa da murya cikin rad'a tace "ke Maryam yau mun shiga uku zamu tozarta wannan d'an iskan yaron ne yazo"? Cikin rashin fahimta maryam tace "wanne yaron kuma" dan ita ta manta da shafin wani Ashraf ma balle ta damu da yace yana sonta......
"Kefa Ashraf nake miki magana akai yanzu ya shigo muna tare da Alhaji ya gaida mu dad'in da naji ma Allah yasa alhajin bai gane gurin ki yazo ba ya d'auka ziyara ya kawo mana Maryam tashi kije kici kan uwarsa dan babansa kiyi masa kaca-kaca ki wulakanta shi ki wanke min shi tas da ba'ka'ken maganganu ta yadda gaba bazai marmarin 'kara zuwa gidan nan da sunan gurin ki yazo ba dan naga alama indai mukai wasa zai wargaza mana shirinmu da zarar Alhaji ya sani shikenan ya hada mu da masifa dole ki aure ni kuma abinda bana fata kenan Allah ya sauwake miki wannan kaddarar ta sameki" zabura Maryam tai tana cewa.
"Wallahi bai isa ba bazan aureshi ko maye ne shi saiya barni wai ana so dole ne"?.
"Inaga shi a gidan ubansa ana yi dolen shiyasa ya nace saike bayan ga 'yan Mata nan a gari kamar kayi sannu a baka".
"Humm aiko kuwa ya taro masifar da tafi karfinsa wallahi saina sakashi kuka da idanunsa idan bai rabu dani ba".
"Kinga Maryam ba magana ba anan mu kad'ai ne baisan kinayi ba tashi zakiyi kije yana can parlon ba'ki ki tabbata kinyi abinda zai 6ata masa rai Wanda zaiji har abada baya so ya sake kallonki ma tashi maza kiyi sauri kafin Alhaji ya sake dawowa tunda mun samu ya fita" mi'kewa Maryam tai a fusace ta dau'ki mayafinta tana fita ranta a 'bace zuciyarta tazo har wuya ta cika dam da fushi burinta tana zuwa ta d'aga hannu da farko ta fara daukeshi da mari kafin ta koro masa munanan kalamai turus tai data shiga ta tsaya tsam ganin da wanda suke tare suna zance harda tafawa suke sun dariya shiru tai tana huci d'agowa sukai duk su biyun suna kallonta ganin yadda Ashraf ya kureta da kallo ji take kamar taje ta rufeshi da mugun duka wani irin ba'kin kallo 'kasan ido tai masa sabida ganin Amaan yana gurin da ace baya nan yau da Ashraf ya gane wacece ita..............
Muryar Amaan taji yace "ke tsaiwar me kike anan tsabar raini tun d'azu kinyi ba'ko baki kawo masa ko ruwa ba balle kizo ku gaisa me kika tsaya yi a part d'in naku kije ki kawo masa abun sha yanzu" kallon amaan dayai maganar tai tana sake jin sabon takaici ya rufeta ko iya bud'e baki ta bashi amsa batai ba sai juyawa datai har hawaye yana zubo mata ta d'ebo masa drinks ta kawo ta wuce kitchen ta had'o masa abinci da kayan cinye-cinye ta dawo tsaye tayi saboda ba zama ya kawota ba hakan ma tsoron Amaan yasa tayi amma yau da ace baya gurin nan parlon nan yayi mata kad'an saboda irin guguwar bala'in data d'auko zata saukewa Ashraf.
Mi'kewa Amaan yai yana shirin fita ya kalleta kallo me cike da gargad'i yana jinjina kai yace "ki zauna kuyi magana ta fahimta dashi" kallonsa Maryam tai kamar zata fashe da kuka saboda da yasan yadda take jin tsanar Ashraf d'in nan a ranta da baiso ya nuna mata fuskarsa ba balle harta xauna inuwa d'aya dashi suyi wata magana Amaan yana fita Ashraf ya kalleta ganin bata motsa daga inda take tsaye ba yace..
"Bismilllahi zauna man ba jimawa zanyi ba akwai uzurin dazan tafi nima" wani irin kallo tai masa tana cewa "Ashraf meya kawoka gurina me zakai min mene damuwarka dani meye tsakanin mu da Dole saika shiga rayuwa ta meye had'in biri da kada"? Shiru yai ya zuba mata ido yana kallon ta dama yasan za'ai haka tunda yaga a yadda ta shigo kamar a fusace take kodai bazata amince masa bane domin labarin zuciya a tambayi fuska..........
"Meye ka zuba min ido kana kallona ka amsa min tambaya ina son zan tafi bazama ya kawoni inda kake ba" da mamaki Ashraf ya kuma kallonta yana jinjina kai tabbas bazai samu kar6uwa ba alamar 'karfi tana game 'kiba kalamanta sun nuna masa amsa tun bai furta ba................
Sanyi ne yaji ya shiga ratsa shi dabin jikinsa kallon kayansa yai yaga yadda ruwan juice yake bin farar shaddar dake jikinsa tsananin mamaki ne ya kamashi juice ta zuba masa a jiki kan bala'i bai farga ba ta d'auko miyar shinkafa data d'ebo tana watsa masa a gaban kirjinsa tare ta wulli da kwanon tana nunashi da yatsa fuskarta a 6ace tace "daga yau karka kuskura na Kara ganin wannan jakar fuskar taka ni nafi karfin auren irinka niba sa'ar ka bace ka kama kanka a kaina bana sonka bana son me sonka idan Kuma ana so Dole ka fad'a min da'ki'kin banza jaki wofi ka turo yaya Amaan nace bana so yanxu kuma ka d'ebo kafa kazo gidanmu to bari kaji duk abinda kake ji dashi nafika indai ka sake zuwa gurin na xakaga d'anyan kai sai nayi maka abinda har ka mutu bazaka manta Dani ba banza kawai" mtswww taja zazzafan tsuka tana barin parlon shiru Ashraf yayi yana kallon jikinsa zuciyarsa na tafasa da irin maganganun data fad'a masa tun kafin ya furta yana sonta kamar shi Maryam ta zauna tana wula'kantawa ko bara yazo gurinta ya kamata ta karrama shi balle da kimarsa ta ganshi huuuuhhhh wani irin numfashi ya fitar me zafi da 'kuna tare da