"Innalillahi khairat meya samu babyn kuma yakai ta fad'i"?.
A rikice Khairat tace "Momy baby bata da lafiya da zazza'bi ta kwana dan Allah ki kira ya Hamid yazo ya dubata".
"Hamid ya tafi hospital bari naje Ahmad ya kirashi waya na network d'inta ya sauka " Momy ta fad'a tana ficewa mi'kewa Khairat tai ta nufi frigde zata d'auko ruwa ta shafawa babyn amma me itama tana mi'kewa juwa ta debeta ta fad'i a gurin, tare da Ahmad Momy suka shigo ganin itama Khairat d'in ta fad'i yasa hankali tashe Momy tace.
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un meye yake damunsu ne kodai sunci wani abu me guba ne"?.
Shiru Ahmad yai ya zuba musu ido yayin ta Momy ta shiga kai komo a parlon hankalinta inyayi dubu ya tashi har Hamid ya shigo Shima dai babu nutsuwa a tare dashi ganin ba iya baby bace harda Khairat yasa mamki ya rufe shi yana kallon Momy yace.
"Meya faru dasu haka suka fad'i a lokaci guda".
Kai Momy ta girgiza tana cewa "ban sani ba Hamid bansan meke damunsu ba kawai ka dubasu" Momy ta karasa maganar daidai wasu bayi masu ayyuka a part d'in sun shigo ta umarcesu dasu shiga bedroom d'in Khairat su ciro katifar dake kan bed d'in su kawo mata ita parlor, amsawa sukai kamar ta basu umarni suka d'auko suna kawowa Hamid ne ya taimakawa Momy ta dorasu akan katifar sannan tana tsaye tace ya dubasu, hum yayi mamaki baby zazza'bi take kuma a gwajin dayai Mata ya sauka to amma Khairat fa baiga komai ba saidai gaskiya dika su biyun suna bu'katar a qara musu ruwa, kallon Ahmad yai wanda ya had'e rai kafin ya jinjina kai yana d'aurawa kowaccensu drip a hannunta da zaiyiwa Momy wata magana amma sakamakon da Ahmad a gurin kuma zasu iya yin hayaniya yasa kawai ya share daya kammala abinda dazai musu ya koma hospital yace idan ya dawo zaiyi magana da Momyn, Ahmad ma bai zauna ba ya fita sai iya Momy ce a gurin su ta d'auko bargo tana rufesu domin sunyi barci.
'Dorayi^^^^
____Tafe wata budurwa take ita kad'ai ko ganin inda take jefa qafarta batayi saboda irin damuwa da tunanin datai zurfi a cikinsa ga kuma hawaye yana zuba na ba'kin ciki da takaicin rayuwar gidansu da halayyar yan gidan musanman matar ubanta da kuma shi kansa mahaifin nata wani lokacin har tunani take anya shine ya haifeta ba tsintar ta yayi ba uba na qwarai bazai ri'ka cutar da yarsa irin haka ace ba kula ba walwala ba nuna qauna magana ta fatar baka wacce zatasa taji dad'i bazai Mata ba ya'ki mayar da hankali akan iliminta amma yake biyawa su Abidah da Nadiya bashine ya haifesu ba ita da take 'yar hatta kud'in da zata hau napep baya bata kullum a qafa take zuwa makaranta amma su Abidah kwanan nan ya sauya musu mota ta zuwa school........ kuka ne me qarfi taji yana tunkaro ta cikin dauriya ta danne taci gaba da tafiya ga masifar gajiya datai ga yunwa kuma ta tabbata saita koma zata d'ora musu girki ta gama ta dauko ta kawo musu dining tai serving kowa kamar wata bewar su suyi kaca-kaca da dinning din ita zata gyara ta tattare kwanuka ta wanke ga su sata wanki suna zaginta da injin wanki a gidan amma tsabar sun karanci mugunta ruwan da zatai musu wankin ma sai sun zuba Mata qanqara d'uma d'uma a ciki yadda hannunta zai sanqare haka zasu tulo Mata kaya ta wuni a tsakiyar rana tana wankewa su bushe ta goge ta kaiwa kowa cikin wardrobe dinta abin nan yana mugun ba'kanta Mata rai rashin uwa maraici yaja Mata haka da ace mahaifiyar ta tana nan bazata tozarta haka ba share hawaye tai har ta kusa ta tuna littafinta ta mantoshi akan kujera cikin class da sauri ta juya zuwa FCE d'in batare data tuna cewa hakan zai zama Mata laifi bane a gurin Hajiya Khuburah gashi kuma data koma bata ganshi ba sannan babu students ko d'aya balle ta tambaye su ha'kura tai cikin damuwa ta sake d'auko hanya ta dawo gida tana bud'e gate d'in gidan saida gabanta ya fad'i ganin motar Daddynta ya akai yau ya dawo da wuri bayan kullum sai magriba yake dawowa gida yau kuma tun la'asar shiga tayi jiki a sanyaye ta bud'e kofar falo da sallama shiru kamar ba mutane babu wanda ya amsa Mata sai tu'kuicin baka'ken harara data samu kaita sunkuyar zata wuce cikin tsawa hanya Khuburah tace.
"Zo nan dan uwarki".
Jin abinda hajiya Khuburah tace yasa ta dakata tare da juyowa ta dawo har gabanta ta dur'kusa tana cewa.
"gani Mama''.
Wani irin kallo tayi mata cike da tsana tana cewa "a gidan ubanwa kika tsaya sai yanzu kika dawo ana jiranki kizo ki d'ora girki tsabar ba'kin hali shine kika tsaya a wani wuri baki zo akan lokaci ba bayan kinsan Nadiya tana da ulcer bata juri zama da yunwa ba amma kika kama kika zauna a hanya ko, a gidan ubanki kika tsaya"? ta karasa maganar tana kai mata mari, hawaye ne masu zafi suka shiga zubowa Ayrah wato ita da yake bata da wanda zai tambaye ta taci ko bataci ba uwa balle ta samu kulawa a yau banda biscuit da drinks data sha a gurin qawarta Zarah bataci komai ba domin datayi musu kayan breakfast hajiya Khuburah cewa tai ta 6ace mata da gani haka ta tafi school amma ga wacce kawai dan batazo ta d'ora girki da wuri ba har ake zaginta...............
Ba zato taji sun rufeta da duka kamar zasu kashe ta sai tattaka ta suke hajiya Khubura tana zaune a hakimce ta d'ora qafa d'aya kan d'aya sai kad'a kai take tana cewa "kuci uban daya kawota duniya sawa tace ku fasa Mata baki".
A fusace Nadiya dake faman d'irkarta ita da Abidah tace "anya mum wannan da ba dabba za'ai yi bata akai mutum kwata kwata ace yarinya ta zama me dod'add'iya qwaqwalwa duk abinda aka fad'a Mata bazai shiga kunnen taba saikace jaka"?.
Ta'be baki hajiya khubura tai tana cewa "da alama dai jakar ce domin bata sahun mutane a gurina dan naga qwaqwalwar jakuna gareta dukan da kuka lakad'a Mata bai shigeta ba shiyasa ta tsaya kuka kuci gaba da nad'ar 'yar isa sawa tace ku fasa mata baki" hajiya Khubura ta karasa maganar tana hankad'a Ayrah baya tare dasa qafa taka Mata ciki, qara Ayrah tai cike da azaba a take wani wahalallan amai ya fara fito Mata har ta hanci, da sauri hajiya Khubura ta matsa gefe tana sa hannu ta kare hanci da baki wai karta d'auki cuta tace.
"Kan uba mu zakiwa qazanta a parlor gurin zama da hutun mu aiko saikin shanye sa😳".
Kuka Ayrah keye sosai cikin damuwa hannuwanta a bud'e alamar neman yafiyarsu muryarta na rawa tace "dan girman Allah Mama kiyi hakuri zan gyara gurin".
Cikin tsawa hajiya Khubura tace "karki kuskura ki sake kirana mama domin ni ban haifi 'ya asararriya irinki ba kije can qabari ki nemi uwarki Allah ya sauwa'ke na miki kallon 'ya hayyy tabdijan amma baki ma da hankali Wallahi daga yau na sake jin wannan tsinannan bakin naki ya kirani da Mama saina kusan kashe ki a gidan nan kuma kiyi abinda nasaki ki shanye wannan aman" ta fad'a tana kifata a gaban wuri tace.
"Abidah ni ta raina min wayo kuzo kusata ta shanye wannan qazantan data zubar mana".
Tasowa sukai Nadiya ce akan gaba tana zuwa ta d'auke ta mari zatai magana itama taji saukar wani irin firgitaccen mari me tafiya da ji da gani ya sauka a fuska kafin ta wani yunkuri sabo wanda yafi na farko ya sake sauka a daya 'barin a gigice Nadiya ta fasa qara wata ba'kar juwa ta debeta tayi baya timm ta fadi kasan carpet tana fashewa da kuka wanda kafin su farga cikin zafin nama Abidah ma ta samu nata rabon itakam da yake tafi Nadiya raki ihu tai ta zundumawa tana burgima a kan carpet d'in kamar ana yankar jikinta.
Yana tsaye a kansu ransa a mugun'bace idonsa yayi ja kallon yadda jikin Ayrah ke rawa yayi takaici na sake rufeshi kamar ya cire belt din jikinsa ya musu shegen duka yake ji sai kuma ya fasa dukawa yayi yana d'ago Ayrah batare da yace mata komai ba sai mahaifiyarta da yake tunawa irin ri'kon datai masa kamar d'an data haifa idan ya zuba ido akaci gaba da cutar da yarinyar nan bazai ta'ba yafewa kansa ba...............
Katse masa tunani hajiya Khubura tai sakamakon wata ba'kar d'anyar ashar data danna tana cewa "Aiman ka fita idona a cikin gidan nan ina ruwanka da lamarin mu na rantse da Allah bazan yarda bari Alhaji ya fito ya mana iyaka domin wallahi saidai ka koma gidan ku ko kuma ni ya sakeni na bar masa gidansa bazanci gaba da zama kana nuna min rashin tarbiyya irin wacce Fatima ta koya maka ba kasan laifin da tai min kawai zaka dau hukunci a hannunka wato kaiga isashshe d'an isassu me qanwa ko''?..
(Fatima mahaifiyar Ayrah ce ta rasu shekaru uku da suka wuce itace ta reni Aiman shi d'an qanin Daddyn Ayrah ne tun daga yaye ya'ki gidansu yake zaune a gurin Fatima komai nasa kuma tamkar uwa haka ta daukeshi sannan ta raineeshi a matsayin nata).
Wani irin razanannan kallo me firgitarwa Aiman yayi mata wanda yasa cikin shakka ta soma matsawa baya baya tana cewa "wallhi bari kaji tunda juninka fitsara zan gwada maka Nima ba kanwar lasa bace zanje gidan naku zan hadaka da wadanda suka isa dakai suyi min maganinka Ina daidai dakai d'an marar kunya kawai".
Nunata Aiman yayi da yatsa a fusace yace "karki sake zagina kin gane"?.
Itama a fusace tace ''na zaga ubanka ya buge uwarka tsinanne la'ananne ni zakaiwa rashin da'a? To bari kaji ko Zainab uwar data haifeka bata isa fad'i in fad'a Dani ba balle wani banza kai data haif.............
Bata karasa ba ya wanketa da mari ihu ta zunduma daidai Daddy ya fito baiga sanda yai Marin ba ihunta kawai yaji gasu Abidah da Nadiya har lokacin suma suna kukan zafin da fuskokinsu ke musu da sauri ya karaso yana kallon Aiman yace.
"Subahanallahi me yake faruwa Aiman ya naga haka kukan me suke"?.
Tun kafin Aiman yai magana hajiya Khubura dake ri'ke da kunci cike da takaici tace "au Alhaji shi zaka tambaya bayan wulakanci da cin mutumcin dayai min marina fa yayi".
"Mari dai"?.
Daddy ya tambaya cikin mamaki yana kallon ta da alamar rashin yarda akan abinda ta fad'a, haushi ne ya rufe hajiya Khubura a fusace tace "eh mari yanzun nan ya mareni akan nayi masa magana ya mari Abidah da Nadiya".
Kallon Aiman Daddy yayi yana cewa "meyasa ka maresu Aiman me sukai maka"?.
"Daddy Ayrah suka saka a gaba suna dukanta kamar zasu hallaka ta harda amai kalli inda tai kuma tsabar rashin imani wai saita shanye, wacce irin rayuwa ce wannan suzo suna qarqashin inuwar mahaifin ta suna cutar da ita komai itace take musu hakan bai ishesu ba sai suna dukanta to wallahi bazan yi lamani ba" ya karasa maganar yana hararar su Nadiya dake gefe suna jan ajiyar zuciya.
Shiru Daddy yai ya tsume yana kallon Ayrah jin a kanta ne komai ya faru kuma Aiman harda marar masa mata nunata yayi da yatsa yana cewa "wato ke kin zama shed'aniya ko? Kullum sai an samu sa6ani a gidan nan a kanki kin hana zaman lafiya to bari kiji idan har baki gyara ba sai na dauki mummunan mataki a kanki zan bayar dake".
Daddy na rufe baki Aiman yace "Daddy ba laifin Ayrah ga babbar me lefi nan Hajiya Khubura itace ta gur6ata zaman gidan nan ba kowa ba da a lokacin da Umma tana raye ai ba haka muke zaune ba bamusan rayuwar 'kunci ba sai sanadin shigowarsu cikin rayuwarmu dan haka Ayrah tana gidan insha Allahu babu inda wadannan agololin zasu sa taje".
Mi'kewa Hajiya Khubura tai tana cewa "idan Kaine ka haifeta saika hana ya sadakar da ita me gida yace bazata zauna masa a gida ba kaga ko kai dan karere baka isa ka hana ba dole ta hada kaya ta kama gabanta".
"Wallahi babu inda Ayrah zataje tana gidan nan tunda gidan mahaifin tane saidai su koma gidan ubansu".
A masife Hajiya Khubura tace "kaine zaka koma gidan ubanka tunda ai kaima zilama ce ta dawo dakai nan d'in ai kasan yafi mahaifin ka kud'i idan ba tsoro ba ka koma".
"Look malam don't disturbing me ba dake nake ba da mahaifina nake dan haka ki rufa min baki kin gane"?.
"Bazan rufe bakin ba kad'au mataki d'an me ido a tsakar ka mara mutunci kawai".
"Na fada miki da ki daina zagina wallahi tallahi daga Rana irin tayau idan kika kuskura tsautsayi yasa kika sake zagina, humm na rantse da Allah saina 6allaki a gidan nan tunda ke ba uwa ta gari bace".
Zainab ce ba uwa ta gari ba amma dai bani ba idan ka fasa 6allani kai ba d'an halak ban............
Bata karasa ba tayi shiru tana matsawa baya da sauri harta kusa fad'uwa qasa sakamakon hannu daya d'aga zai sake kifeta da mari a karo na biyu maganar Daddy ce ta dakatar dashi daga yunkurin sa.
"A'a Aiman bari kada ka sake marinta".
Huci me zafi Aiman ya fitar yana sauke hannunsa qasa tare da doka Mata wata uwar harara yaja tsuka cike da fusata ya fice daga parlon ran hajiya Khubura na quna ganin yadda yaci Mata fuska a gaban 'ya'yanta amma Daddy baice masa komai ba bai nuna masa 6acin rai ba yasa taja qaqqarfan tsaki tana kallon su Nadiya tace.
"Ku tashi kuje kuyi wanka muje eateries muci abinci acan tunda wannan d'an iskan yaron ya gama 6ata min rai yau bazai bari tayi mana girki a gidan nan ba idan tayi ma zai iya lalatashi ko yasaka mana guba a ciki muci mu mutu ba damuwar sa bace dan naga d'anye ne".
Mi'kewa su Abidah sukai suna shiga part d'in su hajiya Khubura zata bi bayansu saida ta bangaje Ayrah harta fadi ta baya ta take Mata yatsun hannu tana cewa "ubanki kike kallo a jikina mayya kika zuba min wandannan tsinannun idanuwan naki aikin banza uban me za'ai da auren mutum me d'a a hakan ma d'an kishiya" ta qasara maganar tana kallon Daddy daya d'ago suka had'a ido kafin fuuu ta bud'e kofa ta fice shiru parlon yayi na wani lokaci Daddy ya zubawa Ayrah ido so yake yayi tunani akan wani abu game da ita ya kasa tuna komai yasan Ayrah 'yarsa ce kuma hakan bai 6ace masa ba amma a ransa yana jin wata iriyar ba'kar qiyayyar ta ko ganinta bai so wanda ada yasan ba haka bane to meya sameshi ne, qara zuba mata ido yayi tana dur'kushe a gurin da hajiya Khubura ta kifata kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya nufi hanyar fita saboda an kusa kiran sallar magriba Ayrah tana kallon Daddy ya bud'e kofa ya fita wani irin zazzafan hawaye ne me d'aci yake fita daga idanuwanta ta sani mahaifin ta yana matukar sonta kafin rasuwar mahaifiyarta da kuma bayan rasuwarta yana tausaya mata dalilin haka yasa ya'ki aure da farko saboda yana tsoron irin matar da zai yayowa kansa irin muguwar matar dazata shiga tsakanin sa da 'yar shekara biyu da rasuwar mahaifiyar Ayrah ya kasa yin aure yace saiya samu mace mai d'a wacce tasan dad'in d'a zata ri'ke masa Ayrah tsananin ta da Allah ta bata gata ta yaye Mata kewar uwa data rasa amma baiyi dace ba ya auri hajiya Khubura Mai 'ya'ya uku domin tana d'a saurayi yana can qasar rasha (Russia) yana karatu sunan sa Khalil bai ta'ba zuwa gida ba tunda tai sabon aure shekara guda bayan rasuwar mahaifinsu.
Mi'kewa Ayrah tai jikinta yana Mata mugun ciwo sakamakon dukan dasu Nadiya sukai mata har jan qafa take ta shiga part d'in mahaifiyar ta inda yanzu a ciki take rayuwa da komai nata tun bayan auren hajiya Khubura da Daddy yai tamai asiri tare da kad'ar masa hankali akan ayrah tun daga lokacin komai ya fara sauyawa rayuwar qasqanci ta sameta kamar ba gidan mahaifin taba ko yar aiki bazata fad'a mata bautuwa a gidan ba hatta bedroom d'inta su Abidah sun koreta sune suke kwana dole sai part d'in mahaifiyar ta takoma.
MRS ÃL'ÅMÉÉÑ ÁHMÃD CË.
Tnks for your supports🔥.
Naja'at Musa Abubakar
Fatima Musa Abubakar
Salim Musa Abubakar
Aisha Musa Abubakar
Abubakar Musa Abubakar
Everything about you is so good but one thing is wrong that you are not mind.
We will meet again.
TYPING📲 Mon, Nov,11/24 11:06AM YUSRAH MUSA ABUBAKAR💋🤟.
👑ROYALTY👑
ÀÑÑÙRÌ WRITER'S ASSOCIATION 💫
Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta.
2~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Mujahidina.
@YUSRAHMS CE
Page 03 & 04
👑PALACE👑
Yau tun bayan sallar asuba baby batai marmarin sake kwanciya ba wanka tai ta shirya tun lokacin school baiyi ba bata tsaya zancen breakfast ba kawai ta dauki Jakarta ta fito a part d'insu ta shiga part d'in Momy bata lura da Ahmad ba sai da taji yana waya da sauri ta juya ganin irin kallon da yake aiko Mata yasa kawai da tacewa prince Hamid good morning dan karta tsaya ya gama waya ma ya qaqalo Mata wani abun lefin yasa ta juya zata fita kai Ahmad ya jinjina yana mikewa ya fita ta dayar kofar batai zato ba sai ganinsa tai a gabanta da sauri tayo baya tana zaro ido me kuma tai masa zai tare ta...........
Katse Mata tunanin yai ta hanyar jawota yana kallon prince Hamid daya biyo bayan Babyn yaga me Ahmad d'in zaiyi mata domin yana kallon lokacin daya jinjina kai shiyasa ma ya taso saboda karya cuceta sakar masa hararar gargadin ya sake ta yayi amma kamar Ahmad bai gani ba ya d'auke kai yana dawo da kallonsa kan Baby yace.
"Which rubbish is this"?.
Da mamaki tace "me nayi yaya"?.
"Oh tambaya na kike¿ Do you want to know why? Na miki tambaya kema kina tambaya na?