x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 1 - ROYALTY YAN SARAUTA

  • 1 words
  • 3000 words
  • Out of 85109 words

Category: Love Stories

Views 1662

20 Jul 2025
Start ads
After Image Ads

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

TYPING 📲 FRI, 18/23 08:️20AM YUSRAH MUSA ABUBUKAR ✍️.

👑 ROYALTY 👑

WHATSAPP NO:234 8160983083.
I'm back Na dawo is my time whow missing me ku fito mu kwashi nishad'i yadda ya kamata.


IN THE NAME OF ALLAH THE MOST BENEFITS AND THE MOST MERCIFUL ALLAH SWT THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPTS ONLY WHAT IS PURE ALLAH THE MOST HIGH DOES NOT SLEEP WE LOV OUR NABEE WE LIKE HIM NO SUCCESS WITHOUT HIM HE'S THE MIRROR OF OUR LIFE HE HAVE NO LIMIT, PEACE BE UPON HIM AMEEN.


DEDUCTED TO
My Late father😭 }{MUSA ABUBAKAR IBRAHEEM}{ ubangiji Allah ya gafarta maka Allah yakai haske cikin 'kabarinka Allah yayi maka rahma.

Ibrahim Musa Abubakar
Aishat (Ummi) Musa Abubakar
Abdullah (Adali) Musa Abubakar.
😭Ubangiji Allah ya ji'kanku da rahma Allah yakai haske 'kaburburan ku ina ro'kon Allah yasa aljannah ce makomar ku Amin.

Yusrah Musa Abubakar
Saleem Musa Abubakar
Naja'at Musa Abubakar
Aishat Musa Abubakar
Fatima Musa Abubakar
Abubakar Musa Abubakar
😥Mu kuma ubangiji Allah ya bamu ha'kurin rashin mahaifin mu da 'yan uwan mu Allah yasa idan tamu tazo mu cika da imani alfarmar sayyidina muhammadur rasulullah SAW Amin.


ÀÑÑÙRÌ WRITER'S ÃSSÕÇÌÅTÍÔÑ 💫 HOME OF HOSPITALITY AND HARMONY gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai 'ya'yan ta.

STORY WRITTEN ND EDITING
Yusrah Musa Abubakar
Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë.

🕋🕌🕋
It's Friday don't forget to recite suratul al-khaf may Allah open the door of success 4 all of u Muslims in the world amiinn.

Yusrah Musa Abubakar (YUSEEN AL-AMEEN CE
📝📚✍️WRITER👇
YARIMA ABDUL-MALEEK
SAFREEYYAH
'DAN MILIONAIRE
HUSNAH KO BADIYAT
ME KAMAR SARKI
MINISTER ASHRAF

ANDNOW...........📚✍️
👑ROYALTY👑
I wish to thank Allah swt for the opportunity he gave me in putting across another book,🙏 royalty is a book that entertains educates and informs,, alhamdulillah ala kullu halin may the blessings and the peace of Allah swt be upon to our prophet NABI SAW no success without him he's the mirror of our life he's the answer to every question he've no limits ya rasulullah.

1️⃣Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil mursalina.

@YUSRAHMS CE
NO: 01 to 02
Tsaye wani zu'keken saurayi yake fari tarr dashi a cikin wani dan'kareran tsararren parlor wanda ya wadatu da kayayyaki na alfarma irin na sarauta da wata had'add'iyar budurwa kyakkyawa dur'kushe a gabansa tana kallonsa cikin tashin hankali ta toshe bakinta da hannu dan kada kukan da take ya fito fili sai hawaye dake ta faman ambaliya a fuskarta ransa a mugun 'bace cikin tsawa mai firgitarwa ga mai sauraron sa yace.

"I said stop look me like that what are you doing here"?.

Jikinta ne yadau rawar tsoro da tashin hankali ga zafin da bayan ta ke mata dalilin dukan dayai mata da belt.

"What am I supposed to do? me zanyi Baby ba dake nake magana ba zaki fad'a min ko sai jikin ki yayi tsami, uban wa yasa ki d'aga min waya har ki samu damar magana na saki ne"?.

Kai kawai take iya girgizawa ta kasa magana tsabar tsananin tsoro da irin bacin ran da take hangowa a cikin kyawawan idanuwansa.

"Baki da baki"? ya fada yana sake sauke mata wannan gardiyar belt d'in irin wacce sojoji ke d'amara da ita a bayanta da karfi dan a duniya ba abinda ya tsana yake saurin sa ya fusata kamar ya maka magana ka bashi amsa daka ranar kuwa da saika wuni ka kwana kan yana ciwo saboda azabar dazai d'andana masa wacce bazaka sake marmarin masa laifi ba shiyasa yanzu hankalinta ya tashi zuciyarta tahau bugawa da 'karfi.

"Nace baki da baki kin kurmance ne baki gane yaren da nai miki magana dashi baa"? Ya karasa maganar a fusace yana sake zuba mata belt d'in a gadon bayanta.

Zatai ihu ya daka mata tsawa wacce yasa ta sake susucewa a hargitse ta mi'ke zata gudu ya dam'ko ta tare da murde mata hannu da 'karfin da yasan zataji ciwo ihu ta kurma da karfi itama tana faduwa qasa cikin azaba ta fashe da kuka ta rasa inda zata sa kanta taji sassauci ko'ina rad'ad'i yake a jikinta tsuka ya ja zuciyarsa na qara ingiza shi tana tado masa da sabon fushi a kanta kallo d'aya ya mata yana tsallake ta yabar parlon ya koma bedroom yana cewa cikin kamammiyar murya mai dad'in sauraro.

"Idan jikin ki ya fad'a miki yau gobe ko ance ki d'aga min waya baza ki d'aga ba yarinya karama sai rashin ji" haka ya shige part dinsa ya barta kwance tana juyi a kasan carpet.

Kai prince Hamid dake zaune ya girgiza yana mi'kewa yaje inda take ya d'agota dan bashi da ikon hana Ahmad ya hukunta ta kuma da yasan abun zaiyi zafi har haka daya hanata d'aga wayar ba tare da yace mata 'kala ba kawai data mi'ke tsaye ya saketa yabar parlon yabi bayan Ahmad yaje ya masa magana a kanta yana shigewa ta share hawaye da'kyar ta d'aga qafarta ta fara takawa a hankali cikin d'ingishi ta fita tana shiga part dinsu kallo d'aya Mami dake kishingid'e tai mata tana d'auke kai batace komai ba ta mayar da hankalin ta kan TV kamar bataga a yadda ta shigo ba saidai tasan duk fad'in gidan babu wanda zai mata haka bayan Ahmad shiyasa ma bata tanka ba itama babyn batai magana ta wuce tana shiga bedroom ganin babu kowa kila Aunty Khairat ta fita yasa tana zuwa ta fad'a kan gado ta kwanta tana cigaba da kukanta tunda tasan babu mai ce mata tayi shiru balle a lallasheta dama Abbansu yana nan ne ko Abban su Ahmad d'in su kad'ai ne zasu lallasheta zuwa 'bangaren Sultan Sharfaddeen (Mai Martaba Sultan Ameer) kakansu a yanzu zai bata wuya kan taje domin tafiyar da nisa kamar ba gida d'aya ba yake da nisa dasu kafin kaje fadarsa haka suke da rata sakamakon gidan sarautar nada girma na gaske ga kyau da tsari abun burgewa.

Sau'ke ajiyar zuciya mai zafi tai tana mi'kewa taje jikin mirror ta fara kallon kanta a tabkeken mudubin ganin yadda yai jaa duk inda ya daketa ya shata kamar jini zai fito yai tsartuwa domin fara ce tar-tar kuma kaf yaran gidan babu wanda ya d'auko fuska irinta Ahmad yake kama dashi sai ita ko Khairat da suke uwa d'aya uba d'aya dashi basa kama dashi kamar yadda ita suke kama amma ya rasa wanda zai ri'ka zalunta yana hukuntawa sai ita¿ d'an tsaki taja kamar kuma an tsikare ta a firgice ta juya tana kallon qofa tsoro 'karara bayyana a kyakkyawar fuskarta gani take kamar inta juyo zata hada ido da Ahmad ko zai fahimci wannan tsakin dashi take ganin dai ita kad'ai ce har lokacin babu kowa yasa ta sau'ke ajiyar zuciya tana tunanin wannan wacce irin masifa ce mutum baya guri ma amma tsoron sa yasa takejin kamar yana gun juyawa tai tana shiga toilet ta hada ruwa mai zafi tana gasa jikinta sai yamutsa fuska take tsabar azabar da takeji amma haka ta daure ta d'umame jikinta dakyau kamar wata mai jego ko'ina kuwa jikinta sake d'aukar rad'ad'i yai har saida taji dama batai hakan ba neman maganin zugi take a cikin drawer dake jikin bed din domin ranar taga Aunty Khairat ta shigo dashi tasha itama daya bugeta akan 'karamin abu dabai taka kara ya karya ba iya dubenta bata ganshi ba ta ha'kura gashi jikin nata ya dameta tayi tunanin sa kaya taje gurin prince Hamid ta kar'bo amma saboda tasan zata iya had'uwa da prince Ahmad yasa ta ha'kura kawai ta kwanta cikin dauriya tana cije pink lips d'inta bata sake marmarin fitowa ba balle tabi takan wani abinci har saida akai sallar magriba da isha sannan ta fita parlor inda Mami take bayan ta gaishe da ita ta kwanta ajan daya daga cikin d'uma-d'uman chusion d'in dake zagaye da falon kawai ta lumshe idanuwanta kamar maijin barci ta.

Kallonta Mami tai na 'yan sakonni tana girgiza kai kafin ta mayar da hankalin ta kan TV tana cewa.

"Baby tashi daga kwanciyar nan ki kaiwa yayan ku abinci yanzu naga takwas tayi kar dare yaja baici ba kinsan indai goma tayi ya ha'kura komai son da yakewa abincin zai barshi tashi maza kije a had'a miki ki kai masa".

Tashi zaune tai bayan ta gama jin me Mamin tace idonta ya cika da hawaye jikinta ya dau rawar tsoro lokaci guda ta fara kuka harda yarfa hannu taya zataje gunsa a yau aiko gobe bata fatan su had'u dashi balle tun a yau da komai bai lafa ba.

Wani kallo Mami tai mata tana cewa "meye haka? wannan shashancin kuma fa kukan na mene"?.


Cikin muryar kuka take girgiza kai tana kallon kofar shigowa gani take kamar shine zai shigo ko yana jinta tace "Allah Mami tsoro nake ji bazan iya zuwa gurinsa ba yad'au fushi dani sosai dan Allah ki taimaka min ki aika Sultan".

'Dangowa Mami tai tana qare mata kallo da karantar yanayi na rud'u da rawar da jikinta keyi tace "na aika Sultan Saboda da me?
Bayan gaki"?.

Goge hawayen fuskarta tai tana cewa "Mami idan naje zai karya min 'kafa wallahi nasan ba ha'kura yai ba".

"Oh ya karya miki qafa? A'a kin manta ba 'kafa zai karya miki ba kashe ki zaiyi,, kinsan Allah baby ki kiyaye ni zaki tashi ki kai masa kibar wannan shirmen 'bata lokacin ko saina bige ki a haka ma ba tsira kakai ba maybe kiyi latti wajen kai masa kinga kin 'bata biyu baki wanke biyar ba kin 'bata goma kinsan kina jin tsoron nasa kikai masa laifi"?.

Tana shashshe'ka tace "Mami ba laifi nai masa ba kawai dan an...............

Katseta Mami tai da cewa "na tambaye ki mene abinda ya faru tsakanin kune? Ta tashi ki kaima abinci baby kafin ki jawa kanki wata wahalar kinsan ko a rami kika 'boya saiya 'kwa'kulo ki da ace yaga damar qara miki wani dukan ina zaune a parlon nan zaizo ya wuce ya nad'eki ba ruwansa to tunda kinsan haka ne dan me zaki zauna kina kwane-kwane just ki tashi kikai masa idan kin manta bari na tuna miki kina qara wasting time dinki wajen kai masa kinga idan kika d'ada kuskure ya jibgeki acan gobe saiki hanyar ma'kabarta ko".

Kukan tane ya karu sosai ta d'ora hannu aka dan tasan ita kam tata tazo karshe da'kyar ta mi'ke kamar mara lafiya ta soma takawa ta nufi hanyar fita dan dakatawa tai tana sake juyowa ganin idon Mami a kanta yasa cikin muryar tausayi tace.

"Dan Allah Mami kiyi hakuri bazan iya zuwa inda yake b..............

Bata karasa ba a tsawace Mami ta katseta "get of my sight baby kafin na fusata".

Fita tai tana kuka had'uwa sukai da Sultan zai shiga part d'insu ganinta haka yasa yace.

"Aunty baby wai har yanzu ke da yayan ne mai kikai masa kuma yau"?.

Share hawaye tai tana kallon sa bata bashi amsar tambayar saba sai cewa tai.

"Sultan ka taimake ni ka kaiwa yaya abinci idan naje saiya kusan kashe ni yau nasan ba hakura yai ba".

Zaro ido Sultan yai wanda kana gani alamar tsoro ne 'karara ya bayyana a fuskar sa kallon gefe da gefen part d'insu yin 'kasa da murya yace.

"Wallahi bazan iya zuwa gurin yaya yanxu yana cikin fushi ba saboda kwanan baya da Aunty Khairat tai masa laifi yana bedroom Mami ta aikeni nakai masa healthy spinach mix dayace a masa ina shiga wata tsawa daya daka min bansan lokacin da nayo tsalle na fito a d'akin ba sai gani kaina nai a falo da gudu ta baro part da'kyar nai barci a ranar saboda gani nake kamar biyoni zaiyi".

Dammm baby ta sake jin gabanta ya fad'i muryar ta na rawa tace "Sultan nasan baka so ya kasheni dan Allah ka kaima masa yau d'in ma aiba kaine kai masa laifin ba nice iyaci yai maka tsawar ka ceci rayuwa ta".

Kai Sultan ya girgiza yana cewa "nima abinda kike gudu shi nakeyi wallahi Aunty baby bazan iya zuwa gurinsa ba da zan iya danaje saboda ke amma nima tsoro nake ji dan Allah kiyi ha'kuri babu abinda zai miki" kafin ta sake magana da sauri kamar walkiya Sultan yayi wuf ya shiga part din Mami.

'Dora hannu tai aka zuciyar ta na bugawa da karfin gaske ta nufi hanyar kitchen tana goge hawaye ta tarar masu aikin suna ciki sanar musu tai su had'a mata abincin ya Ahmad zata kai masa nan danan kuwa suka hada mata komai akan tray ta dauko da niyyar kai masa jikinta na rawa tana zuwa main 'katon parlon daya raba tsakanin part d'in Mami da part Momy da kuma part d'in su Ahmad d'in anan cikin sa'a taga Momyn tsaye tare da prince Hamid da alama magana suke yana nuna mata wani abu a paper dake hannunsa.

Wata irin 'kakkafar ajiyar zuciya ta sau'ke tana godewa Allah da sauri ta karasa gurin ta tana dur'kusawa a gabanta ta fashe da kuka mai ban tausayi tana addu'ar Allah yasa daga nan Momyn ta hana ta karasawa part d'in.

Kallonta Momy tai da dsn mamaki ita batama lura da itaba saida taji sautin kukants da sauri ta d'agota tana cewa "Subahanallahi baby lafiya me akai miki kike kuka? ko keda Mami ne? fad'a min waye ya ta'ba min ke a gidan nan"? Momy tai maganar tana kallon yadda shacin belt ta fita a bayan hannunta nan take ta gane da Ahmad ne ko ba'a fad'a mata.

Cikin kukan tsoro baby take kallon kofar part dinsa dake kulle tana fatan Allah yasa baya nan da'kyar ta d'aga hannunta dake rawa tana nuna wa Mommy cikin shashshe'ka tace.

"Yaya ne".

"Me yai miki? ko dukan ki yai"?.

Kai ta girgiza cikin tsoron kada tace eh Momy ta masa fad'a ya sake d'aukar zafi da ita tace "a'a ba duka na yai ba abinci Mami tace nakai masa yaya Hamid qarfe nawa yanxu"?.

Kallonta prince Hamid yai cikin tausayawa yasan tsoro take ko lokacin cin abincinsa ya fita a zahirin gaskiya kuwa Ahmad yana bedroom maybe ma yau bazai ciba duba watch d'in dake d'aure a hannunsa yai yaga tara da minti arba'in batare daya d'ago ba yace "da sauran lokaci kije ki kai masa".

Shiru tai ta kasa koda motsi tana jiran jin me Momy zata ce kallonta Momy tai tana cewa.

"Baby ko akan haka kike kuka"?.

Da sauri ta girgiza kai "A'a Mommy kaina ne yake ciwo" ta karasa maganar tana kokarin boye tsoron ta dan kar Momyn tayi tunanin wani abu.

"Ok ayya baby Allah ya sauwa'ke kiyi hakuri ki daina kukan kada ciwon ya qaru je ki kai masa idan kin dawo kizo part dina ki amshi magani kinji".

Da'kyar tace "to" tare da daukar turen tai gaba tana shiga part d'in ta wuce dinning table ta aje jin shiru yasa cikin sand'a tana ajiyewa zata fita sai kuma ta tuna ba ai masa haka Khairat ta ta'ba kawo wa bata sanar masa ba yaje har part d'insu ya jawota yasa ta cinye dukkan abincin tana kuka kuma ya faffalla mata mari takai kusan sati biyu a kwance bata da lafiya.

'Dauke numfashi tai tuna hakan da tai yasa dole ta tura kofar bedroom dinsa a hankali tana le'kawa can ta hango shi a tsakiyar 'katon gadon shi yana lullu'be da dukkan alamu bacci yake.

A hankali ta sauke wani irin sansanyan numfashi taja kofar ta mayar ta rufe juyawar da zatai
End Ads