x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 50 - KASUWANCINA

  • 147001 words
  • 150000 words
  • Out of 176000 words

Category: Romance Story +18

Views 178

30 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
bakin ciki,Hajja kuwa Murna takeyi sun auri mataye na gari,da Daddy yazo gaisheta harda gori ta masa cewar saura kai tsohon gwauro an kasa aure,ka daure ka ajiye mata ko ka
Samu nutsuwa ga yan uwanka su Uku sun dallo mata matasa., Daddy yace na kusa ai Aayan ne yake bani matsala shi sai wacce yake so,wai cewa yayi na auri Maman Mufeeda,nan take Hajja ta fashe da kuka su Mufeeda gaba daya sun mallake mata zuri'a yanzu har uwar ma so ake Danta ya aura kuma abin haushin duk masu kudi,masu halin kirkin dangin Mufeeda suke aurewa takaici ya kama Hajja tace yanzu har Uwar tasu gososo da ita itama aure take so kuma ta rasa wanda zata aura sai kai,Uwa gososo da ita katuwar banza tana Tafiya kamar wahainiya da Duwawu kamar tukubar tsire tana mirginasu sai shegen iyayi da kisisina duk tabi ta koyawa yaranta suna ta mallake Jama'a nan Hajja ta dinga masifa,Daddy yace bafa aurarta zanyi ba Aayan ne yake so na aura,ai abinda yace shi kakeyi tunda yace ka aureta nasan sai ka aura,da kamar ba kai ka haifeshi ba Sai abinda yace sai yanda yayi da kai tirr da halinka.

Meenat kuwa bayan sun karya tana saman Sofa Ameer na Bed Amma hankalin kowa yana kan dan uwansa,tana tunanin daren jiya yanda Ameer yasa taji mugun Dadin da baza ta manta ba shima tunanin da yake kenan, kallonsa tayi shima haka yace dawo nan Muyii bacci,Meenat anji dadi jiya batayi musu ba ta koma jikinsa ta kwanta,yana shafa gashinta me santsi da tsayi a hankali ya rada mata ko mu kara sati daya a Hotel kinga sai muyi 2wks ko?Meenat ana shagwaba tace ae mu kara yanda kaga ya dace,Nan ma basu bata lokaci ba Ameer ya fara rabata da kayan jikinta.














AszmaBaffa
[2/14, 11:57 PM] Asmabaffa: πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–
πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–

KASUWANCI NA







121-125






Official






By
AsmaBaffa








AsmaBaffa wannan page nawa ne na kaina sabo da dadin Typing😍.












Ameer ya fara rabata da kayan jikinta kenan Meenat ta fara karbar Dadinta zam zam firgigit ta dawo hayyacinta ta tuna basu fa da aure Allah ya tsinewa me yin haka,ita bata damu da wani dan Adam ba wai ko zai mata gori nan gaba kawai sabo da Allah ta tuna ba kyau fa,nan take Meenat ta maida kayanta tana Hawaye ta tattara nata ya nata,Ameer yana tambaya lfy?ta bari da yamma sai su koma Kano,Meenat dama ta Kware wajen iya masifa nan ta hayayyako masa da masifa tana Galla masa harara,zaka lalatani dama haka kake wlh bazan aureka ba kaji na rantse na fada ma bazan taba aurenka ba har abada,Hannu Ameer yasa tare da riko kafadarta da sauri ta fisge kanta tace matsa Malam bani ba kai anyi min tarbiyya ta zaka batata dama Ku gidanku baku gaji tarbiyya ba,maganar nan da ta fada tayiwa Ameer ciwo matuka ko ba komai ai tayi masa kara amma ba komai shi ya jawo daya kula yarinya haka amma ya zaiyi wlh yana sonta da gaske sosai ma,shanye bacin ransa yayi tare da cewa kiyi hakuri da nasan abinda nayi zai bata miki rai bazan taba ko rike miki yatsa ba,kiyi hakuri karki ce bazaki aureni ba,wlh ina Sonki kamar raina,da farko ban gane hakan ba sai da za ayi min aure na gane ke nake so Meenat,Da ace ba ke bace bazan bari ma na biyoki nan ba,karki manta ni ba yaro bane amma na biye miki muka zo nan,dan Allah ki aureni Ameer ya furta tare da dire gwiwoyinsa biyu a kasa yana rokon Meenat kamar almajiri,sai hakuri yake bata bayan ita ma ai da laifinta amma Still hakuri yake bata.

Meenat idonta a rufe kamar bata San Ameer ba bazan aureka ba tunda dan Iska ne kai wa ya sani ma ko gado kayi ,Meenat da kuruciya ma magana da dama idan tazo mata gani take dai dai ce, wannan maganar ta Meenat itace ta batawa Ameer rai ai ko ba komai ta daraja iyayensa wato a wajen iyayensa ya gaji iskancin,idonsa ne ya canja yayi jajir jikinsa yana rawa sabo da bacin rai,shi da ba Meenat bace ta fada masa haka ba da sauki,kuma duk da haka bai ji haushinta sosai ba amma ai iyaye iyaye ne ko me suke yi,a fusace ya Mike ya shirya tsab ya hada nasa ya nasa ba wanda ke kula wani,da sauri ya ajiye mata Key din room din ya ja akwatinsa karama yayi waje,a nan ta zauna gefen Bed tayi tagumi tana tuna irin maganganun da ta yabawa Ameer gaskiya bata kyauta ba duk irin mutunci da abinda yake musu musamman Ita Meenat ma komai shi yake mata,ta dade a haka amma girman kai yasa tace bai isa na bashi hakuri ba wlh ta Mike ta bar Bedroom din itama da kayanta,Ameer yana jiran Taxi itama haka gasu nan a titi kowa a gefensa kamar ba wanda yasan wani,Meenat sai kallonsa takeyi a ranta tana gaskiya Ameer yana da kyau carkwadi,Ya tsaida Taxi dinsa sai tayi sauri ta rigashi shigewa ciki,ya jawota waje yana fushi ba tare da yace komai ba,ta makale ta rike kujerar mota kam,ya fisgota amma taki jawowa dake hannu daya yasa,Driver na taxi yace Subhanallah Mallam bafa a garin arna muke ba,baka sani ba ko tana da aure kawai kazo kana rike mace kuma baza kayi mata magana ta fita ba sai ka dakumi mace ku fara kokawa,Driver bai gama magana ba yaga Meenat itama tana ta kokawar kwacewa a hannun Ameer ba ruwanta da wannan namiji ne,kokawa suka fara driver yana kunga Innalillahi kai..kai...ku bari mana...ke macece ki kyaleshi,kai malam kaci girma mana ka hakura,ba wanda ya kula me taxi a cikinsu Ameer yasa hannu da karfi yayo waje da Meenat har tana bigewa kadan a kanta,Ta Dafe wajen ta jawo rigar Ameer tace ai na rigaka tsaida me Taxi din zaka raina min hankali ka wani ce kai ka tsayar,yayi yayi ta sake masa riga taki,me taxi yana baiwar Allah ke kuwa kiyi hakuri mana ki sakeshi kina mace,Meenat tace ai wlh sai dai a kasheni,Ameer yace ina zuwa me taxi ya juyo yana kallonta yace sake ni,Meenat sai taji tsoro ta sakeshi taga ba fuskar wasa,amma sai ta kuma fadawa motar da gudu,Ameer ya dakkota kamar jaririya kowa yana kallo yayi tafiya me nisa da ita sannan ya ajiyeta ya dawo motar da sauri ya shiga ya kulle yasa lock,sai ta glass take kallonsa yana kallonta yace Driver muje Airport,Meenat ma da sauri ta tare taxi tace bi bayan waccen motar karka bari su tsere mana,haka suke tafiya suna bayan su Ameer,Sai da Ameer yazo airport abinsa yana fitowa yaga Meenat itama da sauri tace wlh nima sai ka hau dani jirgin ai ta dalilinka nazo garin,bai kulata ba yanda ya siya ticket haka Meenat ma tayi har suka shiga jirgi,Nan ma tace kujerar Ameer ce tata sukayi ta ture ture ana kallonsu,mintuna suka iso Kano suna zuwa Meenat ta shiga Taxi Ameer ya shige motarsa Driver yazo daukansa Direct gida ya wuce,itama Meenat gidana ta taho sabo da tasan bata isa taje wajen Ammah ba me zata mata gwara ma ni Mufeeda na rufa mata asiri,Ameer naga ya shugo a fusace yace Anty na dawo ina yini?Harara na aika masa na hade rai nace yanzu abinda kayi ka kyauta kenan Ameer?am so sorry Anty dan Allah ki bawa Yaya hakuri wlh bazan sake ba,nan Ameer ya dinga bani hakuri Aayan yana jinsa bai San yana gidan ba daya palon,Nace Yana wancen palon kaje ka bashi hakuri,sai dai ki rakani dan Allah Anty,nace muje to mun fara tafiya sai ga Meenat ta shugo ita dama bata San ma za a mata aure ba kawai Hakuri ta fara bani wai na roki Ammah a yafe mata barayi ne suka sace ta da kyar ta gudu daga gidan yan Mafiya,Nace wannan kuma ke ya shafa ke da Ammah kuma ki tafi gidanku nan gidan mijina nane Allah bazan tafi ba cewar Meenat,Ameer nasa a gaba yana rabe rabe muka shiga Aayan dama yana jin komai da muke cewa haka dai kawai Meenat take gani kamar a Tv ana film.

Ameer ya fara bada hakuri yana kasa da kai,Aayan yace kanka kayiwa Ameer ba ni ba Amarya tuni tayi aurenta sai ka zuba ruwa a kasa ka Sha ka nemi wacce kake so na aura maka,ko Kunya Ameer yace Allah yanzu tayi aure?,ta auri wani?,kai amma Alhmdllh naji dadi dama ina da wacce nake so Yaya,Aayan kawai Murmushi yayi yace jeka ka bawa Abba hakuri,Ameer haka yaje wurin Daddy ma ya bashi hakuri Daddy yace ba damuwa,firgit na farka tsakiyar dare daga Dogon Mafarki na Amma sai bacci ya kwashe ni again.

Meenat tunda ta dawo naki kulata ko kallonta bana yi,haka ta tafi wurin Aayan shima tace yan Mafiya ne suka saceta,Aayan yace Allah sarki alhmdllh Allah ya auna mana arziki da kika kubuta,Meenat tace wlh kam kai kaga yara manya da tsofaffi,baka Ga wani tsoho ba abin tausayi suka yi masa aski tare da yankashi gunduwa gunduwa,Aayan yace sannu kunga tashin hankali,Meenat tace dan Allah ka bawa sis hakuri fushi takeyi dani kuma ba laifi na bane Ammah fada zata min idan Mufee bata goya min bayana ba,Aayan yace ke da yan Mafiya suka kama ta ya za ayi miki fada.

9pm na dare na shiga Bedroom din Meenat tana zaune ta zuba tagumi tana tunanin Ammah me zata yi mata,ga Ameer da sukayi fada yaki kulata shine damuwarta,a hankali na bigi hannunta ta gyara zamanta sai kebewa takeyi zatayi kuka,a hankali nace Meenat Ashe baki da tarbiya ban sani ba?Ashe dabba ce ke? Ke inba dakikiya ba mace da kike me daraja da kima amma shine kika biyewa zuciya kika zuga Ameer wai kina mace kece me sace Namiji,Meenat kanki kalau kuwa? Ana tunanin kinfi kowa Sanin duniya Ashe Dabba ce kawai bamu sani ba,kika bi Ameer Har Hotel,Hotel fa Meenat yaushe kikayi wannan wayewar ban sani ba,Sis wlh...yi min shuru makaryaciya abinda kun kira mu da dare jiya ko kin manta ne na tuna miki,tarbiyar da aka bamu kenan?Ina muka san wani Hotel ma?to bari na fada miki wlh wlh kinji na rantse ko Meenat kina da aure,rana daya aka daura miki aure da Ma'eesha Ameer ma ranar aka daura masa,Kinci Amanar mijinki,ga Azabar Allah kuma ki shirya nan da 3days za a kaiki gidan miji shashasha wacce bata San inda kanta yake mata ciwo ba,idan ma kinsan kunyi wani abu gwara ki fada tun wuri idan ya miki ciki ke kika jiyo kuma,Kuka Meenat ta barke da dashi tana wlh bazan yarda ba bana sonsa Allah sai na gudu na bar gari,ficewa nayi na kyaleta nan tana sharbar kukanta,ina fita ta Mike tayi part din Ameer da Daddy tana Kuka,Bedroom din Ameer ta nufa tare da bankawa ciki tace Ameer Ashe an daura min aure nima gaban Ameer ya fadi yace ashe za ayi yaki wlh wlh ba wanda ya isa ki hada shimfida dashi bari mu tabbatar da gaskiya za a kwashi yan kallo,Meenat tana kuka tana kayi wani abu dan Allah an min aure,Harara Ameer ya zuba mata me zan miki ni da nayi gadon Iskanci nake dan Iska kuma tunda Aayan yace matar da aka bani tayi aurenta ma ai shike nan na huta kije ki rungumi mijinki wanda ba gadon Yan Iska ba,ai in ka isa Allah ya tsine min ka gama tabe min jiki kace naje wani wajen mijina gwara ma ka canja tunani ko wlh naje na tona ma asiri wajen Aayan da Ammah,Ameer yace jeki mana ya juya mata baya Meenat haushi ya kamata ta karasa Jikin mirror na Ameer ta dinga watsi da kayan kai ta gama fashe turarukan tas da komai,bai kulata ba ta samu Bedsheet din da yake kai ta dinga ja iya karfinta,Ameer yana dariya a ransa wannan masifa ta Meenat mutum ya mata ciki ai ya shiga uku a duniya,tashi yayi daga saman Bed ya Mike tsaye,Meenat kamar mahaukaciya ta cire bedsheet din ta jefar dashi ta dage kafiyar dake saman Bed din gaba daya,Wayar Ameer ta fadi kasa ta dauke wayar ta fasata a kasa ta tsage kwatsa kwatsa,Tayi waje da sauri tana kuka tayi wajena Mufeeda ina wajen Aayan ta buga mana kofa na bude tare da Galla mata harara nace lfy? Marar tarbiyya ya akayi? Shuru tayi tana tsiyayar da hawaye dan Allah Sis wlh zan fada miki gaskiya,kizo kiji da kyar nabi bayanta muka zauna a palo nace ina Jinki ina da aikin yi,Meenat ta fara ina...Ina...sis Allah bamuyi Babban Iskanci ba wlh ba abinda ya min,kinga..uhm....kawai Romancing dina yayi wlh kuma ni sace shi nayi mu gudu ina sonsa za ayi masa aure,ai shine dan Iska daya min tunda ai ni ban tayashi ba kuma ni...yi min shuru yanzu Meenat da ba ayi muku aure ba da shike nan ba ruwanki haka zaki sakarwa namiji jikinki,ni duk gwagwarmayar dana sha a duniya ki duba yawon dana yi da neman kudi har gidajen manyan yan siyasa lokacin kun fini sanin duniya ma Amma banyi komai Bad ba ban saida mutuncina ba sai ke,ki duba irin dadewa da zaman da mukayi tare da Ameer gida daya same palo dakinsa kusa da naku Amma duk bakiyi komai ba sai yanzu,mutumin da bai ce yana sonki ba yanzu idan wata yake so ba ke bafa?Idan Allah ya canja masa ra'ayi ya auri wata fa?wannan mutuncinki ne,ai kuma kuna da laifi me yasa baku fada min za ayi min aure ba,mene abin boye boye a fito a fada min mana sai kuyi kunbiya kunbiyarku kawai kuma kuce zaku ga laifina,Ai kun san ba dutse bace ni ku fada min gaskiya mana,ai har waya mun bugo muku me yasa baku ce anyi min aure ba wlh ba ruwana alhaki a kanku,baki na saki ina kallon Meenat nace to ai kinyi ta banzar ke aka Yiwa gata so ake yace yana sonki da kansa shashasha sannan a fada muku shine kika wani dauke Ameer kuka tafi yanzu idan an kaiki me zaki kai masa dakin mijin da zaiyi zumudinki? Meenat tace to ai da saura a abunda mukayi me mukayi ma ai ba aje wajen ba,wa aka yi min aure dashi? Ni yanzu kin fara bani tsoro Meenat Amma Ameer ne dama aka daura muku aure tare,Da Sauri Meenat ta buga tsalle taja gefe tace yanzu dama shine?Amma baku fada mana ba? Kun cuce mu wlh bakin Meenat yaki rufuwa,nace banza saura kije ki Bada kanki da duk kin fimu class Meenat ashe na banza ne dama,Meenat tace ke nifa ba irinki bace Amma dan Allah ku kyale Ameer ku nuna ban san nice matarsa ba ai wlh sai na yi masa rashin mutunci da ya zage ya taba min jiki na, baki na tabe nace banza a banza Man kare bayan shi ya miki 1-0 me zakiyi masa kuma ki godewa Allah mijinki ne gwara ma da aka miki auren ashe, fari Meenat tayi da ido tace wlh gwara da kuka yi min ni halittar mu ba daya bace na fiku lfy kuma ai da laifinku domin haka Ammah ta dinga dura min tsumi ba wanda yace ni Amarya ce,kuna ta min gyare gyare ba dole na kasa tsare kaina ba,ba shi yasa yanzu ake lalacewa da yawa yan mata ma yanzu maganin mata suke sha ki fadi ta inda zan zauna lfy,ai wlh kune ma masu laifi tunda kune kuka ki fada mana yanzu kun bata mana lokaci.

Mikewa nayi na barta nan ban kulata ba,gani Meenat tayi an nuna mata Aayan ya samu Ameer yace ka shirya babu me kai ma Amarya ka dauki Abarka kuje ku cinye junanku,Ameer kai a kasa yace wacece wai Yaya? Wacce ta saceka kuka tafi Iskanci Hotel Meenat,Ameer da Sauri ya wani rungume Aayan yana ihun murna da godiya,amma baku fada mana ba ai wlh da mun san hakane baza mu dawo daga Honey moon ba kawai Kd zamu koma sai mun gama cin Amarci zamu dawo.Allah ya shiryeka sai kuje ku bawa Ammah hakuri.

Sai Meenat taga Da wuri Ameer yazo Sabo da Ammah data koma gida bata mata fada ba sai Nasiha tace Laifinsu ne da basu fada Musu ba,kuskurensu ne amma suma sunyi gaggawar daukan mataki basu tsaya munji dalili da wace Amarya ba muka tafi,dama duk me bin shawarar wasu matan to zaiyi nadama karshe Sabo da wasu basa tuna me zaije ya dawo kawai sai su yanke hukunci,da Ameer yazo ma haka Ammah tayi masa nasiha da fada ba ji ba gani Ameer yana hada zufa ina gefe tana rusa Kuka,a cikin dogon Mafarkinta tana ta kuka wiwi tana Bawa Ammah hakuri

Ammah ce ta tashi Meenat tana bacci sai kuka take wiwi ta hada uban zufa tana fada tace Meenat yaufa ake daura aure wannan wanne Iskanci ne sai ki kwanta tun jiya kike bacci kinki tashi in baki sani ba ki sani Kema Amarya ce yau za a daura miki aure,a firgice ta tashi yanzu duk auren data ga an daura,da zaman Hotel dinsu da Ameer,da fadan da sukayi da kuma auren Ma'eesha gaba daya mafarki ta shiga yi duka gaba daya,dariya tayi data tuna duk a mafarki wai suka kira Mufee a Waya suna making love da Ma'eesha suna first night,kai Mafarki karya ne ashe ko auren ma ba a daura ba bare har ma su hadu da Ameer,Lokacin ma Ameer tuni ya sha wanka Aayan ya rikeshi, Meenat mamakin mafarkinta takeyi yanzu duk wannan dadin da suka ji da Ameer a mafarki ne?Abinda take iya tunawa shine ana gobe daurin aure sun tsara da Ameer zata sace shi kafin daurin aure,ta kwanta bacci da dare kuma ta fara mafarkin harma ta saceshi,sun gudu ga abinda ya faru kuma.
Da sauri tayi wanka
End Ads