kashe Meenat tace yanzu akan wannan zaki tasheni kusan karfe dayan dare?Nace ae gwara na kara jin gaskiya,cikin magagin bacci Meenat tace baya Sonki ko kadan,yaaaa tsaneki ne Sis kin kasa ganewa bakya birgeshi ko kadan ta koma ta kwanta sai baccinta takeyi,ni kuwa gaba daya naji duniyar ta kife min.
Nan danan zazzabi ya fara kamani me zafi ga bakin ciki Meenat ta gano Aayan baya sona bana birgeshi,nan nayi tunanin yes gaskiya ne tunda ko yabo na ba yayi bai cewa ina da kyau na hadu,wannan ya nuna ya tsaneni sosai ne kawai sai na fashe da kuka na dinga yi da karfi a saman Bed cikin bargo,duk na hana Ma'eesha da Meenat bacci da Kukana sai ma kara karfinsa da nayi,sai tsaki sukeyi suna juyi su fa sam basa kaunar bacci tare dani dama tun Asali tun Ammah na da rai Sabo da tashinsu nake na hanasu bacci,lokacin ina Sana'a a gida tare da da Ammah cikin dare zan tashe su nace sai munyi lissafin kudi ko na fara basu labarin ya za ayi a tara kudi,ko tattali,idan kuwa nayi Sana'a banci riba ba ko jarin ya karye to fa sunga ta kansu kwana zanyi ina kuka a kan gadon mu,Ammah watarana sai ta jawo sandarta ta kwandala min sannan nake shuru dan ni bacci bai dameni da yawa ba,na riga na saba da jarabar neman kudi ban fiye bacci me yawan gaske ba.
Suna jina kalar Kukan da nake harda me jiniyar motar yan kwana kwana,Meenat tasa Hijab ta fice har saman Aayan dan ita ta manta ma tace Aayan bai sona,cikin magagi ta fada min,knocking tayiwa Aayan ya zata nice sai yaji muryar Meenat,a firgice ya bude tunaninsa wani abu ne ya sameni tace wlh Yaya mudai kazo ka tafi da ita ta damemu wlh sai kuka take ta hana mu bacci,ko ka canja mata dakinta ita kadai mu takura mana takeyi,me ya sameta? Ba komai mu bamu sani ba dama haka takeyi ko a gida idan ta fadi a Business ko jarinta ya karye to sai ta kwana tana uban kuka har sai tayi Zazzabi,Aayan yace akan kudin? Meenat tace sosai ma watarana akan Naira darinta ta fadi a kasuwa sai da ta kwana tana kuka karshe sai da aka mata Allurar zazzabi Sabo da kuka,Duk daren nan sai da Aayan ya dinga dariya,Meenat tace ranar da jarin Awarar ta ya karye aka rasa dubu daya mun zata wlh ta samu tabin kwakwalwa,ni dai kaje dan Allah ka daukota a can ta damemu mu,maeesha ma tana zaune ba bacci kuma gobe muna da Test a schl.
Meenat na gaba Aayan yana bayanta suka je har Bedroom din yanda nake haka nake ta barka kuka na,muryar Aayan dana ji ce tasa na kara ci gaba da kuka na yafi na da karfi ma,na cukwikwiye kaina a bargo ga uban gumi na hada,yace ke mene haka? Amma anyi girman banza babba dake to wa zai wa wani fada kenan? Na dauka ma lallashina yazo ya lallabani mu tafi dakinsa sai kawai naji ya rufe ni da bala'i, Kamar me Aljanu na dinga shure shure a Cikin bargon na kara ci gaba da kuka na,ina wayyo Marainiya ni,Zan mutu, Meenat tace baza fa tayi shuru ba wlh sai a kwana a haka da ita gwara ka dauketa kuje can in yaso ko zaneta ma kayi mu muyi baccin mu,Maeesha tace wai me akayi mata ne tana dariya tace wlh sis Mufee baza ta girma ba ko ni na fita wannan kuka dama ta saba abinta,Aayan yace Dan kune kawai zata hanaku bacci Amma da Bazan kalleta ba ta shekara tanayi,Meenat tace dan Allah ka rufa mana asiri ka dauketa muyi bacci,Aayan ya fara kokarin janye bargon dana ke ciki yana tsaki nace wlh tunda yayi tsaki Bazan je ba a barni nayi Kuka na,da karfi ya fisge bargon ya hau saman Bed din yanda nake kwacewa ina burburwa hannayena ya rike biyu na kasa motsi sai Kukana nake harda hawaye kwara kwara,ya samu bakina yasa yatsun hannunsa dan mugunta ya dinga dalla masa yatsansa kamar Harbin kunama ba shiri nayi shuru,tashi mu tafi yace, nace Bazan je ba,ai kuwa ya make min baki naji zafi ba shiri nace zanje wlh kayi hakuri,meenat sai dariya suke ya figeni yana jana fii yace kusha baccinku yau zata gane kurenta,Meenat ta rufe kofa tace wanne zata gane kurenta wai mu za awa wayo kuje dai ku sha iskancinku kuyi luf abinda shi kanshi kasa bacci yayi dama hakan yake so na ganeku.
Ai kuwa kamar Meenat ta sani yana kaini Bedroom ya fara masifa yana min fada ke baki san kina shiga hakkinsu ba? Ba kyau takura rayuwar wani Yara suna so suyi bacci kuma a gabansu kannenki kike musu kuka,ai ba su akewa ba matan aure me gida sukewa kuka ba wani ba,idan shagwabarki kikeji kizo kiyi min ni zan dauketa ba su ba,nace to ni me nayi abinda fushi kake dani, yace ba dole nayi fushi ba muna Business dinmu kinzo kince Ameer yana da kyau ke yanzu zaki ji dadi nace Meenat ce me kyau ba ke ba,to ai nima sau nawa kace Meenat ta fini,wannan ai cin fuska ne,to ki kiyaye yanzu duk kinsa ma na fasa baki kudin Business sai an sake sabo,nima dadi naji zan masa wayo naji dadina nace to a sake sabon mana wa yake jin tsoro tunda kudi zan samu sai na samu wanda yafi na da ma.
A ransa yace lallai Mufeeda yarinya ce yanzu ta yarda,nima a raina nace dadi a banza kuma a bani kudi nice da riba ka hadu da ni,Muryarsa naji yace to yanzu duk kukanki da shagwabarki Maza sauketa a kaina ki samu kudi kuwa da yawa yarinya,Nace ai ba sai kace ba yanzu zan nemo hanyar arzikina mota,gida da kasar waje ko da kafar katako,jikinsa ya jawoni muka fada saman Bed ba kunya na fara kuka na irin na dazu,shi kuwa lallabani ya farayi yana mene ne Pretty na? Na koma shagwaba kala kala yana biye min tare da fara sarrafani,a raina nace da haka kawai ina can zanyi kwanan kunci tunda hakane Meenat na gano yanda zan dinga baki aiki idan ta baci,Aayan kuwa a ransa dadi yake ji marar misaltuwa yana godewa Meenat dama ya kasa bacci ko kadan ni kawai yake bukata.
AsmaBaffa
[1/19, 12:07 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖
KASUWANCI NA
76-80
Official
By
AsmaBaffa
Ina mika dubun godiya ta gereku
MAMAN 2 KIDS
AUNTY SUMEE
MEENAL SIDI
MRS HAMZA
ADABIYA ISAH
SAMEERA AHMAD
JAMILA SULE
MAMAN MEENAT
Sai manya manyana ina jinjina muku
MAMAN MEENAT
MUM SUHAIL
MAMAN HAIDAR
QUEENMERMU
MAMAN WALEEDA
JIDDER ZARIA
MARCYCOOL
PHERTIMARH
AUTA
FLOWER ina kike kwana biyu Allah yasa lfy?
BIBA
HEENDU
HUMAIRAH
Page naki ne AYSHATABDULLAHI Me hadarin Sharhi na gode.👍😍
Kwance nake a jikinsa na lafe luf muna huce gajiyar harkoki da muka kwasa,kin taba soyayya Ne Mufeeda? Naji muryarsa yana tambayata,wow yanda ya furta Mufeeda kamar wasu Aljanu ne suka fada Sabo da dadin sunan ba a cewa komai, kamar gaske nace ae na taba yi,gabansa ya fadi sosai ya shiga damuwa har kishi ya cika shi ya daure yace da wa? KUDI nace ina na san wani so ni ban san komai ba ai ni imani na kudi,ni kudi ne masoyina,Dariya yayi a ransa yasan ban san ma kudin ba ban san dadinsu ba Amma ina kirarin nasan kudi,a fili kuwa yace yanzu idan na baki million daya a hannunki me zakiyi da ita? Yanzu duk kuna ci kuna sha da Sutura ga schl baku da matsala da ita,ta ya zaki kashe million daya fada min naji? Kwanciya ta na gyara a jikinsa tare da fadawa tunanin ta yanda zan kashe kudin da ya fada,na gama tunani na nace na dinga cin kayan dadi,na fantama na Sa kaya irin na matan shugaban kasa,na dinga zuwa wajen da ake gasa kaji ina ci,na siyi fili kato,da mota,dariya yayi yace to kuna da motar hawa duk wacce kuke so akwai,me kike so kici wanda babu a gidan nan?Sannan kuna cin na wajen ma ai ko? Ae to ni dai ina so ace nima ina da nawa na kaina ba na wani ba,sabo dame?kayan mijinki ai naki ne, a'a ba nawa bane kafin a baka ma sai kayi yar murya,ko kuma a dinga bata rai ko kasa mutum ke ebowa ya baka watarana sai ya gaji,sannan Maza dan suna ma abu sai suyi ta juya ka ana ma kallon wata shatara, matan Hausawa kenan kike nufi duk abinda yasa suke karatu da aikin Gomnati don kawai su samu kudi ba sai sun saurari na mijinsu ba,kuma most of them badan Allah suke so su samu kudin ba kawai biyayya ce basa so suyiwa mijinsu shi yasa suke neman kudin, ya fita kin fita,bai Isa ya saki kiyi ba,wani ma in kudinta yafi na namiji zai sha wulakanci dole shi zai kwantar da kai yana mata biyayya.
Nace hakane ko Ilmi macen tafi namiji sai kaga ko kudin albashi ya dauka ita zai kawowa sai yanda tayi dashi,shi yasa Maza suke tsoron auren macen da ta fisu Ilmi ko ta fisu albashi,sabo da matan Hausawa basu iya samu ba,mace daga tana daukan dan Salary sai kuga ta fara wulakanci kowa taka shi takeyi ita me kudi,dan Allah mata mu gyara halayen mu,wasu gidansu kaje da kyar suke kallonka ma bare mutunci ya hadaku Sabo da tana daukan Salary,mazan sam basa jin dadinsu,ga jarabar son kudi da neman kudi aje nan aje nan ba hutu ba lokacin me gida kuma bai Isa yace komai ba tafi karfinsa sai abinda taga dama,idan ma kishiya zaiyi cewa zatayi ya kara me ya dameni suje can su karata da kudina me nake nema a wajensa ko Sakina yayi zan iya rike kaina da Yara na,abin haushin kuma da zasu rabu sai aga ta koma bin Maza kanana tana kashe musu kudin da ta kasa taimakon mijinta dasu.
Mun dade muna hirarmu dashi yana wasa da dukiyar fulanina wani dadi na shigata na juyo ina facing dinsa tare da kara shigewa jikinsa,yace ya dai? Wani sonsa nakeji yana ratsani ta ko wacce gaba dake jikina,baki nasa ina lashe lips dinsa kamar mayya nan ma haka muka kara birkita kanmu mun dade muna farantawa juna rai,ni kam yanzu son Aayan ya gama ragargaza min zuciya,kwakwaran numfashi banayi sai da tunaninsa,komai nasa birgeni yakeyi,ji nake kamar a hademu na zauna cikin jikinsa har abada abin fa ya wuce gona da iri yanda nake jin son Aayan ya zarta hankali har mamaki nakeyi,bani da burin da ya wuce na ganni tare dashi ina jikinsa,kallon Aayan kadai idan ina yi a Cikin gidan gaba daya sai naji dadi da sanyi marar misaltuwa,nayiwa zuciyata fada abin yaci tura,ko schl naje ba komai nake ganewa ba kawai tunanin Aayan yafiye min komai a duniya.
Kwanaki sun dan ja,Ameer ko yaushe yana part dinmu kusan kullum sai yazo,a nan yake cin lunch da Dinner haka kullum suke fada da Meenat,Ma'eesha ce kawarsa kullum suna tare suna danna waya da jin wakoki aikinsu kenan, Meenat bata da time yanzu karatun waec da Neco sukeyi,Ma'eesha kuwa za a shiga Ss1 kwana nan,ni kuma ina ss1 going to 2 Sabo da ya tsallakemin jss3 ban karasa ba aka sani a ss1 shi yasa Amma da Ma'eesha ma ta fini class.
Ma'eesha ta zama yan mata Sabo da kansu daya da Meenat kusan ma tafi Meenat girma ta kamoni Sabo da dama tana da saurin girma tsayin kafa tayi sai ka rantse ma ba Meenat ce yayarta ba,Sabo da zama da suke yawan yi da Ameer Ma'eesha har ta fara son Ameer sosai Amma boyewa takeyi dan kar mu gane sai dai kullum bata da zance sai Na Ameer.
Kudi masu yawa Aayan ya bamu muje mu sake uniform tare da schl bags da takalma amma sai yace yasan idan nice me araha zan siyo mu tafi tare da su Meenat Driver ya kaimu.
Muna mota Driver zai kaimu store nace canja hanya Baba ka kaimu Kasuwar kofar Wambai yafi araha,Meenat tace wlh mu store za a kaimu masu tsada yace a siya mana,Baki na make mata tayi shuru,ya kaimu Kofar Wambai muna gaban table din masu takalma ina ta zabga cikiniki yaki daidaita,na daga wani baki nace nawa wannan Malam? Dubu uku yace,a garin ina za a siyi wannan dubu uku Malam Dubu daya da Dari biyar idan ka siyar, Ma'eesha ce ta matsa gefe tare da kiran Aayan a waya Hello Yaya taki kaimu store wlh muna kasuwar Kofar Wambai kuma a kasuwar ma table din masu araha wai dan Dubu daya da Dari biyar kuma suna ta Surutu da masu saida kayan dan Allah da aurenta fa Yaya.
Mata masu zuwa kasuwa a zauna ayi ta Surutu da masu saida kaya,da aurenki zaka ga wasu har canja murya suke suna lankwasheta abinda basa yiwa mazajensu sai siyiwa yan kasuwa sabo da suna neman a rage musu ayi musu araha su siya a banza.
Aayan kuwa kishi ne ya sokeshi da bacin rai wai yacewa yarinyar nan suje Mall amma ta kaisu kasuwa cikin maza ana ta cakudewa yanzu haka ma wani ya gogar masa jikin matarsa nan take bai San sanda ya shiga mota ba ya bar Office driver ya ja suka tafi,a hanya ya kira Ma'eesha ta fada masa inda suke minti kadan sai ga Aayan ya danna musu Horn tare da sauke glass.
Ina ganinsa hankalina ya tashi na rude ko ta kan me kaya banbi ba nayi sauri na isa motar mu na fada ciki,Meenat da Ma'eesha suka shiga bayan mota kusa da Aayan da Kansa ya kaisu Shopping ya siya musu wanda suke so masu tsadar gaske komai har ni ma suka siya min nawa,ni kuwa tuni nasa Baba Driver ya maidani gida.
Da suka dawo da kyar na fito palo,Ranar da dare nasha warning wajen Aayan sai da ya min ba dadi ina bashi hakuri.
Anyi mana hutun schl Meenat tana zana waec da Neco dinta,yau Sunday muna zaune a palo ina yankewa Aayan Farce,Ma'eesha na karatu a wayarta da Ameer ya siya mata me kyau,Meenat kuwa abinci take ci dawowarta daga schl kenan yamma lisss,wayar Aayan ce ta fara ruri,da hannuna na daga kiran naga ansa Bobo nasan Yarima ne na kara masa a kunne yace Hey frnd ya kk,Yarima yace gani a gidanku fa bude min kofa, Ma'eesha yayiwa magana yace budewa Yarima kofa Angel dama haka yake cewa Ma'eesha,Meenat kuma yace mata Preety, ni kuma daga ke shike nan sai ta mugun baci zai ce Mufeeda ina takaicin wannan abun da yake min Amma ya na iya tunda ni ba a sona.
Ma'eesha na bude kofa Yarima yayi arba da ita wow ya furta a ransa da gani ba sai an fada ba yasan ma kanwar matar Aayan ce Sabo da kama da muke kawai haske zan fisu kadan shima idan baka sanni sosai ba baza kace na fisu haske ba,ba wani me yawa bane,Maeesha akwai fara'a ta gaisheshi tana murmushi sai kallonta yake ta gama Tafiya da Imaninsa gaba daya, bashi da burin auren yarinya karama Amma akan wannan kuwa sai dai a mutu, da sallama dauke a bakinsa ya shigo,Gaskiya Yarima ya hadu Chocolate ne me haske karshen kyau yana da shi dan fulanin Asali ne,ga wanka iya wanka dama duk irin abokan su Aayan ai haka suke basa muamula da garori, Ma'eesha kuwa kunya ma taji irin yanda ya mata Kwarjini gashi ya hadu sai kuma irin kallon da yake mata.
Yana zuwa ya mikawa Aayan hannu suka tafa shegen gari kwana biyu Aayan ko Saudiyya banga kaje Umrah ba last wk ina can ina ta jiranka kace zaka je har na dawo bamu hadu ba,Tabe baki Aayan yayi tare da cewa gwauro shike yawo lokacin da yaga dama,dariya Yarima yayi lallai Aayan ka canja,juyawa nayi muka gaisa dashi a mutunce yana tsokanata da Abokinsa yayi kiba ya kara kyau me nake bashi ne,Meenat kawo masa ruwa,Kallon wacce aka kira da Meenat yayi tana can Dining tana cin abincinta da alama bata San anyi bako ba,Yarima a ransa yace su wannan gaba daya kama sukeyi da juna amma Ma'eesha irin muryata ce da ita sak,Meenat ce muryarta tafi tamu siranta sabo da iyayinta ta maidata siririya,kayan sanyi ta kawo masa iri iri kana ta gaisheshi a ladafce ya amsa tare da cewa Mufeeda wannan duk kannenki ne? Ae mana wannan Ma'eesha wannan Meenat,yace ke kuma Mufeeda triple M kenan yeah Ma'eesha ta amsa muna dariya,Meenat yan mata uwar iyayi tana ji da yan matan ci sai girman kan tsiya watarana kamar wata yar sarki aka take komawa magana ma sai taga dama,watarana kuma ta zage ayi da ita,Muna zaune ana hira sai ga Ameer ya shugo an ci wanka yazo dan ya birgeni ni Mufeeda wacce ban san me yake bama,Maeesha har taji sanyi data ganshi kusa da ita ya zauna ta gaisar dashi,Yarima ya fara kishin Ameer ya zauna kusa da Ma'eesha kuma yaga Ma'eesha sai wani Fara'a take masa sun fara surutunsu da alama sun saba da juna,s hi kuwa Ameer gaba daya Hankalinsa na kaina yanda na hade cikin Lace riga da skert ba karamin kyau nayi ba,abinda ya bashi haushi ganin ina yankewa Aayan farce gashi kuma kafafun Aayan gaba daya saman cinyata ya dorasu yana kwance dan naji dadin yanke masa farcen.
Muna zaune daf da Magrib wata yar aiki ta shigo wai Meenat tazo tayi bako,Meenat tace ita bata da bako baza taje ba,tun kafin ta fara magana Ameer ya fara dariya,haka Aayan ma,nima na gane me suke nufi ko irin su Kwaja ne suka zo,Yarima yace mene haka daga ana kiran yarinya zaku fara mata dariya bai dace ba,Yar aikin tace a wata fyallelliyar mota yazo Hajiya da gani dan